Category: Latest News

  • NAJERIYA A YAU: “Abin Da Ya Sa Muka Dawo Daga Rakiyar Kirifto”

    [ad_1]

    Karin fannoni



    A ’yan watanni da suka gabata, matasa da yawa a Najeriya sun dukufa don ganin hakar su ta cimma ruwa wajen samun kudaden kirifto.

    Amma alamu na cewa a baya-bayan nan wasu daga cikinsu sun sare sun kuma saduda sun dawo daga rakiyar harkar.

    Shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan dalilan wasu matasan na yin watsi da harkar kirifto.

    Domin sauke shirin, latsa nan


    [ad_2]

    Source link

  • Tinubu Ya Umarci A Yi Bincike Kan Hatsarin Jirgin Kasa Daga Abuja Zuwa Kaduna

    [ad_1]

    A ranar Talata ne wani jirgin kasa da ya taso daga tashar Kubwa da ke Abuja zuwa Kaduna ya kauce hanya, mintuna kadan da tashinsa, inda fasinjoji akalla 14 suka jikkata, lamarin da ya haifar da firgici a tsakanin matafiyan.

    Tuni dai, Hukumar Kula da Zirga-zirgar Jiragen Kasa ta Nijeriya (NRC), ta sanar da dakatar da zirga-zirgar jiragen; har zuwa wani lokaci.

    LEADERSHIP, ta tattaro cewa; jirgin wanda ya kunshi tarago guda 10, ya taso ne daga kadan bayan karshe 11 na safe daga Kubwa.

    Har ila yau, hukumar jiragen kasa ta Najeriya (NRC) ta bayyana cewa; an fara bincike kan hatsarin da jirgin kasan daga Abuja zuwa Kaduna ya yi a garin Asham da ke Jihar Kaduna.

    Hukumar ta ce, binciken zai gudana ne karkashin kulawar hukumomin da abin ya shafa tare da sa ido daga ma’aikatar sufuri ta tarayya, domin kokarin gano musabbabin faruwar al’amarin.

    A cikin sanarwar da NRC ta fitar a yammacin ranar Talata, ta bayyana cewa; jimillar mutum 618 ne suke cikin jirgin a lokacin da ya sauka daga kan hanyarsa.

    Kazalika, hukumar ta bayyana cewa; daga cikin fasinjojin, mutum akalla 14 ne suka samu raunuka daban-daban, sannan kuma an garzaya da su asibiti. Sauran fasinjojin kuma, an mayar da su zuwa tashoshin Idu da Kubwa cikin wani jirgi da aka turo daga Abuja.

    Haka kuma, an dakatar da dukkanin ayyuka da zirga-zirgar jirgin kasan daga Abuja zuwa Kaduna na dan wani lokaci, har sai an kammala bincike da kuma gyara hanyar.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Hadimin Gwamnan Kano ya maka mawallafin Daily Nigerian a kotu saboda kiransa da ‘ɓarawo’

    [ad_1]



    Daraktan Tsara Tafiye-tafiye na Gwamnan Kano, Abdullahi Ibrahim Rogo, ya maka jaridar Najeriya Daily Nijeriya da mawallafinta, Jaafar Jaafar a gaban kotu, bisa zargin ɓata masa suna ta hanyar kiransa da ɓarawo.

    ‎A kwanakin baya ne dai jaridar ta zargi Daraktan da karkatar da kudade har sama da Naira biliyan shida da rabi zuwa asusunshi, kodayake daga bisani Gwamnan jihar, Abba Kabir Yusuf ya wanke shi daga zargi, inda ya ce ba satar kudaden aka yi ba, na aiki ne.

    To sai dai jaridar ta sake yin labari mai taken “Gwamnan Kano ya kare hadiminsa barawo, ya ce gwamnatin Ganduje ma ta kashe N20bn a ofishin”, inda ta ce daga cikin kudaden da ake zargin hadimin da karkatarwa, tuni ma ya mayar da Naira biliyan daya da miliyan 100 ga hukumar yaki da rashawa ta ICPC.

    Amma Abdullahi Rogo ya maka jaridar da mawallafinta a gaban kotun majistare mai lamba 15 da ke Nomansland a Kano da ke karkashin Mai Shari’a Abdul’aziz M. Habib.

    Rogo dai ya maka mutanen ne tare da dan jaridar da yake aiki a kamfanin mai suna Umar Audu, yana neman ta tilasta musu su biya shi diyyar bata masa suna ta hanyar kiransa da barawon da suka yi, duk da cewa ana kan bincike kuma ba a kai ga samun sa da laifi ba tukunna.

    Hakan a cewar Rogo ya saba da tanade-tanaden sassa na 106 da 107 na kundin ACJL na jihar Kano na 2019  da kuma sassa na 114, 164 da 393 na kundin manyan laifuffuka na jihar Kano.

    ‎A wani labarin kuma, ‎kotun ta umarci Mataimakin Babban Sufeton ’Yan Sanda mai kula da shiyya ta daya ta rundunar da ke Kano da ta gudanar da cikakken bincike kan zargin bata suna da kafar yada labaran ta yi.

    Umarnin kotun, wanda magatakardar kotun ya sanya wa hannu mai dauke da kwanan watan 28 ga watan Agustan 2025 ya biyo bayan karar da da Abdullahi Rogon ya shigar a gaban kotun.


    [ad_2]

    Source link

  • Masana Sun Bayyana Bunkasa Da Tasirin Harshen A Duniya

    [ad_1]

    Tarihi da mabiya tarihi sun tabbatar da girma, kima da daukakar harshen Hausa a idon duniya ya daidaita da duk wani harshe da ake da shi a doron kasa.

    A bayyane yake cewar inma harshen Hausa a matsayin harshe, adabi da al’adun Hausawa sun shiga kowace nahiya ta duniya tare da kyankyashe ‘ya’ya da jikoki.

    Karbuwa da bunkasar Harshen Hausa a matsayin Harshe mafi girma a Afurka ta Yamma ne dalilin da ya sa al’ummar Hausa da Hausawa ke karrama harshen ta hanyar shirya bukin tunawa da harshen a kowace shekara.

    A yau harshen Hausa ya bi sahun harsuna dubu 7500 da ake da su a duniya da al’ummar su ke bukin tunawa da harsunan a kowace shekara a bayyane ko akasin hakan.

    A shekaru 10 sa suka gabata ne daya daga cikin zaratan matasan Hausawa mai kishin Hausa da son ci- gaban ta a kasar Hausa ya jagoranci kirkirar ranar Hausa ta duniya a kafafen sada zumunta na zamani domin jin amon Hausawa da al’adun su.

    Harshen Hausa shine kan gaba a yawan masu magana a Afrika ta Yamma ta yadda yake da karbuwa a Nijeriya, Nijar, Ghana, Kamaru, Benin, Gabon, Togo, Afrika ta Tsakiya, Sudan da Saudiyya da sauran su. Hasalima kowace nahiya ta duniya akwai jami’ar da ake koyar da harshen Hausa da Hausanci.

    Bunkasar Harshen Hausa ya sa harshen ke barazanar batar da kananam harsuna wadanda tuni wasu da dama a yau suka bace ba amo ba labarin su a bisa ga yadda yake mamaye harsuna a mabambantan kasashe.

    Sai dai duk da kima da martabar da Harshen Hausa yake da shi da yadda daruruwan miliyoyin al’umma ke magana da Harshen har yau Jamhuriyar Nijar kadai ce kasar da ke amfani da Hausa a hukumance a matsayin harshen kasa.

    Farfesan al’adun Hausawa na farko a duniya (2009) Aliyu Muhammad Bunza ya ce a na gudanar da taron ranar Hausa ta duniya domin jin amon Hausawa da al’adun su da gudunmuwar da suka bayar a duniyar zamanin su domin sun mamaye kasashe da yawa a Afrika sun kuma kafa sansani da yawa.

    Shehin Malamin wanda ke koyarwa a jami’ar Usmanu Danfodoyo da ke Sakkwato ya kuma ce manufar taron shine domin Hausawa su san ina aka kwana ina aka tashi, samun hadin kan su a duk inda suke da wadanda ke a kasar Hausa da wajen kasar Hausa.

    A bana a ranar 26 ga Agusta ranar da Majalisar Dinkin Duniya ta kebe a matsayin ranar Hausa ta duniya an gudanar da gagarumin bukin ne a Daura da ke jihar Katsina a hamshakiyar fitacciyar masarautar da ta kafa ingantaccen tarihin zama tushen Hausa da Hausawa, tarihin da babu wata kasa a kasar Hausa da ke da irin sa.

    Basarake mai magana daya da murya daya, Mai martaba Sarkin Daura, Alhaji Umar Faruk Umar, kasaitaccen Sarkin da ya yi fice wajen daga darajar Hausawa da al’adunsu tare da gudanar da mulkin gaskiya da adalci ne ya karbi bakuncin dubun- dubatar al’ummar ciki da wajen kasar Hausa da suka halarci taron

    Taron ranar Hausa na bana a Daura wanda shine karo na 10 an yi masa taken “Amfani da Harshen Hausa wajen wanzar da zaman lafiyya” ya kayatar da da jama’a musamman yadda Hausa da Hausawa suka hadu, suka raya harshen, baje kolin al’adunsu su, tattauna matsaloli da kalubalen da harshen ke fuskanta da hanyoyin magance su.

    A taron an gudanar da kayataccin wasannin Hausawa da suka yi fice da su, kama daga hawan daba tsakanin kasashen Hausa Bakwai da na Kanne Bakwai da kokawa da wasannin wuta na makere, haka ma mawaka sun baje fasahar hikimar su.

    Abdulbaki Jari, matashin da ya jagoranci assasa ranar Hausa ta duniya ya bayyana cewar ba wai ana tunawa da ranar Hausa kadai a Afrika ta Yamma da Afrika ta Tsakiya ba, har ma a wurare da dama na duniya ciki har da Turai, Amurka da Asiya.

    Dan jaridar ya bayyana cewar Harshen zai kai matakin da ya kamata a duniya idan har masu amfani da harshen suka hada kai domin magance kalubalen da ya dabaibaye harshen.

    A kan gudanar da taron a Daura kuwa, Jari ya bayyana cewar Daura ita ce tushen Hausa kuma cibiyar dukkanin kasashen Hausa wadda ke martabawa, mutuntawa da daga dajar al’adun Hausawa don haka ta ke da kima a wajen Hausawa.

    Jari ya ce ba wai sun assasa taron domin a rika gudanar da buki ba kawai, a’a, ya ce hanya ce da Hausa da Hausawa a fadin duniya za su hada kai su tattauna kalubalen da ke damun su da samar da zaman lafiya mai dorewa.

    Matashin ya bayyana cewar harshen Hausa yana da girma da daukaka, don haka ya bambanta da sauran harsunan da ke bacewa, ya ce a na magana da harshen a nahiyar Afrika tsakanin mutane fiye da miliyan 170.

    Jari wanda ma’aikaci ne a kafar yada labarai ta TRT Afrika ya bayyana cewar Harshen ya riga ya samu gurbi a kasashen Afurka musamman a Jamhuriyar Nijar a inda ya ce sama da kaso 80 cikin 100 na al’ummar kasar suna magana ne da Hausa. Haka ma a Ghana suna da amfani da Hausa sosai.

    Ya ce girman harshen Hausa da karbuwar sa a duniya ne ya sa kafafen yada labarai da dama a fadin duniya ke yada shirye- shiryen su da Hausa domin isar da sako ga dinbin mabiyan su a fadin duniyar Hausawa.

    Matashin ya bayyana cewar kamar wasa suka assasa ranar Hausa ta duniya a 2015, a kafafen sada zumunta amma ba zato ba tsammani saboda karbuwa da tasirin harshen, a yanzu duk duniya a na maganar tare da gudanar da taron a kasashe kusan 25.

