Jami’an Tsaro Sun Kashe Ƙasurgumin Mai Garkuwa Da Mutane, Maidawa Da Wasu A Kwara

[ad_1]

Jami’an tsaro a Jihar Kwara sun kashe ƙasurgumin mai garkuwa da mutane, Maidawa, tare da wasu daga cikin ‘yan tawagarsa a wani samame da suka kai kusa da Isanlu-Isin.

Wata majiya daga jami’an tsaro ta bayyana cewa an gudanar da aikin ne a ranar 30 ga watan Satumba, 2025, a ci gaba da yunƙurin kawar da masu garkuwa da mutane a jihar.

Majiyar ta ce labarin mutuwar Maidawa ya isa ga sauran ‘yan ƙungiyar ta hannun wani ƙasurgumin mai garkuwa da ake nema, Baccujo, wanda ya tattauna da abokan aikinsa a Katsina.

Ta ƙara da cewa kiraye-kirayen da gwamnatin jihar ta yi na neman gaggawar ɗaukar mataki ya sa jami’an tsaro suka ƙara ƙaimi wajen fatattakar masu garkuwa da mutane, waɗanda ke kai wa ƙauyuka hare-hare kuma suna yin garkuwa da mutane domin karɓar kuɗin fansa.

An gudanar da ayyukan ne a matakai daban-daban a wuraren da aka fi garkuwa da mutane a ‘yan makonnin nan, ciki har da Ekiti, Ifelodun, Isin, Edu da Patigi.




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *