Amurka za ta tallafa wa Nijeriya daƙile matsalar tsaro

[ad_1]



Gwamnatin Najeriya ta ce Amurka ta amince za ta ƙara faɗaɗa haɗin gwiwar tsaro tsakaninsu, wanda ya haɗa da samar da karin bayanan sirri, makamai da sauran kayan yaƙi, domin ƙarfafa yaƙi da ’yan ta’adda da ƙungiyoyin masu tayar da kayar baya a ƙasar.

Hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Mashawarci na Musamman ga Shugaban Ƙasa Bola Tinubu kan Bayar da Bayanai da Tsara Dabaru, Bayo Onanuga ya fitar a ranar Litinin.

Wannan dai ya biyo bayan jerin tattaunawa da aka gudanar a Washington tsakanin manyan jami’an Najeriya da na Amurka, domin zurfafa dangantakar tsaro da ƙulla sabbin hanyoyin haɗin gwiwa.

Tawagar Najeriya ƙarƙashin jagorancin mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, ta gana da jami’an majalisar dokokin Amurka, Fadar White House, ma’aikatar harkokin waje, da hukumomin tsaro na ƙasar.

A cikin tawagar akwai Antoni Janar na Tarayya, Lateef Fagbemi; Shugaban Ma’aikatan Tsaro, Janar Olufemi Oluyede; Shugaban Leƙen Asirin Tsaro, Laftanar Janar Emmanuel Undiandeye; da Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Kayode Egbetokun, tare da wasu wakilai daga ofishin mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro.

A yayin ganawar, tawagar Najeriya ta ƙaryata zargin da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi na cewa ana kashe Kiristoci a ƙasar, tana mai cewa matsalolin tsaron ƙasar babu wanda suka ƙyale domin kuwa suna shafar al’ummomi daban-daban ba tare da la’akari da addini ko ƙabila ba.

Zargin na Trump ya haifar da ƙalubale da dama a cikin ƙasar, inda hannayen jari suka zube, baya ga ta’azzarar matsalolin da ake gani a ’yan kwanakin nan.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *