Category: Latest News

  • INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

    [ad_1]

    Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta nuna matukar damuwarta game da rashin amsar katunan zabe har guda 360,000 a Jihar Kano.

    Kwamishinan zabe Jihar Kano, Ambasada Abdu Zango, shi ya sanar da hakan a ranar Asabar lokacin da ya karbi mambobin kwamitin da gwamnan Jihar Kano ya kafa don kara wayar da kan jama’a game da sabon rajistar masu kada kuri’a da ake gudanarwa a yanzu.

    Kwamitin da ke karkashin shugabancin kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Kwamade Ibrahim Abdullahi Waiya, ana sa ran zai wayar da kan masu kada kuri’a kan muhimmancin karbar katin zabensu da kuma shiga cikakken harkokin jefa kuri’a a lokacin zabe.

    Ambasada Zango ya ja hankali kwamitin da ya kara zage damtse wajen yin gaggami, yana mai cewa dukkan katunan da ba a amsaba har yanzu suna hannun INEC.

    Ya yaba wa gwamnatin jihar da ta kafa wannan kwamiti, yana mai cewa mambobin kungiyar da shugabanin Waiya za su taimaka wajen gudanar da wannan aiki cikin nasara.

    Ya kuma tabbatar da cewa kwamitin zai hadin kai da INEC wajen wayar da kan masu zabe kan sabon rajistar da kuma amsar katunan zaben.

    Da yake magana a fadar gidan gwamnatin Jihar Kano, kwamishinan yada labaran ya bayyana cewa Gwamnan Jihr Kano, Abba Kabir Yusuf ne da kansa ya kafa kwamitin don shigar da dukkan kungiyoyi a cikin jihar, ciki har da jam’iyyun adawa, domin karfafa shigar kowa cikin harkokin zabe.

    Ya bukaci INEC da duba yuwuwar karin adadin wuraren jefa kuri’a a Kano don saukaka cunkoso a lokacin gudanar da zabe.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Sin Ta Sanar Da Rukuni Na Hudu Na Abubuwa Da Wuraren Tunawa Da Yakin Kin Jinin Mamayar Dakarun Japan

    [ad_1]

    A ci gaba da shirye-shiryen bikin ciki shekaru 80 da cimma nasarar yakin kin jinin mamayar dakarun Japan, da yakin kin tafarkin murdiya, majalisar gudanarwar kasar Sin ta sanar da tabbatar da rukuni na hudu na abubuwa da wurare 34, don tunawa da yakin kin jinin mamayar dakarun Japan a matakin kasa. A nata bangare kuma, ma’aikatar lura da harkokin da suka shafi tsofaffin sojoji ta kasar Sin, ta fitar da sanarwa mai kunshe da bayanai, game da ayyana rukuni na hudu na wasu shahararrun jarumai da gungun jarumai 43 da suka sadaukar da ransu, yayin yakin kin jinin mamayar dakarun Japan.

    Sanawar da ta fito daga majalisar gudanarwar kasar Sin, ta shaida cewa ya wajaba dukkanin yankunan kasar, da sassan hukumomi masu ruwa da tsaki su karfafa kariya, da kula da abubuwa da wurare masu tunatarwa game da yakin kin jinin mamayar dakarun Japan, kana a yi aiki bisa tsanaki wajen tonowa, da rarrabewa, da yayatawa, da baje kolin abubuwan tarihi, da na al’adu, da ayyukan ’yan mazan jiya masu nasaba da batun.

    Sa’an nan a dage wajen yayata ruhin kishin kasa, da na yakin kin jinin mamayar dakarun Japan, da bunkasa manufar dunkulewar kasa waje guda. (Saminu Alhassan)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

    [ad_1]

    Duk da irin mawuyacin hali da babbar jam’iyyar adawa ta PDP take ciki, kan babban taronta na kasa a watan Nuwamba na wannan shekara, wani sabon rudani ya kara turnuke shugabannin jam’iyyar adawa sakamakon yadda jam’iyya mai mulki ta APC take zawarcin wasu gwamnonin PDP.

    Rahotanni na nuna cewa jam’iyyar PDP na dab da rasa wani gwamna daga yankin kudu, wanda aka bayyana cewa a yanzu haka ya kammala shirye-shiryen sauya sheka shi da magoya bayansa.

    Jam’iyyar PDP na fama da matsaloli masu yawa wanda har ta kai ga rasa gwamnoni biyu wadanda suka koma jam’iyyar APC a cikin watannin da suka gabata, amma jam’iyya na ci gaba da kare kanbunta, yayin da aka tabbatar da cewa Shugaba kasa Bola Tinubu idan ya dawo daga daga ziyarar kasashen waje zai karbi wani gwamna na PDP wanda zai sauya sheka daga PDP zuwa jam’iyyar APC.

    “Zan iya tabbatar muku da cewa an kammala dukkan sharye-sherye na sauya shekan wani gwamna na PDP zuwa cikin APC. Ana ganin wannan gwamna a matsayin gwamna mai aiki tukuru da kwazo wanda yake da farin jini sosai a fagen siyasa a jiharsa. Abin da zan iya cewa a yanzu shi ne, ya kasance yana bangaren jihohin kuduncin Nijeriya ne. Mun gama dukan wasu shirye-shirye, muna jiran dawowar shugaban kasa daga kasashen waje don bayyana ficewarsa a hukumance,” in ji wata majiya.

    Duk da cewa majiyar bai ambaci sunan gwamnan da abin ya shafa ba, idan zama a iya tunawa dai PDP tana da matukar karfi a bangaren siyasar kudancin Nijeriya. A kudu maso gabas, Gwamnan Jihar Inugu, Peter Mbah ne kawai daga jam’iyyar PDP, yayin da a kudu maso kudu a yanzu haka dai akwai gwamnan da aka dakatar Sim Fubara na Jihar Ribas da Gwamnan Jihar Bayelsa, Duoye Diri, yayin da kudu maso yamma ma tana da gwamnonin biyu ciki har da Seyi Makinde na Jihar Oyo da Ademola Adeleke na Jihar Osun.

    APC za ta iya samun gagarumin rinjaye a jihohin kudu maso yamma idan Gwamna Mbah ya koma jam’iyyar, wanda shi ne kadai gwamnan PDP a wannan yanki, domin hakan zai daukaka yawan gwamnonin APC zuwa uku a wannan yanki. Haka nan lamarin zai iya faruwa a yankin kudu maso kudu idan Gwamna Fubara ko Gwamna Diri suka koma jam’iyyar APC daga jam’iyyar adawa ta PDP. Saboda haka, yawan gwamnonin a kudu maso kudu na iya karuwa daga biyar zuwa shida.

    Majiyoyi da ke kusa da APC da PDP sun ce daya daga cikin gwamnonin PDP ya riga ya fice daga jam’iyyar PDP, kuma Shugaban kasa Tinubu zai karbi gwamnan zuwa APC lokacin da ya dawo daga tafiya.

    Haka kuma majiya daga daya daga cikin gwamnonin yankin kudu ya tabbatar da cewa a daga cikin gwamnonin PDP na yankin kudu cewa ya riga ya fice daga PDP, kuma ko da yake gwamnan tun da farko yana son zama a cikin jam’iyyar don yin aiki tukuru wajen ganin an sake zaben Shugaban kasa Tinubu a 2027, an bayyana cewa ya dauki matakin barin PDP ya koma APC domin hakarsa ta cimma ruwa.

    “Ya dai koma APC ne don samun nasarar ganin ya karfafa jam’iyyar a jihohin kudu da kuma samun karfi a arewa ta tsakiya da sauran yankunan Nijeriya gaban zaben 2027. Tuni dai mun karbi gwamnonin Delta da Akwa-Ibom a cikin jam’iyyar, kuma za mu ci gaba da amsar wasu a nan gaba,” in ji wata majiya.

    An bayyana cewa sabon shirin da aka yi na ganin karin gwamnonin PDP sun fice zuwa jam’iyyar da ke mulki an kawo ta ne saboda abubuwan da ke faruwa a cikin jam’iyyar adawa ta ADC, inda aka fara samun labarai cewa jam’iyyar na iya amfani da tsarin karba-karba wajen fitar da dan takara a zaben 2027. An ruwaito cewa APC na shirin samun gagarumin nasara a kudu don rage tasirin da ake tunanin wani dan takara daga kudu zai iya yi, idan har dan takarar ADC ya fito daga wannan yankin.

    Wata majiya ta ce, “Muna ganin cewa ADC na sake gabatar da wasu dubaru ta hanyoyi daban-daban. Idan wannan jam’iyyar ta tsayar da tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar daga arewa maso gabas, hakan zai rage samun kuri’un kudancin kasar nan. Amma idan wannan jam’iyyar ta tsayar da wani dan takara daga kudu, hakan zai jawo hankalin shugaban da ke kan mulki, wanda zai bukaci ya tabbatar da karfin iko a wannan yanki. Wannan shi ne dalilin da ya sa jam’iyyar da kuma fadar shugaban kasar ba sa barin abubuwa su je ba tare da tsari ba ta hanyar mai da hankali kan zawarcin masu gwamnonin PDP masu tasiri.”

    Kazalika, an bayyana cewa cikin gwamnonin da APC ke zawarci sun hada da Gwamnan Jihar Inugu, Peter Ndubuisi Mbah, Gwamnan Jihar Bayelsa, Douye Diri, Gwamnan Jihar Filato, Caleb Muftwang da Gwamnan Jihar Zamfara, Alhaji Dauda Lawal.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Kasar Sin Sun Gudanar Da Hada-Hada Bisa Daidaito Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Nan

    [ad_1]

    Kamfanoni mallakin gwamnati da wadanda gwamnatin kasar Sin ke sarrafa su, sun gudanar da hada-hada bisa daidaito cikin watanni bakwai na farkon shekarar nan ta 2025, inda adadin jarinsu ya daidaita, kana ribar da suke samu ta dan ragu kadan.

    Alkaluman da ma’aikatar kudin kasar ta fitar a Jumma’ar nan, sun nuna yadda adadin jarin wadannan kamfanoni ya kai yuan tiriliyan 47.31, kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 6.66, tsakanin watan Janairu zuwa Yulin bana, adadin da ya yi daidai da na shekarar bara.

    Alkaluman sun kuma nuna ribar da wadannan kamfanoni suka samu a watannin bakwai na farkon shekarar bana ta kusa yuan tiriliyan 2.48, adadin da ya dan ragu da kaso 3.3 bisa dari a mizanin shekara. (Saminu Alhassan)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Tottenham Ta Ɗauki Xavi Simons Daga RB Leipzig

    [ad_1]

    Tottenham ta kammala sayen ɗan wasan tsakiyar ƙasar Holland, Xavi Simons, daga RB Leipzig kan kuɗin fam miliyan 51.8 (€60m).

    Ɗan wasan mai shekaru 22 ya ce tun da daɗewa yake mafarkin wannan dama, bayan ya kammala gwajin lafiya a kulob ɗin da Thomas Frank ke jagoranta.

    Simons ya buga wasanni 78 a Leipzig, inda ya zura ƙwallaye 22 tare da taimakawa aka ci ƙwallaye 24.

    Ya dawo Leipzig ne a matsayin aro daga PSG a 2023, kafin ya sanya hannu kan kwantiragi a farkon wannan shekara.

    Haka kuma ya buga wasanni 28 tare da ƙasar Holland, inda ya ci ƙwallaye biyar, tun bayan gasar cin kofin duniya a Qatar 2022.

    “Tottenham babbar ƙungiya ce, kuma tun lokacin da na haɗu da kocin, na fahimci wannan shi ne wurin da ya dace a gare ni,” in ji Simons, wanda aka dade ana dangantawa da komawa Chelsea.

    Kocin Tottenham, Frank, ya bayyana cewa Simons ya rattaba hannu kan yarjejeniya mai tsawo, kuma babban abin da kulob ɗin ke nema ne saboda duk da ƙarancin shekarunsa, ya riga ya samu gogewa sosai.

    Simons shi ne na uku da Tottenham ta dauko a bana bayan Joao Palhinha da Mohammed Kudus. A da Chelsea ta yi tattaunawa da Leipzig domin daukarsa, amma daga baya ta janye saboda tana kokarin kammala cinikin Alejandro Garnacho daga Manchester United akan fam miliyan 40.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Akwai Bukatar Gwamnonin Arewa Su Yi Koyi Da Jihar Legas Wajen Bunkasa Albarkatun Fatu

    [ad_1]

    Lokacin da Gwamna Babajide Sanwo-Olu na Jihar Legas ya kaddamar da kamfanin fata na Mushin, wato ‘Industrial Leather Hub’ tare da hasashen samun kudaden fitarwa na shekara-shekara na Naira biliyan 387.5, hakan sai ya bayyana wani babban rashin daidaito a ci gaban Nijeriya.

    Legas, ba ta da wani tushe na kiwo, amma ta nuna jagoranci da hangen nesa, yayin da Arewacin kasar da ke da yawan dabbobi da fatu suka gaza wajen bunkasa a fannin fata ba.

    Wannan rubutu ya yi nazari ne kan yanayin masana’antar fata ta duniya da ta cikin gida, wanda kuma itace damar da Nijeriya ta rasa, gudunmawata a matsayin tsohon Shugaba/ Darakta Janar na NILEST, ya zama dole gwamnonin Arewa su dauki matakan gaggawa don farfado da wannan sashe.

    Tare da jagoranci da zuba jari, Nijeriya na iya samun fiye da Dala biliyan 4 a shekara a kudaden fitar da fata, kirkirar miliyoyin ayyukan yi, da kuma dawo da matsayin tarihi a matsayin babbar mai karfi a duniya a fannin fata.

    Misali daga Jihar Legas

    Jihar Legas kwanan nan ta kaddamar da Mushin Industrial Leather Hub, da nufin samar da kudaden fitarwa na Naira biliyan 387.5 a kowace shekara. Wannan abin ban mamaki ne, idan aka yi la’akari da cewa Legas ba ta da wani tushe a fannin kiwo. Wannan kaddamarwar tana nuni wani rashin daidaito: a yanzu dai Legas ce ke jagoranci tare da hangen nesa da tsara dabarun da ya kamata a ce jihohin Arewa ne ke kai, wadanda ke da yalwar kiwo, amma an bar su a baya. Wannan na haifar da ayar tambaya cewa: me ya sa Legas ke jagorantar masana’antar fata yayin da a ce Arewa ce Arewa ce ta yi fice akan hakan?

    Harkar Fatu A Duniya

    Masana’antar fata ta duniya tana da kimar samun fiye da Dala biliyan 400 a duk shekara, inda kasuwannin kayan kwalliya, takalma, motoci, da kayayyakin alfarma ke tafiyar da shi. Afirka na bayar da kusan kashi 30 na fata da ba a sarrafa ba na duniya amma tana bayar da kashi 6 ne kawai na fitar da fata da aka sarrafa, wanda kimarsa ta kai Dala biliyan 3.5.

    Kasar Morocco kadai na samun fiye da Dala miliyan 500 a shekara daga fitar da fata da aka gama sarrafawa. Wani abin ban dariya shi ne shahararriyar fatar Morocco, wanda aka saba kira da ‘Morocco Leather’, an yi ta ne daga fatar akuya da asalinta daga Sakkwato take wato ‘Sokoto Red, wacce asalin ta daga Arewa Nijeriya ce.

    Yayin da Morocco ta samu suna mai karfi a duniya, Nijeriya ta bari karfinta ya ragu, ta rasa damar..

    Arzikin Da Ke Tattare Da Harkar Fatu A Nijeriya

    Nijeriya na daya daga cikin manyan masu samar da fata daga fatar dabbobi a Afirka, inda dabbobi ke da yawa a jihohin Arewa kamar Kano, Sokoto, Katsina, Bauchi, da Borno. Wannan sashi na masana’antu yana daukar ma’aikata kusan 750,000, ciki har da sama da 500,000 a kananan masana’antar kayan karshe kamar takalma da jakunkuna. Duk da haka, fiye da kashi 90 na fatar Nijeriya ana fitar da ita ce kawai a asalinta ko kafin sarrafawa, wanda ke hana kasar samun karin kima da kudaden fitarwa mafi girma.

    Tsofaffin gungun masana’antar fata da suka bunkasa a Kano da Sokoto sun ragu, inda fiye da masana’antar fata 40 suka rufe a cikin shekaru ashirin da suka gabata.

    Na Kafa Gaggarumun Ginshiki A Jagorancina A NILEST

    A matsayina na Shugaba/Daraktan Janar na Nigerian Institute of Leather and Science Technology (NILEST), na gane cewa fata wani muhimmin jigo ne wajen tsara manufofin bambance-bambancen tattalin arzikin Nijeriya. Na jagoranci shirye-shiryen sauyi wadanda suka kafa tubalin farfado da masana’antar.

    Kafa sabbin Cibiyoyin Horarwa da Fadada Ilimin Fata guda 23 a fadin kasa, don tabbatar da cewa kwarewar fata da horo sun isa kowane sashe na Nijeriya.

    Kirkirar shirye-shiryen farfado da masana’antar fatu da taswirar fasaha ga manyan gungun masana’antar Arewa.

    Jagorancin Kwamitin Kula da Manufofin Fata da Kayayyakin Fata na Kasa, wanda ya samar da cikakkiyar manufar fata ta farko a Nijeriya.

    Hadin gwiwa da kasashen waje, ciki har da ziyara zuwa Portugal don samun hadin gwiwa a fannin canja fasaha, horo, da samun damar kasuwa.

    Zuba jari a bincike da ci gaba, tare da mai da hankali kan hanyoyin tanning masu tsabtace muhalli da kirkirar kayayyaki.

    Shirye-shiryen horo da suka ba da karfi ga masu sana’a, matasa, da mata a fannin kimar fata.

    Dalilin Nasarar Legas, Arewa Kuma Aka Yi Shiru

    Legas na bunkasa ne saboda hangen nesa, kayan aiki, da shugabanci. Gwamnatinta ta jajirce wajen masana’antu, ba tare da la’akari da albarkatun kasa ba. Arewa, a dayan hannun kuma, tana ci gaba da dogaro da dabbobi ba tare da hada shi da manufofi, zuba jari, ko hangen nesa ba. Wannan gibin shugabanci shi ne ke bayyana dalilin da ya sa Legas ke kan gaba wajen fitar da fata, yayin da Arewa ke ci gaba da zama mai samar da albarkatun fatar na asali.

    Hanyoyin Da ZA A Bunkasa Harkar Fatu A Arewa

    Domin cimma burin karfafa masana’antar fata, Arewa Nijeriya dole ne ta kammala tsarin ta hanyar canzawa daga fitar da fata a asali zuwa samar da kayayyaki masu kima. Muhimman hanyoyi sun hada da:

    a. Bukatun Manufofi:

    Tilasta takunkumi kan fitar da fata a asali.

    Sabunta Mahauta (abattoirs).

    Karfafawa wajen farfado da masana’antar tanning da zamani.

    Hada ci gaban fata cikin manufofin masana’antu na jiha.

    b. Dabarun Zuba Jari:

    Gina hadin gwiwar gwamnati da masu zaman kansu wajen bunkasa masana’antar tanning da cibiyoyin masana’antu.

    Jan hankalin masu zuba jari na kasashen waje tare da karfafawa ta musamman.

    Hada cibiyoyin masana’antar fata da yankunan tattalin arziki na musamman (special economic zones).

    c. Ayyukan Yi da Tasirin Al’umma:

    Fadada ayyukan yi a wannan sashe zuwa miliyan 1.5–2 a cikin shekaru goma masu zuwa.

    Ba da fifiko ga hadin kan matasa da mata a cikin gungun masana’antar fata.

    d. Hasashen Fitarwa

    Nijeriya na iya samun Dala biliyan 4 a fitar da fata shekara-shekara nan da 2030.