    Jari wanda ya kafa ingantaccen tarihi a kasar Hausa ya gabatar da bukatar da ke ci wa Hausawa tuwo a kwarya ta hanyar yin kira ga Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Afrika ta Yamma wato ECOWAS da ta duba yiyuwar sanya harshen Hausa a cikin harsunan da ake harkokin kasuwanci da shi da mu’amalar zamantakewa a hukumance a yankin wanda hakan zai kara taimakawa harshen da daga darajar harshen a idon duniya.

    A tsokacinsa kan muhimmiyar ranar da tasirin ta, Farfesa Aliyu Muhammad Bunza ya bayyana cewar Hausawa na gudanar da bukin ranar Hausawa ta duniya ne domin bunkasa harshen tare da kokarin ganin ya zama daya daga cikin harsunan da ake koyar da ilimi da shi kamar yadda ake koyar da larabci, Turanci, Asiyanchi da Faransanchi da sauransu.

    Farfesan ya bayyana cewar mashirya taron na son ganin Harshen Hausa ya kai matsayin da za a rika koyar da kowane irin limin duniya da shi.

    A kan yadda za a inganta harshen kuwa, Bunza ya ce a yi kokarin samar mashi mazauna daga makarantun furamari, sakandire zuwa jami’o’i ya zama harshen hukuma a wajen da Hausawa suka rinjaye mutane.

    Malamin ya bayyana cewar idan aka mayar da kowane ilimi a cikin harshen Uwa to ba yadda za a yi a rinjaye shi a harkokin ilimi da tsaro.

    A cewar sa, Shehin Malamin Malamai, marigayi Farfesa Mahadi Adamu a 1975 ya yi rubutun musamman kan gudunmuwar Hausawa a tarihin Afrika ta Yamma kuma ba a samu wata al’umma da aka yi bayanin gudunmuwar ta ba kamar Hausawa da suka mamaye wuraren.

    Ya ce taron ranar Hausa na da manufar hadin kan Bahaushe, sanin ina Bahaushe ya fito, yadda al’adunsa kyawawa suke, tabbatar da harshen Hausa da bunkasar sa da kokarin inganta Hausa da Hausawa da kara masu kwarin guiwa ga ci- gaban zamani.

    Farfesa Bunza ya bayyana cewar ba a san adadin Hausawa da ake haihuwa da wadanda ke mutuwa ba don haka fadin adadin su abu ne mai wahala.

    Ya ce a shekarar 2020 an bayyana cewar akwai Hausawa akalla miliyan 150 wanda ya ce adadin ba daidai ba ne domin adadin ya baiwa Hausa matsayin Harshe na 11 a duniya a cikin harsuna 7500.

    Ya ce “idan aka bi adadin kwarai Hausa ta na da akalla adadin mutane miliyan 300 a duniya tare da zama harshe na hudu ko na biyar da ake jin sa a duniya saboda duk duniya a bakar fata da turai babu mai auren mace hudu in ba Bahaushe ba, ya fi su iyali da mata, haka ma a Afrika babu al’umma mafi harkokin kasuwanci irin Hausawa.”

    A jawabinsa Firamin Ministan Jamhuriyar Nijar, Muhammad Lamine Zain ya bayyana cewar taron ya kara tabbatarwa duniya cewar Nijeriya da Nijar abu daya ne, ya ce suna fatar taron zai taimaka wajen warware matsalar diflomasiyya da ke akwai tsakanin kasashen biyu.

    Gwamnan soji daga Jihar Damagaram a Jamhuriyar Nijar, Kanal Muhammad Sani masallatchi wanda ya wakilci Firayim Ministan bayyana cewar yadda Hausa da Hausawa suka hadu domin bunkasa harshen su ya nuna tasirin da harshen yake da shi a duniya.

    Firayim Ministan ya bayyana cewar taron zai kara hada kan Hausawa a ko’ina suke a duniya a matsayin ‘yan uwa daya al’umma daya. Haka ma Sarkin Musulmin Damagaram Aboubacar Oumarou Sanda ya albarkaci taron da kakkarfar tawaga.

    Duk da kalubalen bacewar wasu kalmomi da harshen ke fuskanta, yadda dubun- dubatar al’umma a kasar Hausa suka rungumi ranar Hausa ta duniya tare da tunawa da ranar ya nuna kima da tasirin harshen da yadda yake kara bunkasa a idanun duniya.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Magauta sun sa NNPCL a gaba – Ojulari

    [ad_1]



    Shugaban Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL), Bashir Bayo Ojulari ya ce mutanen da ba sa nufin Najeriya da alheri sun sa kamfanin a gaba saboda sabbin tsare-tsaren da yake kawowa na inganta fannin man fetur a kasar.

    Ya bayyana hakan hakan ne lokacin da ya karbi bakuncin shugabannin Manyan Ma’aikatan  Bangare Man Fetur da Iskar Gas na Kasa (PENGASSAN) a hedkwatar kwamfanin da ke Abuja.

    Ojulari ya ce duk da yake sun san za su iya fuskantar kalubalen, amma ba za su taba bayar da kai bori ya hau ba a yunkurinsu na inganta rayuwar ’yan Najeriya.

    “An sa mu a gaba, amma ba za mu taba bayar da kai ga biyan bukatar dan lokaci ba, saboda hakan ba zai haifar wa da Najeriya da mai ido ba.  Mun san ba yadda za a yi ka kawo canji ba tare da kalubale ba,” in ji Ojulari.

    Shugaban kamfanin ya bukaci ’yan Najeriya su kara hakuri da sauye-sauyen, inda ya ce bayan wuya dadi na nan tafe ba da jimawa ba.

    Tun da farko shugaban kungiyar ta PENGASSAN, Festus Osifo, ya ce ma’aikatan na man fetur sun je hedkwatar kamfanin ne domin su gode masa kan irin gudunmawar da ya bayar a taron kungiyar na bana da aka yi kwanan nan a Abuja.

    Ya kuma ce suna jinjina wa shugaban na NNPPCL saboda abin da ya kira gagarumar nasarar da ya samu ya zuwa yanzu a karkashin shugabancinsa.


    [ad_2]

    Source link

  • Me Ya Sa Wasu Kafofin Watsa Labarun Japan Suke Kokarin Musanta Kisan Kiyashin Nanjing?

    [ad_1]

    Alal hakika, tarihi ba zai taba mantawa da kisan kiyashi da sojojin mamaya na kasar Japan suka yi a birnin Nanjing na kasar Sin ba. Muggan laifukan yaki da dakarun na Japan suka aikata cikin kwanaki sama da 40 bayan mamaye birnin a ranar 13 ga watan Disamban shekarar 1937 sun yi matukar muni.

    Tarihi ya tabbatar da cewa, dakarun na Japan sun hallaka fararen hula Sinawa da dakaru marasa dauke da makamai da yawansu ya haura 300,000, tare da yi wa sama da mata 20,000 fyade. An kuma fayyace wadannan muggan ayyuka cikin kundayen tarihi yadda ya kamata.

    To sai dai kuma sabanin abun da ake zato, cewa bangaren Japan zai ci gaba da neman afuwa, da nuna nadamar wadannan abubuwa da suka faru a baya, sai ga shi wasu kafofin watsa labaran kasar na furta wasu kalamai na kokari musanta tarihi.

    A wata makala da aka wallafa ranar Litinin din farkon makon nan, editan wata jaridar kasar Japan ya soki wani fim mai suna Dead to Rights, wanda ya yi bitar irin cin zarafin da sojojin Japan suka aikatawa Sinawa fararen hula a wancan lokaci. Har ma dan jaridar ya ce wai batun kisan kiyashi na Nanjing labarin yaudara ne kawai da kasar Sin ta kitsa. Lallai irin wadannan kalamai masu ban mamaki suna da munin gaske, suna kuma dada karfafa zargin da aka dade ana yiwa bangaren Japan na karyata hakikanin tarihi, da nufin sauya gaskiya, da kaucewa daukar alhakin abubuwan da suka faru.

    Tun bayan fitar da Dead to Rights a Sin da sauran sassan duniya, fim din ya samu matukar karbuwa, kasancewar ya yi “Waiwaye Adon Tafiya” game da munin ta’asar da dakarun Japan suka aikata a birnin Nanjing a wancan lokaci. To, amma abun tambayar shi ne me ya sa har yanzu wasu masu ra’ayin rikau na Japan ke kokarin kore abubuwan da fim din ya nuna? Amsar wannan tambaya a bayyane take, irin wadannan Japanawa suna tsoron kara bayyanar gaskiya!

    Yanzu haka a nan kasar Sin ana ta shirye-shiryen gudanar da babban bikin cika shekaru 80 da cimma nasarar yaki da mamayar sojojin Japan, da nasarar yakin kin tafarkin murdiya, wanda shi ma wani lokaci ne da zai dada tabbatarwa duniya zahirin abubuwan da suka wakana, tare da karyata sassan dake kokarin lullube gaskiya, da kaucewa daukar alhakin ta’asar da aka aikawa al’ummar Sin a yayin mamayar birnin Nanjing.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Manyan Jami’ai A Ma’aikatar Tsaro Ta Cikin Gida Za Su Ci Gaba Karɓar Albashi Har Ƙarshen Rayuwa

    [ad_1]

    Ministan Harkokin Cikin Gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, a ranar Alhamis ya bada sanarwar wani gagarumin shiri na Shugaban Ƙasa Bola Tinubu, wanda ya bada damar karɓar albashi har ƙarshen rayuwa ga duk wani babban jami’i da ya yi ritaya daga ma’aikatar a matsayin Mataimakin Kwanturola, Kwanturola, ko Kwamanda-Janar zuwa sama.

    Ministan ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a Babban Taron Bita na Ministan na shekarar 2025 a Abuja, inda ya bayyana nasarorin Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida tare da nanata sadaukarwar ta ga aiwatar da sauye-sauye da ƙarfafa wa ma’aikata gwiwa a hukumomin da ke ƙarƙashin ta.

    Hukumomin da za su amfana da wannan tsari a ma’aikatar su ne: Hukumar Gyaran Hali (wato ta gidajen yari), Hukumar Shige-da-Fice (NIS), Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya(FFS), da Hukumar Tsaro ta farin kaya (NSCDC).

    Wannan bayani yana ƙunshe ne a cikin sanarwar da Jami’in Yaɗa Labarai na Ƙasa (PRO) na Hukumar Kashe Gobara ta Tarayya, DCF P.O. Abraham, ya fitar jim kaɗan bayan taron bitar.

    Ya ce: “Ministan ya bayyana matuƙar godiya ga Shugaba Tinubu bisa ga ɗimbin goyon bayan sa, yana mai tabbatar da cewa dukkan hukumomin da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Harkokin Cikin Gida suna amfana da albarkatun da ke cikin Shirin Sabunta Fata.”

    Tunji-Ojo ya ci gaba da lissafa manyan nasarorin ma’aikatar, waɗanda suka haɗa da kammala aikin ƙarin girman ma’aikata wanda aka daɗe ba a yi ba, ya ce sama da ma’aikata 50,000 ne aka yi wa ƙarin girma a cikin shekaru biyu da suka gabata.

    Haka kuma ya ce daga yanzu ba za a riƙa yin ƙarin girma bisa matakin daɗewa a aiki ba, sai dai bisa iya aiki da kuma dagewa, ya nanata cewa ma’aikatar ta ƙudiri aniyar yi wa kowane ma’aikaci sakayya bisa ga ƙoƙarin da ya yi a aiki.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Baki Kusan 50 Daga Kasashe 30 Na Turai Za Su Halarci Bikin Tunawa Da Nasarar Yakin Turjiyar Sinawa Kan Zaluncin Japanawa

    [ad_1]

    A yau Alhamis, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya sanar da cewa, ya zuwa yanzu akwai shugabanni da tsoffin ‘yan siyasa da manyan jami’ai, da jakadun dake kasar Sin da sauransu kusan 50 daga kasashe 30 na Turai da suka tabbatar da za su halarci bikin da za a yi albarkacin cika shekaru 80 da samun nasara a yaki da kutsen Japan da yaki da mulkin danniya a duniya. Wannan ya nuna niyyarsu ta hada hannu wajen tunawa da tarihi da kiyaye zaman lafiya da adalci.

    Guo ya jaddada cewa, kasar Sin ta shirya bikin ne da nufin tunawa da tarihi da magabata, da kiyaye zaman lafiya da ma tabbatar da makoma mai kyau ga bil Adama a nan gaba. (Bilkisu Xin)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Shugaban NPA, Dantsoho Ya Zama Mataimakin Shugaban Kungiyar Tashoshin Ruwa Ta Duniya

    [ad_1]

    An zabi shugaban Hukumar Tashoshin Jiragen Ruwa ta Nijeriya (NPA), Abubakar Dantsoho, Mataimakin Shugaban Hukumar Kula da Tashoshin Jiragen Ruwa ta Duniya (IAPH), wanda ya kara tabbatar da karuwar tasirin Nijeriya a harkokin tekun duniya.

    Zaben da aka gudanar a birnin Tokyo na kasar Japan, ya sake zama wani muhimmiyar nasara da ci gaba ga Dantsoho, wanda a baya ya kafa tarihi a matsayin dan Nijeriya na farko da ya jagoranci kungiyar kula da tashar jiragen ruwa ta yammacin Afirka da tsakiyar Afirka tun bayan kafuwarta a shekarar 1972.

    Da yake tabbatar da nasarar a cikin wata sanarwa a ranar Talata, mai magana da yawun NPA, Ikechukwu Onyemekara, ya ce, zaben na Dantsoho na nuni da amincewar da duniya ta yi masa na sake raya harkoki a fannin tashoshin ruwan Nijeriya. Shi ma Sakatare-Janar na IAPH, Masahiko Furuichi ya yi maraba da wannan zaben, yana mai cewa, “Ina farin cikin yin aiki tare da ku a cikin IAPH na shekaru masu zuwa.”

    An kafa ta a cikin 1955 kuma tana da hedikwata a Tokyo, IAPH kungiya ce ta duniya mai dauke da tashoshin jiragen ruwa fiye da 190, kuma tana gudanar da kasuwanci a cikin ƙasashe 89.

    Mambobin kungiyar IAPH suna kula da sama da kashi 60 cikin 100 na cinikin teku da kwantena na duniya. Kungiyar tana taka muhimmiyar rawa wajen tsara manufofin tekun duniya, tare da yin aiki kafada da kafada da Hukumar Kula da Teku ta Duniya, Hukumar Kwastam ta Duniya, da tsarin Majalisar Dinkin Duniya.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Dangote ya ƙulla yarjejeniyar gina kamfanin takin zamani na dala biliyan 2.5 a Habasha

    [ad_1]



    Ƙasar Habasha ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da wani reshe na Rukunin Kamfanonin Dangote na Nijeriya domin gina wata sabuwar masana’antar samar da takin zamani ta kimanin dala biliyan 2.5.

    Hakan na ƙunshe cikin wani saƙo da Firayim Ministan Habasha, Abiy Ahmed ya wallafa a shafin X ranar Alhamis.

    Abiy ya ce wannan yarjejeniya da Dangote Group na attajirin Afirka, Alhaji Aliko Dangote, za ta sanya ƙasarsa cikin jerin manyan ƙasashen da ke samar da takin zamani a duniya.

    Ya bayyana cewa wannan aikin gina masana’antar wanda za a fara nan ba da jimawa ba, za ta riƙa samar da tan miliyan uku na takin zamani a kowace shekara.

    “Wannan aikin zai samar da ayyukan yi ga ’yan ƙasa, ya tabbatar da wadatar takin zamani ga manomanmu da suka daɗe suna fama da ƙalubale.

    “Sannan zai zama mataki na musamman a yunƙurinmu na cin gashin kai wajen samar da abinci,” in ji Abiy.

    A watan Yuni, Aliko Dangote ya shaida cewa nahiyar Afirka za ta iya zama mai isar wa kanta da takin zamani cikin shekaru 40 bisa tsarin faɗaɗa masana’antarsa ta dala biliyan 2.5 da ke Legas.

    A halin yanzu dai, Afirka na shigo da fiye da tan miliyan shida na takin zamani a kowace shekara, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ruwaito.


    [ad_2]

    Source link