Gini mai hawa 3 ya rufta kan mutane a Legas
[ad_1]
Wani gini mai hawa uku da ake ginawa ya rufta kan mutane a unguwar Yaba, da ke Jihar Legas.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), ta ce ginin ya rufta ne da misalin ƙarfe 8 na dare.
Shaidu sun ce akwai mutane biyar zuwa shida a cikin ginin lokacin da abin ya faru.
NEMA ta ce ta ceto mutum huɗu, kuma an garzaya da su asibiti domin kula da lafiyarsu.
Sai dai hukumar ta ce ba a tabbatar da adadin waɗanda har yanzu suke ƙarƙashin ginin ba, yayin da ake ci gaba da aikin ceto.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link