Category: Latest News

  • Tarihin ‘Yan Majalisar Farko A Nijeriya Kafin Zamanin Mulkin Mallaka

    [ad_1]

    Tun farko kafin fara yin mulkin mallaka Sarakunan gargajiya sune suka kasance tamkar ‘yan majalisa, irin na wakilai da kuma Dattawa da ake da su yanzu, lokacin ana da sassa uku da suka hada da Arewaci, Yammaci, da kuma Kudanci, an kafa sune a matsayinsu na Sarakunan gargajiyar, da kuma sauran masu tafiyar da al’ummar su a gargajiyance, saboda su samu damar yin wasu ayyuka tamkar a gwamnatance ne kafin,da kuma lokacin mulkin mallaka. Sune suka kasance kamar ‘yan majalisar Dattawa a tsarin majalisa irin na tsarin majalisa na na tsarin mulkin bicameral na Turawa, a wasu sassan Nijeriya kafin a daina yin amfani da tsarin lokacin da aka yi gyare- gyare a tsarin mulkil.

    Tsarin mulkin gargajiya shi aka fara amfani da shi kafin lokacin mulkin mallaka ya bayyana ta yadda suke lura da lamurran da suka shafi aikin gona da albarkar kasa, a wasu kananan larduna ko sashe, da kuma sauran da suke ana iya kiransu da sunan Jiha daga shekarar 1400 zuwa 1800. A tarihance Sarakunan gargajiya na Arewanci da kuma Shugabannin gargajiya a sashen Kudanci suna yin ayyukan da suka shafi addini, kasance kamar kotuna,da kuma tafiyar da harkokin mulki. Zamanin mulkin mallakar da aka fi sani da indirect rule, da aka yi amfani da shi a Nijeriya inda a lokacin Sarakunan gargajiya ne, suka zama tamkar gwamnati a gargajiyance, saboda ai har ma kiransu ake da sunan natibe authorities, sun yi aiki tare a lokacin da masu saukin kai wadanda kuma su Turawan suke ma, kallon barazana ce sun raba su da mulkin tafiyar da al’ummarsu.

    Kafawa

    Majalaisar Sarakuna daga karshe an kafa ta ne a shekarar 1951,a karkashin tsarin mulkin Macpherson, wanda shi matufar tsarin mulkin ita ce a karawa Nijeriya kasancewa cikin tafiyar da gwamnati, yayin da shi kuma lamarin da ya shafi Sarakunan ko masarautun gargajiya aka shigar da su cikin lamarin siyasa.An kafa majalisar Sarakuna a sassa uku na Nijeriya wadanda suka hada da sashen Arewaci, Yammaci, da kuma Gabashi.Daga baya kuma an maye wancan da majalisar Sarkuna.

    Watan Mayu 1956,aka gabatar da kudurin niyyar yin doka a majalisar Kudu maso gabashin Nijeriya, suka gabatar da kudurin zai bada dama ta a amince da Sarakunan gargajiya, wanda ta haka ne aka samu damar kafa majalisar Sarakunan Kudu maso gabashin Nijeriya, duk kuwa a lokacin da akwai turjiyar da aka samu daga masu fafutukar tafiyar da lamurra yadda suka dace, saboda sun ki goyon bayan a sa su masu Sarautun gargajiya a harkokin yadda ake tafiyar da gwamnati.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • An kama direban mota da jabun kuɗin N1m a Oyo

    [ad_1]



    Rundunar ’Yan Sandan Jihar Oyo, ta kama wani direban mota ɗauke da jabun kuɗi har Naira miliyan ɗaya.

    Kakakin rundunar, CSP Adewale Osifeso ne, ya bayyana hakan a ranar Asabar cewa jami’an sintiri na Gwamnatin Tarayya ne suka tsayar da direban a kusa da gidan Guru Maharaji, kan babbar hanyar Legas zuwa Ibadan.

    Direban mai suna Akande, ya fito daga Legas ne, kuma yana kan hanyarsa ta zuwa Osogbo, babban birnin Jihar Osun, kafin shiga hannu a ranar Juma’a.

    A cewar Osifeso, lokacin da aka tsayar da motar, direban ya fara rawar jiki abin da ya sa jami’an suka binciki motarsa, inda suka gano kuɗin a cikin wata leda.

    Mota da yake tafiya da ita ƙirar Toyota Sienna ce mai lambar FKJ 443 YG.

    Akande, ya amsa cewa wani mutum ne ya ba shi kayan a garejin Ojota, Legas, inda aka ce man shafawa ne da za a kai Osogbo.

    Amma da aka bincika, aka gano duk jabun sabbin kuɗaɗe ne masu lambobi 235923, 235922, da 235921.


    [ad_2]

    Source link

  • Sin Da AU Sun Sabunta Hadin Gwiwa Game Da Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani Wajen Raya Noma A Afirka

    [ad_1]

    Kasar Sin da hukumar gudanarwar kungiyar tarayyar Afirka ta AU, sun sake sabunta hadin gwiwarsu, game da bunkasa amfani da fasahohin zamani wajen raya noma, da tsarin samar da abinci mai jure kalubale a sassan nahiyar Afirka.

    Da yake tabbatar da hakan a jiya Jumma’a, cikin jawabinsa a taron masu ruwa da tsaki, wanda aka yiwa lakabi da “Haduwar Sin da Afirka”, wanda kuma ya gudana a cibiyar birni ta gwajin fasahohin noma dake birnin Addis Ababa, fadar mulkin kasar Habasha, shugaban tawagar Sin a AU Jiang Feng, ya ce hadin gwiwa a fannin raya noma muhimmin bangare ne na cimma moriyar juna tsakanin Sin da kasashen Afirka.

    Ya kuma bayyana cewa, Sin ta kaddamar da cibiyoyin gwajin dabarun bunkasa noma sama da 20, da ingiza cin gajiyar fasahohin zamani na habaka noma sama da 300 a sassan Afirka, matakin da ya amfani kananan manoma sama da miliyan guda.

    A nata tsokaci, kwararriya a fannin raya noma, da tabbatar da samar da isasshen abinci a hukumar gudanarwar AU, Patience Mhuriro-Mashapa, ta jinjinawa kwazon kasar Sin na wanzar da hadin kai tare da Afirka, musamman karkashin shirye-shirye da dama na bunkasa sanin makamar aiki.

    Ta ce taimakon kasar Sin ga kasashen Afirka, a fannin ingiza zamanantar da harkar noman zamani, ya yi matukar karfafa kwarewar aiki, da bunkasa kwazon cibiyoyi masu nasaba da hakan, kana ya samar da wata babbar kafa ta musayar ilimi a fannin ayyukan gona. (Saminu Alhassan)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Mutum 13 sun rasu yayin tsere wa ’yan bindiga a Zamfara

    [ad_1]



    Aƙalla mutum 13 ne suka rasu, yayin da sama da 20 suka ɓace a Jihar Zamfara, bayan jirgin ruwan da suka hau domin tsere wa ’yan bindiga ya nutse.

    Mazauna yankin da wasu jami’ai sun tabbatar da aukuwar lamarin a ranar Asabar.

    Harin ya faru ne a ranar Juma’a a yankin Birnin Magaji, inda ’yan bindiga suka kai wa ƙauyuka biyu hari.

    Mutane da dama ne suka tsere zuwa bakin kogi, inda suka riski jirgin ruwa guda ɗaya kacal.

    Hakan ya sa aka jirgin da mutane sosai, lamarin da ya sa ya nutse a cikin ruwa.

    “Babban yayana da ’ya’yan yayata biyu suna cikin waɗanda suka rasu,” in ji Shehu Mohammed, wani ma’aikacin lafiya a Birnin Magaji.

    Sarkin yankin, Maidamma Dankilo, ya tabbatar da rasuwar mutum 13.

    Amma ya ce an ceto mutum 22, sauran 22 kuma har yanzu ba a gan su ba.

    Zamfara ta daɗe tana fama da hare-haren ’yan bindiga.

    A makon da ya gabata, ’yan bindiga sun kashe mutum biyu tare da sace sama da 100 a wani hari da suka kai kimanin kilomita 150 daga Birnin Magaji.

    Rahotanni sun nuna cewar Jihar Zamfara ta fuskanci hare-haren ’yan bindiga sama da 50 tsakanin Yulin 2024 zuwa Yunin 2025, inda aka sace mutane sama da 1,000.


    [ad_2]

    Source link

  • Yadda Jariri Ke Koyon Tsotsar Nonon Uwa Kafin Haihuwa

    [ad_1]

    Babu shakka, Allah gwani ne cikin aikinsa da kuma mulkinsa. Yau za mu yi nazari a kan yadda Allah ya shirya jariri, domin sanin yadda zai iya tsotsar nonon mahaifiyarsa, ba tare da wani ya koya masa ba.

    Bisa al’ada, tsotsar nonon uwa, aiki ne na musamman da yake bukatar a koya wa mutum, domin ya iya. Amma saboda Allah ya san ba zai yiwu a iya koya wa jariri wannan aiki na tsotsar nonon mahaifiyarsa ba, cikin rahamarsa da ikonsa; sai ya hutar da mu.

    Tun jariri yana cikin uwa, tsakanin mako na 13 zuwa mako na 26, Ubangiji yake fara shirya jariri ta hanyar kimsa masa ilhamar tsotsar nonon mahaifiyarsa.

    Har ila yau, wannan ilhama ta tsotsar nonon uwa da ake haifar jarirai da ita, ana kiranta da ‘Sucking refled’, a turancin likita. Kazalika, ilhamar tana fara aiki ne gadan-gadan bayan haihuwa a duk lokacin da kan nonon uwa ya taba saman bakin jariri, wato hanka kenan.

    Haka abin yake, idan aka sa wani abu makamancin kan nono; kamar kan yatsa ko kuma fasfaya (pacifier), haka za su rika tsotsa babu ji babu gani, saboda haka aka shirya wa kwakwalwarsu cewa; da zarar kan nono ya dunguri hanka, sai su kama tsotsa kai tsaye.

    Don haka, su ma ba aikin kansu ba ne, haka kawai za su ji suna yi ba tare da wani kokari nasu ba, abu ne shiryayye da Allah SWT.

    Saboda haka, wannan ilhama ta tsotsar nono; tana daukewa a tsakanin watanni sha biyu (12), lokacin da ake shirye-shiryen yaye yaro daga shayarwa.

    Har wa yau, bayan ilhamar tsotsa da ake kira a turance ‘Sucking refled’, akwai kuma wata ilhamar da ake kira da ‘Rooting refled’, ita kuma wannan ilhamar tana taimaka wa jarirai, su iya lalubo kan nonon mahaifiyarsu, ko da kuwa idonsu a rufe yake ko kuma a cikin duhu.

    Bugu da kari, akwai kuma ilhamar hadiya, wato ‘Swallowing reflex’, bayan an tsotsi nonon; ana kuma bukatar a hadiye shi.

    Don haka, ta kan wadannan ilhamomi guda uku ne da Ubangiji ya yi wa jarirai suke iya lalubo nonon mahaifiyarsu, sannan su tsotsa; har kuma su hadiye ba tare da wani mahaluki ya koya musu ba.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Sin Da Amurka Sun Yi Musayar Ra’ayoyi Game Da Batutuwan Cinikayya

    [ad_1]

    Wakilin kasar Sin a fannin cinikayyar kasa da kasa, wanda kuma shi ne mataimakin ministan cinikayya na kasar, Li Chenggang, ya yi musayar ra’ayoyi da jami’an gwamnatin Amurka, dangane da alakar tattalin arziki da cinikayya dake tsakanin sassan biyu.

    Li, ya jagoranci tawagar kasar Sin yayin zantawa da jami’an ofishin baitulmalin Amurka, da na ma’aikatar cinikayya, da na ofishin wakilin cinikayyar kasar, tsakanin ranakun Laraba da jiya Jumma’a a birnin Washington.

    Wata sanarwa da ma’aikatar cinikayyar Sin ta fitar bayan ganawar, ta ce sassan biyu sun yi musayar ra’ayoyi dangane da yadda za a aiwatar da kudurorin da shugabannin kasashen biyu suka cimma, yayin zantawarsu ta wayar tarho a ranar biyar ga watan Yunin bana, da ingiza alakar tattalin arziki da cinikayya tsakaninsu, da kuma bibiyar sauran batutuwan da kasashen biyu suka tattauna, dangane da raya hada-hadar cinikayya tsakaninsu.

    Bugu da kari, Li ya jaddada cewa, wajibi ne Sin da Amurka su nacewa ka’idojin mutunta juna, da wanzar da zaman lafiya, da hadin gwiwar cimma moriya tare. Ya ce ya kamata kasashen biyu su yi amfani da salon gudanar da shawarwarin raya tattalin arziki da cinikayyarsu, wajen warware sabani ta hanyar tattaunawa, da tuntubar juna kafada da kafada, su kuma fadada hadin gwiwa, da yin aiki tare don inganta kyakkyawar alakar tattalin arziki da cinikayya mai daidaito da dorewa. (Saminu Alhassan)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • NTIC Ta Jinjina Wa Gwamna Buni Kan Taimako A Bangaren Ilimi

    [ad_1]

    Kwalejin Tulip Nijeriya ta kasa da kasa Yobe (NTIC) ta nuna jin dadinta dangane da gudunmawar da mai girma Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, saboda irin maida hankalinsa da yayi kan lamarin daya shafi ilimin yara manyan gobe.

    Har ila yau makarantar tayi bikin murnar hazikan dalibanta, wadanda suka ci gaba da samun nasara a lamarin da ya shafi ilimi da kuma wasu abubuwan da suka sha bamban da shi a cikin gida da kuma waje.

    Manajan darekta na NTIC, Dakta. Feyzullah Bilgin, yace nasarorin da aka samu sun hada da jarabawar shiga manyan makarantu ta kasa (JAMB) da sauran jarabawar daban- daban na kasa, sai kuma nasarorin da aka samu a duniya.

    Ya kara da cewa daliban Kwalejin NITIC ta Yobe wani babban lamari ne da yasa ayi takama da su saboda kuwa sannu a hankali sai nasarori suke kara samu wajen wakiltar Jihar Yobe da kuma Nijeriya.

    Nasarorin da ba’a dade da samun su ba sun hada da, matsayi na farko a jarabawar Lissafi da aka yi ta kasai da kuma Olympiad inda aka samu nambar gwal a gasar harshe ta duniya.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Ra’ayoyin Jama’a Daga Kuri’ar CGTN Sun Jinjinawa Gudummawar Sin A Fannin Raya Kungiyar SCO

    [ad_1]

    A gobe Lahadi 31 ga watan Agustan nan ne kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai ko SCO, za ta gudanar da babban taro mafi girma tun kafuwarta. A matsayinta na kungiyar hadin gwiwa ta shiyya mafi yawan jama’a da fadin yankuna, SCO na gaggauta kara zama muhimmin jigo na inganta jagorancin duniya, inda take amfani da fifikon goyon baya, da hadin gwiwa a matsayin muhimman ginshikan shawo kan tarin kalubalen hadurra da matsaloli.

    A matsayinta na wadda ta kafa kungiyar, har kullum kasar Sin na ci gaba da samar da gudummawar jagoranci, da ingiza ci gabanta. Sakamakon wani binciken jin ra’ayin jama’a ya tabbatar da hakan, inda kaso 91.4 bida dari na masu bayyana ra’ayoyi daga kasashe membobin SCOn suka amince da gudummawar da Sin ke bayarwa, wajen cimma nasarorin dandalin, ta fuskar yayata matakai na zahiri na bunkasa hadin gwiwar membobinta, musamman ta fuskar kare tsaron yankinsu, da ingiza ci gaban tattalin arziki.

    Tun kafuwar SCO, kungiyar ta wanzar da “Ruhin Shanghai” na mutunta juna, da cimma moriyar bai daya, da samar da daidaito, da tuntubar juna, da martaba mabambantan wayewar kai, da neman damar ci gaban bai daya.

    Ra’ayoyin jama’a daga kuri’ar da kafar CGTN ta gabatar, sun shaida yadda kaso 86.8 bisa dari na masu bayyana mahangarsu suka amince da cewa, ‘Ruhin Shanghai’ ya samar da sabon salo, mara amfani da danniya da fito-na-fito, wajen aiwatar da jagorancin yanki a wannan duniya mai mabanbantan sassa masu tasiri. A daya bangaren kuma, kaso 81.8 bisa dari na ganin ‘Ruhin Shanghai’ na karfafa muryar kasashe masu tasowa, da samar da gudummawar gudanar da tsarin duniya madaidaici kuma mai adalci

    Binciken jin ra’ayin jama’ar wanda kafar CGTN ta kasar Sin, da jami’ar Renmin ta kasar suka gudanar, karkashin cibiyar tattauna harkokin kasa da kasa a sabon zamani, ya tattaro ra’ayoyin mutane 8,873 daga kasashen duniya 38. Ya kuma hado da ra’ayoyin al’ummun manyan kasashen duniya masu ci gaba, da ma na kasashe masu tasowa. Dukkanin masu bayyana ra’ayoyin na tsakanin shekarun haihuwa 18 ne zuwa sama, an kuma lura da yanayin kason kidayar al’ummun kasashen da kuma jinsinsu wajen tattaro ra’ayoyin. (Saminu Alhassan)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta

    [ad_1]

    Shugaban hukumar ilimin bai daya ta Jihar Bauchi (SUBEB), Alhaji Adamu Mohammed, ya yi kira da al’umma/ iyayen yara da cewa su dauki lamarin sa ’ya’yansu wani babban abu ne da yakamata su bashi matukar muhimmanci.

    Shugaban ya yi wannan kiran ne a taron kwana daya da yake da muhimmanci saboda ya shafi lamarin amfani ne da tsarin mai suna Teaching at the Right Lebel (TaRL) (ko kuma koyarwa ta hanyar da ta dace, wanda aka yi a Bauchi.

    Alhaji Mohammed ya nuan rashin jin dadinsa a wasu kura- kuran da ake yi na al’amarin koyarwa, inda yace wasu Malaman basu cancanci su koyar da masu koyo ba ta kowane mataki na koyon ilimi.

    Ya yi kira da hukumar ta bada agajin gaggawa na lamuran kananan yara,ta UNICEF- TaRL ta kara fadada ayyukan nata domin ta samu cimma burinta kwarai da gaske .

    Ita a na ta jawabin, babbar wakiliyar UNICEF’ofishin Jihar Bauchi , Bauchi, Mrs Nuzat Rafik,ta bayyana shi tsarin na TaRL,a matsayin daya daga cikin dabarar samar da ilimi a duniya.

    Shi yasa ta ce duk kowa daga ciki al’umma yana da irin gudunmawar da zai bada wajen tabbatar da cewa kowane yaro ya samu damar da zai tafi makaranta, ta kuma kara jaddada tsarin nastressing TaRL yana bada dama ga Jihohi su samu kira da sa duk masu ruwa da tsaki.

    A tasu gabatarwar ta hadin gwiwa, Dakta Goni Shetima,wanda shi horarwa ne ta bangaren tsarin TaRL,da Malam Abdulrahman Ibrahim Ado, kwararre jami’in ilimi na UNICEF, sun bayyana cewa tsarin an fara gudanar da shi a karamar hukumar Alkaleri.

    Kamar yadda suka ce, an fara tsarin ne da makarantu 190, ‘yan makaranta 10,865, sai kuma Malaman makarantar gwamnati 290.

    Shi ma darektan shiyya na hukumar (UBEC), wanda Abdulsalam Abubakar ya wakilta,ya bayyana irin jajircewar hukumar kan aiki tare da masu ruwa da tsaki, domin a samu bunkasa ilimi a fadin Jihar.

    A nasu sa albarkar Shugaban kwamitin ilimi na majalisar Jihar, Honorabul Nasiru Ahmed Ala, darekta a SUBEB, Zuhairu Usman, da kuma darekata ingancin lamura SUBEB, Abbas Abdulmumini, sun yi kira da adauki tsauraran matakai wajen daukar Malaman makaranta, a daidai lokacin da gwamnatin Jihar ta ke shirin daukar Malaman makaranta.

    A na shi fatan alkhairin Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Suleiman Adamu, wanda Danejin Bauchi, Alhaji Lawal Babamaji ya wakilta,ya bayyana Sarakunan gargajiya shirye suke wajen bunkasa ilimi a Jihar.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Jigon jam’iyyar PDP a Gombe, Haruna Jonga, ya koma APC

    [ad_1]



    Tsohon babban jami’in hukumar tsaro ta Marshall a Jihar Gombe, Alhaji Haruna Jonga, ya fice daga jam’iyyar PDP inda ya koma APC.

    An yi bikin karɓarsa a ofishin jam’iyyar APC na ƙaramar hukumar Gombe.

    Shugaban ALGON na jihar, Barista Sani Ahmad Haruna, ya ce wannan sauya sheƙa na Jonga alama ce cewa jama’a suna yaba wa ayyukan Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya.

    Shugaban APC na ƙaramar hukumar Gombe, Alhaji Abubakar Danladi, ya ce Jonga babban mutum ne da zai ƙara wa jam’iyyar ƙarfi, musamman kafin zaɓen 2027.

    Da yake jawabi, Jonga, ya bayyana cewa ayyukan raya ƙasa na Gwamna Inuwa ne suka ja hankalinsa, don haka duk mai kishin jihar Gombe ya kamata ya goyi bayan gwamnan.


    [ad_2]

    Source link