    Samun isasshen lokaci: samun kashi 5 zuwa 10 na fitar da fata da aka sarrafa a duniya, wanda kimarsa ta kai Dala biliyan 20 zuwa 30.

    Nazarin Yadda Lamarin Yake A Morroco da Sakkwato

    Fatar Morocco ta zama shahararriyar alama a duniya, duk da cewa ta samo asali ne daga akuya kuma daga Jihar Sakkwato wato ‘Sokoto Red. Morocco ta gina karfi wajen nuna alama, gungun abin da ake fitarwa, da tsarin masana’antu, yayin da Nijeriya ke fitar da fata ta asali. Darasin shi ne a fili: alamar kasuwanci, manufofi, da hangen nesa ne ke kirkirar masana’antu masu karfi a duniya.

    Shawarwari Ga Gwamnonin Arewa

    Kafa cibiyoyin masana’antar fata na jiha da na masu zaman kansu, da hada su da cibiyoyin NILEST.

    Tallafa wa hadakar masana’antar tanning da fasaha ta zamani da kuma samar da kudi.

    Hadin gwiwa da cibiyoyin masana’antu na Legas da na kasashen waje don karfafa sarkar kimar fata.

    Karfafa kafa Kwamitocin Kimar Fata a kowace jiha.

    Karfafa zuba jari daga ‘yan kasa a waje da sashin masu zaman kansu a kayayyakin fata da aka gama sarrafawa.

    Bukatar Samar Da Kyakyawan Shugabanci

    Legas na da karancin dabbobi amma tana da hangen nesa mai yawa. Arewa na da yalwar dabbobi amma babu shugabanci. Arziki ba ya fitowa daga albarkatu kadai ba, sai daga hangen nesa, manufofi, da aiki mai manufa. Arewa ba za ta iya ci gaba da zama ‘yar kallo kawai a juyin juya halin masana’antar fata ta Nijeriya ba.

    Ta hanyar gini kan tubalan da aka kafa a NILEST, cibiyoyi 23, tsarin farfado da masana’antar tanning, hadin gwiwar kasa da kasa, da manufofin kasa, shugabannin Arewa za su iya sanya Nijeriya ta zama mai karfin samar da fata a duniya. ‘Sokoto Red goat’, masana’antar Kano’s tannery heritage, da yalwar dabbobi a Bauchi da Maiduguri’s libestock wealth’ dole ne a yi amfani da su ba a matsayin kayan fitarwa a asali ba, har ma a matsayin kayayyakin karshe da za su samar da ayyukan yi, kudin waje, da alfahari.

    Idan Legas na iya yin mafarki na samun kudaden fitar da fata ta Naira biliyan 387.5 ba tare da dabbobi ba, Arewa na iya cimma fiye da haka da yalwar albarkatunta, muddin ta zabi hangen nesa maimakon zamanta haka nan.

    Farfesa Muhammad Kabir shi ne tsohon shugaban Cibiyar kimiyyar Sarrafa Fatu (NILEST) da ke Zariya. Kuma shi ne tsohon shugaban tsare-tsare na kasa na kwamitin shugaban kasa kan bunkasa fatu a Nijeriya.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Mutum 12 sun nutse bayan sake kifewar jirgin ruwa a Sakkwato

    [ad_1]



    An sake samun damuwar kifewar jirgin ruwa a Ƙaramar hukumar Shagari inda jirgin ruwa ya nutse da mutane 12 a Ƙaramar hukumar ta Jihar Sakkwato wanda ya yi sanadin mutuwar mutum biyu namiji da mace sauran 10 suka samu raununka.

    Hatsarin ya faru ne da daren ranar Alhamis a gulbin Shagari inda mutane suka shiga cikin damuwa da kaɗuwa kan jirgin daya nutse da mutane da babur guda biyu da sauran kayan amfani, a wata ɗaya jirgi uku ya nutse a ruwa a Sakkwato.

    Nasir Umar wanda lamarin ya faru gaban idonsa ya ce, “jirgin ya nutse da mutane 12 da ya ɗauko daga garin Jaranja zuwa Ruggar Buda a mazaɓar Lambara,  kan hanyar ne ya kife a daren Alhamis  aka fitar inda mutum biyar sun samu rauni.

    “Mutanen gari da suka kawo ɗauki ne suka taimaka kuma su ne suka ci gaba da aikin harranar Jumu’a, an yi nasarar fitar da mutum shida, biyar a raye ɗaya ya mutu, mace guda ta bata ba a ganta ba.

    “Kan zurfin ruwan har yanzu ba a samu ceto mace daya da ta rage a ruwan ba, ana dai sa ran ba ta da rayuwa a yanzu,” a cewarsa.

    Ya yi tir da halin da gwamnati ta nuna kan lamarin in da har aka ciro mutanen ba wani wakilin gwamnati da ke wurin, mutane ne suke taimakon junansu a gaban Sarkin Ruwa.

    Kabir Lumu ya nuna kifewar jirgi da ake samu a kwanan nan sakaci ne na gwamnati domin ta ƙi samar da hanyoyin mota a wuraren da ruwa suka mamaye kuma sun ƙi samar da tsari mai kyau a harkar sufurin jiragen, sun ƙyale talakawa suna kowa tasa ta fishshe shi, matuƙar Gwamnatin Sakkwato ba ta dawo cikin hayyacinta ba kan wannan matsalar za a ci gaba da rasa mutane a jirgin ruwa.

    A lokacin da yake tabbatar da faruwar lamarin mai bai wa gwamnan Sakkwato shawara kan Hukumar ba da agajin gaggawa ta jiha, Aminu Liman Bodinga ya ce sun tura jami’ansu inda lamarin ya faru don ba da taimakon da ake buƙata.


    [ad_2]

    Source link

  • An Gabatar Da Shirin Musayar Al’adu Na “Echoes Of Peace” A Mexico

    [ad_1]

    A ranar 23 ga watan Augusta aka gabatar da shirin musayar al’adu mai taken “Echoes of Peace” a birnin Mexico na kasar Mexico. Cikin jawabin da ya gabatar ta kafar bidiyo, Mr.Shen Haixiong, shugaban babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin CMG, ya ce yana farin cikin gayyatar baki su hallarci wajen gabatar da shirin domin a waiwayi tarihi tare a kuma fahimci abun da ya faru, wanda tasirinsa ya keta lokaci da yankuna.

    Ya ce a shirye kafar CMG take ta zurfafa hada hannu da abokan hulda na kasa da kasa wajen hada kai domin shawo kan kalubale da neman ci gaba ta hanyar hadin gwiwa. (Fa’iza Mustapha)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Kungiyar Masana’antu Ta Yi Fatali Da Sake Gabatar Da Haraji Na Kaso 4 Na Kwastom

    [ad_1]

    Kungiyar Masana’antu ta Nijeriya (MAN) ta yi fatali da sake gabatar da harajin kaso hudu na (FOB) da hukumar Kwastam ta gabatar wanda ya fara aiki tun daga ranar 4 ga watan Agustan.

    Darakta janar na MAN, Mista Segun Ajayi-Kadri, ya shaida hakan a Jihar Legas, wanda ya matakin ya saba wa dakatar da cajin da gwamnati ta yi tun da farko.

    Ya ce masana’antu suna kallon matakin zai kara janyo tsadar farashin shigo da kayayyakin sarrafa abubuwa, albarkatun kasa, injuna, da sauran kayayyakin da ba a samu a cikin gida ba.

    Ajayi-Kadri ya ce kungiyar ta yi cikakken nazari kan sake gabatar da harajin na FOB wanda ta tabbatar zai kara dagula lamura ne kawai da sake jefa masana’antu cikin mawuyacin hali.

    “Gaskiyar lamarin ita ce, farashin kashi hudu cikin 100 na kamfanonin ya yi yawa fiye da yadda aka samu karin kashi bakwai cikin dari da kuma karin kashi daya cikin dari na harajin tsarin shigo da kayayyaki,” in ji shi.

    Ya kara da cewa, a sauran kasashen yammacin Afirka kamar Ghana, Cote d’Iboire, da Senegal, ana tsare-tsaren da aka yi niyya ko tattara kudade a tsakanin kashi 0.5 zuwa kashi daya cikin 100 na FOB, tare da karin haraji kawai kan kayan alatu ko kuma wadanda ba su da muhimmanci a shigo da su.

    “Hukuncin da hukumar kwastam ta Nijeriya ta yi na bai daya na kakaba harajin kashi hudu cikin 100 na FOB zai kara tsadar kasuwanci, da karfafa hanyoyin da ba a saba gani ba, zai haifar da karkatar da kaya da kuma kara tsanani,” in ji shugaban.

    Ajayi-Kadri ya nemi gwamnatin tarayya da hukumar Kwastam da su janye matakin kakaba harajin kaso hudu na FOB domin kyautata tattalin arziki ko kuma a jinkita aiwatar da hakan har sai nan gaba.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • ’Yan sanda da Sojoji na binciken dalili a Bauchi

    [ad_1]



    Rundunar ’yan sandan Jihar Bauchi ta kafa kwamitin bincike mai ƙarfi na ƙwararrun jami’an tsaro tare da haɗin gwiwar rundunar ‘sojan Najeriya, domin gano abin da ya jawo aka kashe wani jami’in soja da wani sifeton ’yan sanda ya yi a jihar kwanan nan.

    Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ’yan sanda (PPRO), CSP Ahmed Mohammed Wakil ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai a madadin Kwamishinan ’yan sandan, Sani-Omolori Aliyu a hedikwatar rundunar da ke Bauchi a ranar Juma’a.

    Wakil ya ce, an ɗora wa kwamitin alhakin tattarawa da tantance duk bayanan da suka dace da suka shafi wannan lamari da kuma abubuwan da suka faru nan take”,

    A cewarsa, masu binciken za su bi dukkan ƙa’idojin ƙwarewa na aikin bincike su ɗauki matakai da suka dace don samar da sahihin sakamakon bincike mai tushe da za a dogara da shi, Kuma ya zamo bincke ne da zai kawar da rashin tabbas da kuma tabbatar da cewa, an samu adalci ta hanyar yin nazari sosai.

    Dangane da batun zargin haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba da kuma rakiyar jami’in tsaro  ba bisa ƙa’ida ba.

    Kakakin ‘yan sandan ya bayyana cewa, “Bincike na farko, ya nuna cewa motar tana da alaƙa da kamfanin  Guruje Mining Company Limited da ZURFI Company Limited, waɗanda ke da ingantaccen lasisin haƙar ma’adinai bisa doka a Gwana, ƙaramar hukumar Alƙaleri. Wannan izini ya shafi haƙar ma’adinan Zinc, wanda aka samu daga ofishin Kula da ma’adinan na Tarayyar Najeriya, daga ranar 12 ga Mayu 2023.

    Waɗannan kamfanonin sun yi aiki tare da kamfanin Minco. Ƙarƙashin Dokar 2007 kuma sun mallaki takardar shaidar ƙa’idojin Kamfanoni na 2020.

    “Kuma sun buƙaci jami’an ‘yan sandan da za su kare su  waɗannan kamfanoni a hukumance kuma an amince da su an kuma basu ’yan sanda don samar da tsaro don kare lafiyar ma’aikatan da suka fito daga ƙasashen ƙetare da kuma sauran ayyukan tsaro da ke da alaƙa da kamfanin.

    Sufeto Yusuf Ibrahim na daga cikin wadanda aka bai wa wannan aiki, ya ce “Kamfanin ya yi nasarar fitar da wani adadi mai yawa na ma’adanai na zinc, waɗanda aka gabatar da su don fitar da su, kuma sun biya dukkan kuɗaɗen da suka dace a matsayin kuɗaɗen shiga da aka biya ga Ma’aikatar Ma’adinai da ta Tarayya da lambar rasiti mai lamba 3212-7561-4841 Kamar yadda yake a doka”.

    Ya kuma shawarci ’yan jarida da kada su yi ƙasa a gwiwa wajen yin ayyuka na aikin jarida na binciken gaskiya da nufin tabbatar da haɗin kan ƙasa da nuna kishin ƙasa.


    [ad_2]

    Source link