Category: Latest News

  • Shawarar Gina Kyakkyawar Makomar Bil Adam Ta Bai Daya Ta Samu Amincewa A Duniya

    [ad_1]

    A yau da safe, cibiyar manema labarai ta bikin cika shekaru 80 da cimma nasarar yaki da maharan Japan da yakin tafarkin murdiyya na duniya, ta gudanar da taron manema labarai karo na biyu, inda aka yi karin haske game da ci gaba cikin kwanciyar hankali da inganta ra’ayin gina kyakkyawar makomar bil adam ta bai daya da aka samu, tare da amsa tambayoyin ‘yan jarida.

    Mataimakin ministan harkokin wajen Sin Ma Zhaoxu ya bayyana cewa, ra’ayin kafa kyakkyawar makomar bil adam ta bai daya ya sauya daga wata shawara ta Sin zuwa ra’ayin bai daya da ya samu amincewar duniya, kuma daga kyakkyawan fata zuwa aiki mai fa’ida, kazalika daga ra’ayi zuwa tsarin kimiyya, inda aka samu nasarori masu yawa a mabambantan bangarori.

    Ya ce, al’ummar duniya sun yarda cewa wannan shawara tana nuna hangen nesa irin na Sin game da ci gaban dan adam, kuma tana da muhimmin tasiri wajen hada kan kasashe don samar da kyakkyawar makoma ga duniya. Har ila yau, an dauki shekaru 8 a jere ana rubuta wannan babban ra’ayi cikin kudurin MDD, kuma an sanya shi cikin sanarwar taron shugabannin kungiyar hadin kai ta Shanghai (SCO) sau 8. Haka kuma, ya shiga cikin sanarwar taron shugabannin kasashen BRICS, an kuma sanya ainihin ma’anarsa cikin yarjejeniyar nan ta “Future Pact” mai nufin samar da kyakkyawar makoma ga zuri’a ta gaba.

    Haka kuma, Ma Zhaoxu ya bayyana cewa, kasar Sin tana son mutunta juna, da zaman tare cikin lumana, da kulla hadin gwiwar samun nasara ga kowane bangare tare da Amurka, bisa tabbatar da kare muradun ikon mallakar yankunan kasarta, da tsaro da kuma ci gaban kasar.

    Ya kara da cewa, a shirye muke mu yi aiki tare da Amurka a kan turba guda, da aiwatar da muhimman yarjejeniyoyi da shugabannin kasashen biyu suka cimma, da ci gaba da sadarwa a tsakaninmu, da warware batutuwan da muka sha bamban a kai, da fadada hadin gwiwa, da kuma ci gaba da lalubo hanyar da ta dace manyan kasashen biyu su tafi tare da juna a sabon zamani.

    Jami’in ya kuma yi nuni da cewa, batun yankin Taiwan ya kasance jigo a cikin muradun kasar Sin. Kana lamarin yankin na Taiwan sha’ani ne na cikin gidan kasar Sin, kuma ba a yarda da shisshigin kasashen waje ba. Haka nan, ba za a taba iya dakatar da burin da aka sa gaba na cewa tabbas wata rana za a wayi gari kasar Sin ta dunkule wuri guda ba. (Mai Fassara: Amina Xu, Abdulrazaq Yahuza Jere)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • An kashe makiyaya 4, an jikkata wani a Filato

    [ad_1]



    An kashe makiyaya huɗu tare da jikkata wani a ƙauyen Fili, da ke yankin Doemak, a Ƙaramar Hukumar Qua’an Pan a Jihar Filato.

    Rahotanni daga yankin sun ce an kai musu hari ne lokacin da suke tsaka da kiwo.

    Sakataren kuɗi na Ƙungiyar Miyetti Allah Cattle Breeders Association of Nigeria (MACBAN) a Qua’an Pan, Saeedu Abdurrahman, ya tabbatar da lamarin.

    Ya ce ’yan bindigar sun kashe makiyayan amma ba su sace shanunsu ba.

    Ya ƙara da cewa lokacin da ake binne waɗanda suka rasu, ’yan bindigar sun sake kai wani harin, amma jami’an tsaro sun daƙile harin.

    Ɗan uwan ɗaya daga cikin waɗanda harin ya rutsa da su, Shanono Muhammad, ya ce, “An kashe makiyaya huɗu, ciki har da ƙaramin yaro da ya tafi koyon kiwon shanu.

    ’An kashe su ne da yammacin ranar Talata yayin da suke kiwo.”

    Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, mai magana da yawun Operation Safe Haven, Manjo Samson Zhakom, bai yi ƙarin haske kan harin ba.


    [ad_2]

    Source link

  • Nijeriya Da Brazil Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Bunkasa Tattalin Arziki

    [ad_1]

    Nijeriya da kasar Brazil sun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna guda biyar domin inganta bangaren kasuwanci, diflomasiyya, kimiyya, sufurin jiragen sama da kuma hadin giwa a bangaren kudade.

    Babban mashawarcin shugaban kasa kan yada labarai, Bayo Onanuga, shi ne ya sanar da wannan matakin a ranar Litinin. A cewarsa, Shugaban kasa Bola Tinubu ya yaba wa kokarin Shugaba Lula na sabunta kyakkyawar alaka a tsakanin kasashen biyu, ya nuna cewa har yanzu Nijeriya cike take da dimbin damarmakin da filayen da za su bai wa kamfanonin Brazil dama.

    Shugaba Tinubu ya yi bayanin ziyarorin da ya kai kasar Brazil a baya wanda ya nuna gayar muhimmancin da ke akwai na kyautata alakar tattalin arziki a tsakanin kasashen.

    Da yake fadada bayani kan bangarorin hadin gwiwar, Shugaba Tinubu ya nuna cewa Nijeriya a shirya take domin yin hadin giwa da kasar Brazil a bangaren musayar fasahohin zamani, wadata kasa da abinci, masana’antu, da kuma makamashi.

    “Mun daukaka wannan alkawarin domin tabbatar da shi, kamar yadda kuka gani a cikin yarjejeniyar, ban san dalilin da ya sa masana’antar magunguna, wadanda Brazil ta yi zurfi da nisa a cikinsu ba za su iya kasancewa a Nijeriya ba.

    “Ban ga dalilin da ya sa ba a raba fifikon fasaha na Brazil da Afirka ba. Mun tabbatar wa junanmu cewa mune kawai za mu iya bunkasa tattalin arzikinmu don taimakawa kasarmu,” Tinubu ya shaida.

    Tinubu ya kuma bai wa masu zuba hannun jari tabbacin cewa manufofin farfado da tattalin arzikin Nijeriya na haifar da sakamakon masu kyau a halin yanzu.

    “Sauye-sauyen da na dukufa samarwa tun lokacin da na hau kan mulkin Nijeriya suna matukar tasiri. Da farko sun yi tsanani, amma a halin yanzu ana ganin gayar sakamakon masu kyau,” ya tabbatar.

    Shi kuma a bangarensa, shugaba Lula na Brazil ya nuna farin cikinsa ne da sake sabunta kyakkyawar alaka tsakanin Nijeriya da Brazil. Ya ce, a halin yanzu da duniya ta ci gaba, akwai bangarori da daman gaske da kasashen biyu za su iya amfanar junansu.

    Ya ce kasashen biyu suna da damarmaki sosai na fadaka a matsayinsu na manyan kasashen a duniya da bakaken fata suka fi yawa, za su iya amfanar junansu musamman ta bangarorin noma, kiwo, mai da gas, taki, jirgin sama, bangaren kanikanci da sauran bangarorin da dama.

    Bayan tattaunawar ta tsawon awanni biyu, shugabannin kasashen biyu sun shaida sanya hannun fahimtar juna da aka yi a Palácio do Planalto da ke Brasília.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Sojoji Sun Ceto Mutum 117, Sun Kama Masu Laifi 150 Cikin Mako Guda

    [ad_1]

    Hedikwatar tsaro ta ƙasa (DHQ) ta ce sojoji sun ceto mutane 117 da aka yi garkuwa da su tare da kama mutane 150 da ake zargi da laifuka a faɗin ƙasar nan cikin mako ɗaya.

    Mai magana da yawun hedikwatar, Manjo Janar Markus Kangye, ya ce waɗanda aka kama sun haɗa da ‘yan ta’adda, masu satar mai, da sauran masu laifi.

    Ya ƙara da cewa, wannan kame ya bai wa manoma damar yin noma cikin kwanciyar hankali.

    A Arewa maso Gabas, sojoji sun kama masu taimaka wa ‘yan ta’adda 11, sun ceto mutane biyar sannan wani ɗan ta’adda ya miƙa wuya a Jihar Borno.

    Hakazalika, suk ƙwato makamai, kuɗi, babura da motoci.

    A Arewa maso Yamma, an kama ‘yan ta’adda 35 kuma an kuɓutar da mutane 76.

    A Arewa ta Tsakiya, an kama mutane 49, an ceto mutane 36, yayin da a Kudu maso Gabas aka kama mambobin IPOB tara.

    A Kudu maso Kudu, sojoji sun kama mutane 48, sun lalata wuraren tace ɗanyen mai, tare da ƙwato ɗanyen mai da dizal da kuɗinsu ya kai sama da Naira miliyan 443.

    Janar Kangye ya tabbatar da cewa, za su ci gaba da kai irin waɗannan hare-hare domin tabbatar da tsaro a faɗin ƙasar nan.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Masanan Kimiyya Na Kasar Sin Sun Samu Nasara A Bangaren Fasahar Sadarwar 6G Mai Amfani Da Haske Da Lantarki

    [ad_1]

    Jami’ar Peking ta kasar Sin (PUK), ta ce masanan kimiyya a kasar sun samu nasara wajen samar da fasahar da ta hada haske da lantarki ta “ultra-wideband photonic-electronic integrated technology” domin sadarwar tafi da gidanka ta 6G.

    Ta hanyar amfani da fasahohin lantarki da haske, wani ayarin masu bincike na hadin gwiwa daga jami’ar Peking da jami’ar City ta Hong Kong, sun yi nasarar samar da wani tsarin sadarwa na tafi da gidanka mai matukar sauri, irinsa na fako a duniya da ake sa ran zai inganta karfi da ingancin fasahohin 6G a nan gaba.

    A matsayin tsarin sadarwar tafi da gidanka na zamani a nan gaba, fasahar 6G na bukatar sadarwa mai matukar sauri a bangarori daban daban. Kuma domin shawo kan wannan kalubale, ayarin ya dauki tsawon shekaru 4 yana kokarin samar da tsarin sadarwar da ya hada haske da lantarki. (Fa’iza Mustapha)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Na bar APC saboda Tinubu bai cika alƙawarin da ya yi ba — Marafa

    [ad_1]



    Sanata Kabiru Garba Marafa tsohon ɗan Majalisar Dattawa da ya wakilci yankin Zamfara ta tsakiya jigo a Jam’iyar APC a jihar ya fice daga jam’iyar.

    Sanata Marafa ya bayyana ficewarsa a wani faifan bidiyo da aka wallafa a shafin Facebook a ranar Jumu’a ya ce bayan tattaunawa da magoya bayansa sun cimma matsayar barin Jam’iyyar APC kan ta zalunce su.

    “Bayan mun yi waiwaye a shekara biyu da rabi da suka gabata mun gano cewa, APC a matakin ƙasa da jiha ta zalunce mu, a matakin jiha lalacewar jam’iyar ya kai matuƙa tun bayan kafa kwamitin riƙon ƙwarya har zuwa yanzu ba a taɓa zama ko na minti biyar ba, don tattauna halin jam’iya, kuma ita ce ta fasa jam’iya gidan wane da gidan wane a haka ake tafiya.

    “Shekara biyu da rabi ba a ɗunke baraka ba, don haka mun barwa ɓangaren Sanata Abdul’aziz Yari da Minista Bello Matawalle jam’iyar.

    “Matsalar tsaro da ke addabar jihar na cikin abin da ya sa muka yi zama don duba halin da ake ciki, yanda APC ta yi na tilas sai ta yi nasara a zaɓen Ɗan Majalisa na Ƙaura da aka yi baya cikin alƙawarin da aka yi mana, shugaban ƙasa ya yi mana alƙawalin zai duba lamarin tsaro na Jihar Zamfara, hakan ya sa ya ɗauki jihohi biyu da ya ci zaɓe, ya ba su ministocin tsaro, a Zamfara ba abin da aka yi mana.”

    Kan kalaman da ake yi sun bar APC ne don ba a ba su muƙami ba ne? Ya ce haka ne, ai suna siyasa ne don su samu muƙami su amfanar da al’ummarsu, “don me wani zai tsaya takara mu yi kamfe a zaɓe shi a ƙarshe ya ce shi ba abin da zai ba mu, wannan ba adalci ba ne don haka mun jingine Jam’iyar APC.

    “A nan gaba za mu sanar da jam’iyyar da muka koma, sai a yi yaƙin gaba da gaba kana can ina nan,” kalaman Kabiru Marafa.

    Sakataren yaɗa labarai na Jami’iyar APC a Zamfara Yusuf Idris, ya ce ba za su ce komai ba kan kalaman Sanata Kabiru Marafa domin bai rubuta masu ya sanar da su ya bar APC ba tun daga kan mazaɓarsa har zuwa matakin jiha.


    [ad_2]

    Source link

  • Hakurin ‘Yan Arewa Ya Fara Karewa Kan Matsalar Tsaro – ACF

    [ad_1]

    Kungiyar Dattawan Arewa (ACF) ta yi gargadin cewa karuwar matsalolin tsaro da talauci da kalubalen muhalli na kai al’ummar arewacin Nijeriya bango. Gargadin na zuwa ne bayan taron kwamitin zartarwa na kungiyar karo na 78 wanda ya gudana a Kaduna.

    Shugaban ACF, Mamman Osuman, ya ce, arewa ba za ta ci gaba da zama shiru yayin da rayuka da dokiyoyi ke ci gaba da salwantuwa.

    Ya ce, “Yanzu ba lokaci ne na yin shiru ba. Tsaronmu na ci gaba da tabarbarewa, ana kwashe mana albarkatun kasa, sannan matsalolin muhalli su na karuwa. Dole ne arewa ta farka, ta tashi ta hada kai domin kare kanta,” ya shaida.

    Osuman ya koka kan yadda a kowace rana ake kashe rayukan mutane a yankin, ya kara da cewa, yara, mata, maza, tsofaffi duk sun fada cikin matsalolin ambaliyar ruwa, ta’addancin ‘yan bindiga dadi, ayyukan ‘yan ta’adda da sauran annobobi.

    Ya bukaci shugabannin arewa da mazauna yankin da su farka, su hada kawunansu kana su dukufa da yin addu’o’in neman zaman lafiya a yankin.

    Da yake magana da kafar BBC bayan taron, mai ba da shawara ga ACF, Bashir Hayatu Gentile, ya ce, kungiyar ta yi nazari da bitar matsalolin da suke addabar arewa tare da cimma matsayar cewa akwai bukatar daukan matakan gaggawa.

    “Matsalolin nan ga su nan a zahirance, kuma dole ne a tursasa gwamnati ta dauki mataki. Ba abun da ya fi damun arewa a halin yanzu kamar matsalar rashin tsaro, garkuwa da mutane da yawan kashe-kashe a ko’ina. Dole ne jama’an arewa su hada kawunansu su tilasta wa gwamnati yin abun da ya dace,” ya shaida.

    ACF ta kuma nuna gayar damuwa kan rahoton baya-bayan nan da kungiyar Amnesty International ta fitar da ke cewa sama da mutane 10,000 da aka kashe a yankin arewa cikin shekaru biyu kacal na mulkin Shugaban kasa Bola Tinubu.

    A cewar Gentile, kashe-kashen yana tare da yawaitar sace-sacen jama’a da kai hare-hare a kauyuka.

    Kungiyar ta soki shirun da jami’an gwamnati suka yi kan binciken na Amnesty, inda ta ce kin kalubalantar alkaluman ya nuna yadda rikicin ke da tsanani.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • An Bayyana Dalilin Obasanjo Na Tsanar Buhari

    [ad_1]

    Mai magana da yawun marigayi tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari, Malam Garba Shehu, ya mayar da martani game da tantancewar da tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, ya yi wa ubangidansa, bayan rasuwarsa, inda ya bayyana cewa, babu wani abu illa kawai tsanarsa da ya yi.

    Da yake mayar da martani ga sabon hukuncin da Obasanjo ya yanke kan gwamnatin Buhari (2015-2023), inda ya bayyana wa’adin mulkin a matsayin mafi muni a mulkin farar hula a Nijeriya, Shehu ya bayyana cewa; tuni ya bayyana dalilin da ya sa Obasanjo, bai taba son marigayi tsohon shugaban kasa Buhari ba a littafinsa da ya wallafa na baya-bayan nan.

    Sai dai ya ce, marigayi tsohon shugaban kasar yana matukar girmama Obasanjo, inda ya kara da cewa; sun yi takun-saka ne da shi a kan wata bukata tasa da ba ta biya ba.

    Shehu, a cikin littafin nasa wanda ya bai wa wakilinmu na LEADERSHIP, ya yi zargin cewa; Obasanjo ya bijiro wa Buhari da wasu bukatu a lokacin da yana shugaban kasa (Obasanjo).

    Ya kara da cewa, “Akwai da dama a kusa da Buhari da ke ganin cewa; abin ban mamakin da ya faru a tsakanin Buhari da wanda ke gabansa a aikin sojan da yake mutuntawa, Shugaba Olusegun Obasanjo, shi ne sakamakon bukatar da aka ce Obasajon ya nemi a bai wa wani dan kwangila da yake so a aikin wuta ta Mambila.

    “A kan haka, Buhari cikin ladabi ya fada wa tsohon shugaban kasar cewa, ya bar shi ya gudanar da abin da ya kamata, ta hanyar bin tsarin da ya dace; ba na son zuciya ba.”




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • An kama wani mutum da laifin kashe mahaifiyarsa kan zargin maita

    [ad_1]



    Rundunar ’yan sandan Jihar Jigawa ta kama wani matashi ɗan shekara 25 mai suna Jibrin Ado bisa laifin kashe mahaifiyarsa kan zargin maita a unguwar Gerawa da ke jihar.

    Majiyar PUNCH ta ruwaito hakan ne a ranar Alhamis daga wata sanarwa ta manhajar X ta wani masani kan harkokin tsaro, Zagazola Makama.

    A cewarsa, Ado ya aikata wannan aika-aika ne tare da wasu masu laifin a ranar Talata.

    Waɗanda suka haɗa da: Musa Kwalle da Dan Abba da Sule Musa da wani Arrow dukkansu daga ƙauyen Gerawa.

    Majiyar ta bayyana cewa, a ranar 26 ga watan Agusta da misalin ƙarfe 4:30 na yamma, wanda ake zargin mai suna Jibrin Ado na ƙauyen Daneji, ya haɗa baki da wasu – Musa Kwalle da Ɗan Abba, Sule Musa da Arrow, dukkansu ’yan ƙauyen Gerawa, inda suka shiga gidan mahaifinsa, Adamu Saleh.

    “Waɗanda ake zargin sun yi wa matarsa (Saleh) duka, Magajiya Ado, ‘yar shekara 50 da manyan sanduna har sai da ta sume, suna zarginta da maita,” ya rubuta.

    Makama ya ci gaba da cewa, an garzaya da mamaciyar zuwa babban asibitin unguwar Ringim da ke unguwar, inda ta rasu a lokacin da take jinya.

    “Majiyoyi sun ce tuni aka sako gawarta ga ’yan uwa don binne ta, majiyar ta ƙara da cewa an kama ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin Jibrin Ado, yayin da sauran kuma ke hannunsu”.

    Da aka tuntubi jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, Lawan Shiisu ya yi alƙawarin binciken lamarin tare da yin ƙarin bayani nan gaba. Har yanzu bai yi haka ba har zuwa lokacin da aka gabatar da rahoton.


    [ad_2]

    Source link

  • Mutane Da Dama Sun Tsere Sakamakon Harin ‘Yan Bindiga A Neja Da Kwara

    [ad_1]

    Mazauna garuruwa daban-daban a Jihohin Neja da Kwara, sun tsere daga gidajensu, sakamakon hare-haren da ‘yan bindiga suka kai musu. A Jihar Neja, da yawan mazauna Karamar Hukumar Mariga, sun yi gudun hijira a ranar Litinin sakamakon farmakin da ‘yan bindiga suka kai musu.

    Har ila yau, ‘yan bindigar sun kai farmaki a yankunan da lamarin ya shafa, tun daga karfe 11 na safe har zuwa karfe 5 na yamma, inda suka yi awon gaba da shanun mazauna garin. An kuma samu labarin cewa, ‘yan bindigar sun tafi da wasu yara da ke kamun kifi a kogi, yayin kuma da aka ce; an harbe wani manomi a kusa da kauyen Dusai.

    Wakilinmu ya tattaro cewa, a halin yanzu mazauna garin Ragada da sauran al’ummomin da ke makwabtaka da su, sun samu mafaka a Gulbin-Boka da ke Karamar Hukumar Mariga.

    Da aka tuntubi Kwamishinan Tsaron Cikin Gida, Birgediya Janar Bello Abdullahi Mohammed mai ritaya, ya tabbatar da faruwar al’amarin, amma ya ce; jami’an tsaro sun shawo kan lamarin.

    Haka zalika, mazauna Ndanaku da ke Karamar Hukumar Patigi a Jihar Kwara, sun kauracewa wurin sakamakon hare-haren ‘yan bindiga. Kazilika, harin na zuwa ne makwanni kadan bayan faruwar makamancin haka a garin Babanla da ke Karamar Hukumar Ifelodun.

    Kwamandan ‘yan banga, Gina Gana; wanda shi ma yana daya daga cikin wadanda suka tabbatar da faruwar lamarin, ya bayyana cewa; an kai hare-hare guda biyu ne kwanaki uku da suka gabata, wanda ya tayar wa da kowa hankali a garin.

    Har wa yau, a makon day a gabata ne Gwamna AbdulRahman AbdulRazak, ya yi taro da wasu masu ruwa da tsaki na Ifelodun, inda ya yi bayani dalla-dalla kan kokarin da suke yi na magance matsalar rashin tsaro. Da yake magana a kan hadin gwiwa da ofishin mai bai wa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro da sauran dukkanin hukumomin tsaro, gwamnan ya bayyana cewa; ana yin dukkanin abin da ya kamata, domin kawar da duk wata barazana ta tsaro a jihar, ciki har da Ifelodun, Patigi da Edu.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link