Ma’aukatan lafiya sun tsunduma yajin aiki

[ad_1]



Haɗaɗɗiyar Ƙungiyar Ma’aikatan Lafiya ta Najeriya (JOHESU) da Ƙungiyar Ƙwararru a Fannin Kiwon Lafiya sun fara yajin aiki a yau Asabar.

Ƙungiyoyin sun ce gazawar gwamnati wajen aiwatar da sabon tsarin albashin ma’aikatan lafiya na CONHESS da kuma rashin kawo ƙarshen matsalolin da suka jima suna ƙorafi a kansu ne musabbabin tafiya yajin aikin.

Wannan na ƙunshe ne a wata sanarwa da Shugaban JOHESU na Ƙasa, Kwamared Kabiru Ado Minjibir, ya sanayawa hannu.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *