Shugaban ƙasar China, Xi Jinping, na karɓar baƙuncin taron ƙungiyar Shanghai Cooperation Organisation (SCO) a birnin Tianjin, inda shugabannin ƙasashe kusan 20 daga yankin Eurasia suke halarta.
Taron, wanda zai gudana har zuwa Litinin, ana kallon sa a matsayin wani babban dandalin da ke ƙara tabbatar da matsayin China a tsakiyar harkokin siyasar ƙasashen Eurasia.
Shugaban Rasha, Vladimir Putin, ya isa Tianjin da manyan jami’an gwamnati da ’yan kasuwa daga ƙasarsa, inda kuma ya yi shirin gudanar da tattaunawa da shugabannin ƙasashe daban-daban a gefen taron.
Firayim Ministan Indiya, Narendra Modi, shi ma yana halartar taron, wanda ya kai ziyara ta farko zuwa China tun shekarar 2018.
Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafin X, Modi ya ce: “Indiya za ta ci gaba da gina dangantaka da China bisa amincewa, mutuntawa da kuma fahimtar juna.”
Ya ƙara da cewa haɗin kan ƙasashen biyu zai amfanar da al’ummominsu da suka haura biliyan 2.8, tare da samar da ci gaba ga bil’adama gaba ɗaya.
Rahotanni sun nuna cewa tsohon rikicin iyaka tsakanin ƙasashen biyu da ya haddasa mutuwar sojoji a 2020, ya fara lafawa tun daga bara lokacin da shugabannin suka haɗu a wani taro a Rasha.
Daga cikin manyan shugabannin da suka halarci taron akwai shugaban ƙasar Belarus, Alexander Lukashenko, shugaban Iran, Masoud Pezeshkian, da kuma shugaban Turkiyya, Recep Tayyip Erdogan, lamarin da ya sanya taron na bana zama mafi girma tun kafa ƙungiyar a 2001.
Masana sun bayyana cewa China da Rasha na amfani da SCO a matsayin wata hanya ta ƙarfafa tasirinsu a duniya a matsayin kishiyoyin ƙungiyoyin Yamma kamar NATO, musamman ganin yadda rikicin Ukraine da batun Taiwan ke jawo saɓani tsakaninsu da Turai da Amurka.
Bincike ya kuma nuna cewa Rasha na fatan amfani da SCO wajen samun goyon bayan ƙasashe masu tasowa, tare da ƙara kusantar Indiya a lokacin da take samun saɓani da Amurka kan batun shigo da mai daga Rasha.
Taron na Tianjin ya zo ne ’yan kwanaki kafin bikin gagarumin faretin soji da za a gudanar a birnin Beijing ranar Laraba, wanda zai ja hankalin shugabanni da dama daga sassa daban-daban na duniya, ciki har da Shugaban Koriya ta Arewa, Kim Jong Un.
Shin hakan yana nufin akwai matsala ne tattare da hakan ko babu?
Mafi yawan mata suna samun fitowar farin ruwa a gabansu a cikin tsakiya watansu.
Akalla mata da yawa suna ganin farin ruwa mai kauri ko salala, mara launi yana fito musu a kowace rana, adadin da ya kai kimanin cikin cokalin shayi. Launin ruwan yana iya sauyawa daga farin madara, zuwa farin ruwa, ko kuma baki baki (kalar kasa kasa).
Banbancin launin ruwan ko kaurin sa yana ta allaka ne da canjin na jikin ta a lokacin da yake fitowa.
Wannan fitan farin ruwa da mace take gani ta gaban ta kafin al’adarta ba matsala bace, babu matsala tattare da hakan. In dai babu warin ko karni ko kuma kaikayi. Wani lokacin yana iya kasancewa yalo.
Hakan yana faruwa ne saboda yawan hormones “progesterone” da yake taruwa a jikinta. A wannan gaban ana kiran yanayin da “luteal phase”.
Shin wasu lokuta ne za ki tsammaci ganin farin ruwa a gabanki; Idan kin gani ba damuwa bane
Yawanci mata suna iya samun bushewar gaba kamar na kwana 3 zuwa 4 kowane bayan yankewar al’adarsu. bayan wannan kwanakin, farin ruwa mai danko ya kan sake bullowa wanda zai yi kamar kwana 4 zuwa 5 kafin lokacin fitar kwayar alitta, alama ce ta kwayar alitta sun fara girma, ana kiransa da “follicular phase” that means a lokacin ne “eggs” (for obulation) suke kokarin girma.
Idan kuma lokacin fitar ya yi, ruwan sai ya canza daga mai danko zuwa fari mai yauki kuma mara kauri (salala) haka. A wannan lokacin yana kara yawa sosai fiye da na kullum a da. Shi kuma ana kiran shi “farin kwai”.
Aikinsa shi ne ya taimaka wajen santsi domin ya samu daman isowa kwai da yake jiransa don fitowa.
Sannan mata da yawa suna amfani da ganin wannan ruwan a matsayin alama ta obulation dinsu, hakan yana taimaka musu wajen samun ciki da wuri ko kuma kaura cewa yin cikin. Wannan matakan shi ake kira da ” sadidan na tazarar haihuwa
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shafi ne da ya saba zakulo muku fitattun Jarumai, manyan da kanana, har ma da mawaka, daga cikin masana’antar shirya finafinan Hausa ta Kannywood. Kamar kowane mako yau ma shafin na tafe da wata fitacciyar jarumar, da ta shafe tsahon shekaru a cikin masana’antar Kannywood, wato HAUWA GARBA wacce aka fi sani da SABURA Gidan Badamasi. Inda ta bayyanawa masu karatu wasu matsaloli da ke cikin masana’antar Kannywood, tare da irin kalubalen da suke fuskanta wajen masu kallo, har ma da wasu bayanan masu yawa da suka shafi sana’arta ta fim.
Ga dai tattaunawar tare da wakiliyar jaridar LEADERSHIP HAUSA RABI’AT SIDI BALA Kamar haka:
Da farko masu karatu za su so su ji cikakken sunanki, tare da sunan da aka fi saninki da shi.
Sunana Hauwa Garba, wacce aka fi sani da ‘Yar’Auta ko Sabura ta gidan Badamasi.
Ko za ki fadawa masu karatu dan takaitaccen tarihinki?
An haife ni a garin Kano a Bichi LGA, na yi firamare a Bichi ‘Chiranci Primary School’. Amma ban cigaba ba da yake mu fulani ne, daga nan aka yi min aure. Bayan na fita daga gidan mijina, sai na fara koyan wasan dabe (Drama), daga nan ne dai na samu kaina a cikin wannan sana’ar.
Me ya ja hankalinki har ki ka tsunduma harkar fim?
Abin da ya ja hankalina har na fara fim, bayan na yi aure na auri dan fim, Allah ya ji kanshi Rabilu Musa (Ibro). Bayan na fita daga hannunsa kawai sai na yi sha’awar ni ma na fara fim. To, akwai wacce nake so a ‘yan fim Fati Muhd, lokacin ni masoyiyarta ce, ina son aktin dinta. Daga nan ne na tsunduma na samu Baba Ari, da Musa Maisana’a, da Dan’Auta, da marigayi Cinnaka, sune suka jajirce akan na je na yi fim. Saboda muna zuwa wasan dabe, suka ce ya dace na shiga fim kowa ma ya san da ni.
Bayan fitowa matsayin jaruma, ko akwai wani bangare da ki ke taka rawa a cikin masana’antar?
Gaskiya ni jaruma ce kawai, ba na daukar nauyi ko shiryawa ko makamantan haka, ni dai kawai jaruma ce.
Ya gwagwarmayar farawar ta kasance?
Lokacin da na fara fim, gaskiya ban samu wani matsaloli ba. Saboda ni ba a budurwa ta na fara fim ba, daman wacce take fara fim a budurwar ta, ita ce ke samun matsala. Ni na fara fim bayan na fita daga gidan mijina, kuma wanda na aura dan fim ne, saboda haka dan na shiga fim ba zan samu wani gwagwarmaya ba. Inda zan samu, da a wajensa zan samu a rika cewa ai dan fim za ta aura. Amma kowa jin dadi yake ma zan auri dan fim, wajen ‘yan’uwa da dangi dukka ban samu matsala ba. Kuma ban je wajen wani furodusa ko darakta ba, imu-imu su Dan’auta da Baba Ari muka hada muka yi finafinan mu. Akwai Aminu Dagash, akwai darakta K-Eza su ne suka yi min finafinai biyu, mu ma muka hada group din mu, muka yi finafinai biyu. Dan haka ban sha wata wahala ba.
Kin yi finafinai sun kai kamar guda nawa?
Gaskiya ba zan iya tantance adadin finafinan da na fito ciki ba, na dai yi finafinai da yawa, amma ba zan iya tantance guda nawa nayi ba.
Wacce rawa ki ka fi yawan takawa a masana’antar Kannywood?
Rawar da na fi yawan takawa ita ce; rawar ‘Yar’Auta, shagwababba, kuma kamar irin doluwa, gabuwa, irin bazar-bazar din nan, duk dai irin haka.To, ko uwa na fito bana yin kyau, sai dai in uwar ita ma bazar-niya ce. Amma indai ba haka ba, ba na yin kyau. Ana iya saka ni a ‘yar aikin gida, ko ‘yar gida, amma ga ni ga yadda nake shawaragi-shawaragi.
Ya ki ka tsinci kanki a cikin shirin Gidan Badamasi?
Na tsinci kaina a jaruma, tunda jarumar ce daman, shi ya sa na tsinci kaina a jaruma. Saboda ni abin da nake gani a rayuwa, duk abin da ka ga ka yi sana’arka ce kuma aikinka ne.
Wane waje ne ya fi baki wahala a cikin shirin gidan badamasi?
Wajen da ya ban wahala kwarai akwai, wajen kuwa shi ne, inda nake zuwa nake marin Azima ta yi shigar buzaye ta saka nikab. Duk ‘yan gidan na tsoro, ni kuma ban san wace ce ba na dauka irin buzayen nan ne, ta ki kuma magana kuma gashi da daddare. Na yi ta magana taki magana ni kuma na kwada mata mari, tana bude fuska har zuciyata na ji ba dadi. Dan kafin ma a yi abun, an gwada an gwada na ki, sai da Baba Falalu ya ce “Ke ba fa gaskiya bane, ki daure ki abun nan ‘normal”, sannan na yi.
Bayan Jaruma Fati Muhd da ki ka ce tana burge ki kafin ki fara fim, ko akwai wasu Jaruman da suke burge ki a wancen lokacin?
Bayan Fati Muhammad da take burge ni a mata, dan saboda ita ne ma na kirkiro wannan ‘makeup’ din da nake yi wa kaina. Sai kuma a maza S.Nuhu, muna son shi, dan ba ni kadai ba ma muna son shi. Allah ya ji kansa ya gafarta musu, irin su; Hauwa Ali Dodo, akwai wata babbar jarumata ita tana nan Hindatu Bashir, Allah ya kara mata lafiya.
Me ya ja hankalinki har ki ka kirkiri kwalliyar fuska saboda Fati Muhammad?
Ni masoyiyar Fati Muhammad ce, kuma ta taba zuwa Abuja ana wasa, mu kuma lokacin mun je biki a lokacin aka ce mana Fati Muhd za ta yi wasa. Duk ‘yan matan unguwarmu da muka je bikin da su muka ce mu je mu gani. Muka hada kudi muka bayar da kudin ‘gate’ muka shiga muka zauna, har muna dan tsoro daga can sai ga ta, ta shigo ita da Lawan Ahmad. Wajen ya cika sosai, tana shigowa muka ce indai aka tashi sai mun yi mata magana, ana gamawa muka fita waje muna jiranta. Wajen ya cika makil ta fito ana kakkarewa ta shiga mota, duk da cewa akwai ‘yan sanda a wajen, amma mutane sai kai hannu ake ana shafa motar. Motar da ta shiga kowa yake tabawa yana shafawa a jikinsa ana ta Fati Muhd, ni kaina sai da na kai hannu na shafo motar na shafa a jikina. Tun daga wannan lokacin na ce, in Allah ya yi maka daukaka in ba kada masu bin bayanka za ka samu matsala. Daga nan sai na ga a gwababba zan fito, tana iya yuwa ka yi kwalliya irin ta yara ka damalmale fuska, kawai sai na dauko wannan kwalliyar na damalmale fuska. Sai ga shi ina yin aiki da ita, Allah ya sa ‘yan kallo da masu kaunar aikinmu suka kaunata.
Ko akwai wani fim da ki ka taba fitowa ba tare da kwalliyar fuskar da ki ke yi ba?
Gaskiya ban taba fitowa fim din da ba wannan kwalliyar ba. Saboda ni kaina bana so na fito a fim din da ba wannan kwalliyar. Ba wai bana so bane, ina so amma in na fito ba zan yi kyau ba, tunanin da nake yi kenan. Ba zan yi kyau ba, kuma ba zan bayar da abin da ake so ba, idan na yi kwalliyar tana kara zaburar da ni ga abin da zan yi. Amma dai zan gwada watarana na yi fim ba wannan kwalliyar, na gani ko zai yu.
Ya za ki bambantawa masu karatu, bambancin finafinan baya da na yanzu?
Bambancin shi ne; yanzu an samu cigaba sosai, wajen kyamera, wajen samu, ‘location’ din ma gaskiya an samu abubuwa masu kyau. Kawai abin da dai muka rasa saka kaya, kayan ‘da’ a rufe suke duk jikinka kuma sun yi maka yawa, ba lallai ne a ga surarka ba. Na yanzu kuma a matse suke, shi ne kawai matsalar mu a yanzu. Allah ubangiji ya shirya ya gyara mana.
Wane irin nasarori ki ka samu game da fim?
To, Alhamdulillahi na samu nasarori kala-kala, tunda a cikin fim din nan, ‘da’ ba ni da gida kuma na dawo ina da gida ko na ce gidaje ma, har na dawo ban taba tunanin zan hau mota ba, na hau mota tawa ta kaina. Sannan kuma duk irin masu kudi haka ko ‘yan siyasa, ‘yan majalisa matansu za su ce a kai mu. Ana kai mu wasu ma za a ga kyauta ne kawai za ka samu, wacce za ka gigice. Saboda jin dadi wannan ma nasara ce. Sannan nasara ta biyu duk inda ka je an sanka, wannan ita ce babbar nasara. Daga kauye har birni ba wanda bai sanni ba, ai kuwa shi ne babbar nasara. Suna da yawa in na ce zan zauna nai ta fada, za mu iya gama wannan hirar ba tare da na gama fadar su ba.
Ko akwai wani kalubale da ki ka taba fuskanta game da fim, tun daga farkon farawarki zuwa yanzu?
Ni wallahi idan na ce ga kalubale da na fuskanta game da fim gaskiya babu shi, in ba wannan kalubale na gabadayan mu ba, kamar yadda ake yi mana kallo, ana yi mana kudin goro, da tsohuwa da yarinya, in ma jaririya ce, ke ki ka zo Kannywood. Ki ka zo kina masana’antar nan cewa za a yi ke karuwace, wannan kalmar duk ita ta fi min ciwo. Wallahi idan za ka kwana kana zagina kana tsine min wallahi ko a jiki na, saboda na san ni ba tsinanniyar ba ce. Sannan in za ka kwana kana ce min karuwa ni ba ta damen ba, saboda ba ita ba ce. Amma da ake mana kudin goro gabadayan mu, har cewa ake yi dan fim ba shi da addini, innalillahi wa’inna ilaihirraji’un. Ga ilimin addini a kawunan mu, sallar nan guda biyar ba ta wuce mu, ga tauhidi Allah ya ba mu, sannan ka ce dan fim ba shi da addini. Yanzu duk masu fadar hakan idan ka ce Allah ya isa, Allah fa zai isar maka. Ni ban da wannan ba abin da ya riske ni, lafiya lau nake cikin masana’antar.
Za mu ci gaba a mako mai zuwa insha Allah
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shafin TASKIRA shafi ne da ya saba zakulo muku batutuwa daban-daban wadanda suka shafi al’umma, ciki sun hadar da; zamantakewar aure, rayuwar yau da kullum, rayuwar matasa, soyayya, da dai sauransu.
Tsokacinmu na yau zai yi duba ne game da yadda a yanzu wasu mazan suke gudun auren ‘yan boko, mata masu ilimi da wayewa. Inda shafin ya ji ta bakin wasu daga cikin mabiyan sa game da wannan batu; “Shin Ina matsalar take?, ko hakan ya dace?, Ko akwai wata shawara da ya kamata a bawa masu irin wannan tunanin?.
Ga dai bayanan nasu kamar haka:
Sunana Jamila Salisu Ibrahim Jihar Kaduna:
Gaskiya dai inda matsalar take shi ne, rashin wayewa da wasu mazan suke da shi, mafi yawa kuma mazan da suke da rashin ilimi su ke da wannan dabi’ar da take ba, dauwamammiya ba. Hakan gaskiya kwata-kwata bai dace ba, saboda an fi so namiji ya auri mai ilimi, wacce za ta tarbiyyantar da ‘ya’ya kan hanya ta gaskiya, da tarbiyya gurin rayuwa ta yau da kullum. Amma idan aka ce mace ba tada wani wayewa to, ba ita kadai za ta zauna cikin wannan rashin wayewar ba, har sai ya kai ga yaran da aka haifa suma su zama cikin duhun kai, su kasa mu’amala da al’umma. Saboda duk mutum wanda yake da rashin wayewa yana tare da tsatstsauran/baudadden ra’ayi. Shawara ta a nan ita ce su mazan su gane cewa wayewa ba yana nufin rashin tarbiyya ba ko kuma budewar ido ba, face wayewa na nufin fitowar abu daga duhu zuwa ga haske.
Sunana Abba Abubakar Yakubu daga Jos a Jihar Filato:
Maza na gudun auren mace mai zurfin wayewa da ilimi ne saboda tunanin ba za su yi biyayyar aure ba, kuma ba za su iya zaman gida yadda za su kula da aurensu yadda ake so daga mace ba. Wasu mazan na tunanin akasarin mata masu zurfin ilimi suna ganin ba za su iya mika wuya ga mazajen su kamar yadda sauran mata za su yi ba, don ko dai suna da ilimi sosai ko kuma sun fi mazajen daukaka. Babban abin da maza suka fi so a wajen mata shi ne biyayya da girmamawa. Kuma samun hakan yana da wuya a wajen matan da suke ganin sun samu wayewa ko ilimi daidai da mazajen su ko ma fiye. Wannan shi yake sa maza auren yaran mata da idanun su bai gama budewa ba, kuma ilimin su bai yi zurfi sosai ba, wadanda za su dauke su a matsayin yayu ko dai mazajen su da Allah Ya hukunta suna gaba da su, kuma aljannarsu ke karkashin kafafunsu. Domin idan aka duba yadda rayuwa yanzu ta kai wani matsayi da mata masu ra’ayin ‘feminism’ ke kara yawa suna kalubalantar tasirin maza a kansu, da kuma zargin nuna musu kasƙanci da wasu maza ke yi. Don haka yanzu maza ke shakkar auren matan da za su rika kalubalantar ikon su a kansu, ko kuma raina su a cikin gidajen su. Shawara ta a matsayina na namiji magidanci shi ne mata su rika auren mazajen da suka san za su jure zama da su, wadanda za su iya yi wa biyayya, kuma su nemi yardar Allah a tare da su. Sannan ga su mazajen ina mai yi musu nasiha da su rika tallafawa matan su yadda za su yi ilimi, har su yi aiki, watarana su taimaka musu da iyalansu. Harwayau, su daina gudun masu ilimi da wayewa daga cikin mata ‘yan boko, domin shi zaman aure fahimta ce da tarbiyya. Duk girman mace ba ta wuce zama karkashin namiji, har kuma ta yi masa biyayya, matukar ya zauna da ita cikin gaskiya da amana.
Sunana Princess Fatimah Mazadu daga Jihar Gomben Najeriya:
E! to, aure ra’ayi ne, duk da wasu na daukar auren ‘yar boko da masu Ilimi mai zurfi hatsari ne ga rayuwar su, ta fannin rashin girmamawa da ladabi, da sauransu. Gaskiya ni a nawa ba wata matsala, sai dai in shi namijin ne ke da matsala. Saboda mafi akasarin mata a gidan mazajensu suke dawo wa jan wuya, duba da irin yadda namiji ke basu kulawa da akasinsa. Dabi’u da tarbiyya na lalacewa ne lokacin da mace mai Ilimi, mai zurfi ta ga mijinta na kauce hanya, ko yana kin biya mata bukatun gida. Ta kan nuna masa itama da gaske ta yi bokon duk inda yaso juya ta sai ta bankare, saboda tana da sani da karantar rayuwa da yadda za ta yi ta gyara shi a matsayinta na mai Ilimi. Gudun auren mai ilimi ‘yar boko wallahi gibi ne babba a gidan da namiji, saboda tarbiyya, karatu, dabi’u ana daukar ba mahaifiya ne. Ka lissafa in ka auro wacce babu ilimi sosai da kuma mara ilimi kulawar su ga yaranka da kai kanka ma ba daya bane, ni a wuri na auren mace mai ilimi ‘yar boko shi ne gaba ‘more especially’ ta kasance mai yawan ibada da tsoron Allah. To, fa! duniyar gabadaya ta zamo abun alfahri ba mijinta kadai ba. Shawarata a nan dai wallahi in ta gari ce kam ayi, saboda akwai salon rayuwa da suka sani wanda bai yi zurfi ba ba zai taba saninsu ba. Auren mai ilimi ‘yar boko da Arabic in ya hade Allah duniya ce. Allah ya sa mu dace.
Sunana Malam Abubakar Dallatu Zareku Miga A Jihar Jigawa:
Abu na farko kusan kowa ya san shi, kana tare da ita ne sai wani ya zo ya ce shi abokin karantun ta ne. Matsala a nan ita ce; ya kamata ace, bai kamata wani ya zo wajenta ba, sannan kuma wani lokacin ma suna kebewa hakan gaskiya bai dace ba. Shawarar a nan ita ce; Ya kamata a gyara wannan halayayar, domin muslunci bai yarda da hakan ba, kuma sabawa muslunci ne dole ya yi kishin iyalinsa.
Sunana Hadiza Ibrahim D. Auta. Kaura-Namoda Jihar Zamfara:
Maza da yawa ba sa son auren mace ‘yar boko mai zurfin ilimi da wayewa. A son ran wasu mazan su aure mace daga kammala Sakandare. Idan ma karatun ne ta yi a gidansu, hankalinsu ya fi kwanciya sama da a ce da karatunta suka gan ta. Saboda tunanin da wasu maza suke yi; duk macen da ta yi dogon boko za ta fi karfinsu da aurensu duka. Bugu da kari, suna zargin kamar ta watsar da darajarta ta ‘ya mace a yayin gudanar da bokon. Sannan wayewarta za ta taba musu akidar da suke son bi idan masu ra’ayin juya matansu ne ta inda suka ga dama. Sai dai inda gizon yake sakar; ba kowace mace ce take kasa ganin girman mijinta ba wai don tana da boko ko don ta waye. Sannan ba kowace mace ce boko yake tafiya da mutuncinta ba, don haka a ganina laifi ne idan aka yi musu kallo daya. Don a cikin gida daya za a iya samun kowa da kalar halinsa.
A inda matsalar take shi ne sanin kowane mata suna da rauni to, mafiya yawan matan da suka yi boko mai dan zurfi sukan sami wata kalar wayewa, musamman idan karatun addininsu ba mai zurfi bane sukan yi amfani da wannan bokon wajen kawo nakasu a zamansu na aure. Saboda gani suke yi wani abin ma wanda addini ya wajabta su yi wa mijinsu su ki yinsa, saboda wasu suna ganin sun ma fi mazan, musamman idan karatunsu ya zo daidai da namijin. Kuma idan karatun matan ya fi na mazan zurfi da dai sauransu. Ta Wani bangaren ya dace gaskiya, sabida mafiya yawan wasu auren baya karko, kin ga kuwa da ace an yi auren ba a dade ba an rabu gwara ma ba ayi ba. Shawarata a nan ita ce bai kamata ana gudun su ba, amma kafin maganar aure ta yi nisa su mazan suna bincika zurfin karatun matan na boko dana addini, sannan son samu ma idan namijin zai auri ‘yar boko sosai to, ya nemi wacce ta dan dauki lokaci tana son aure Allah bai nufa ba.
Sunana Nabeela Dikko Marubuciya daga Jihar Kebbi Garin Argungu:
A zamanin nan ana ganin wani lamari da ya ja hankalin al’umma: wasu mazan sun fara kauracewa auren mata ’yan boko masu ilimi da wayewa. Wannan batu yana da nauyin amsa, domin ‘duk inda kaho ya dosa, ba ya wuce kunne.’ Idan aka dubi lamarin da ido mai hangen nesa, za a ga cewa matsalar ba ta taso daga ilimi ba, sai dai daga fahimtar juna da tsoron da ke cikin zukatan maza. A zahiri, matsalar ta ta’allaka ne a kan fargaba da kuskuren tunani. Wasu mazan suna daukar cewa mace mai ilimi da wayewa ba za ta iya yin biyayya ba, ko kuma za ta yi musu fin karfi a gida. Wannan kuwa kuskure ne, domin ilimi shi ne fitilar rayuwa. Ilimi haske ne, duhu jahilci ne.
Sunana Muhammad Isah Zareku Miga A Jihar Jigawa:
Abu na farko shi ne ba kowa ne yake son auren mace wacce ta yi nisa a karatu ba, musamman karatun boko. Matsala a nan ita ce, mutane suna kin auren ‘yan boko ne saboda tsoron kin cikyakkiyar biyayya a zamantakewa ta aure. A gaskiya bai dace ba, suma ya kamata ana aurensu, saboda ba duk aka zama daya ba.
Sunana Khadija Auwal Koki A Jihar Kano:
Da farko dai a ganina gaskiya ra’ayi ne, domin kuwa ita mace mai ilimi cigaba ce a cikin al’umma, kuma cigaban ‘ya’yanka ce. Kuma idan ta yi ilimin kai ma za ka amfana, kuma duniya ma za ta amfana da ita. Abin da ya sa suke gudun auransu, saboda sun san me suke yi, su kuma wasu mazan sun fi san auran wacce ba ta san me take ba. E! to, gaskiya wasu daga cikin matan sukan yi wasu dabi’u na rashin da’a ko tarbiyya, wanda su kuma mazan sukan duba wannan su ga cewar ba za su iya auran su ba. Gaskiya hakan bai dace ba, domin kuwa suna amfani da wannan kalaman na cewa; wadanda suka cigaba da makaranta idonsu ya bude wajan kashewa samari masu niyyar auransu gwiwa, wajan ganin kamar za su auro wacce za ta raina su ko kuma wacce idon ta ya bude. A gani na duk wanda yake da niyyar auran macen da ta cigaba da karatu ya aura, sannan ka da ya duba magan-ganun mutane wajan ganin sun waye ko sama da haka. Sannan kuma a kara da addu’a da neman zabin Allah.
Sunana Sa’idu Abdullahi Damaturu Jihar Yobe:
Wasu mazan suna jin tsoron cewa mace mai ilimi ba za ta girmama su ba ko kuma za ta raina su. A’a, hakan bai dace ba. Ilimi bai kamata ya zama dalilin tsoro ko kiyayya ba. A karfafa maza su fahimci cewa mace mai ilimi na iya zama abokiyar rayuwa nagari. Aure nagari yana bukatar fahimta da mutunta juna ba tsoron ilimi ba.
Sunana Aisha T. Bello daga Jihar Kaduna:
Mafi yawancin maza suna ganin macen da ta yi boko ta waye kamar ba ta da nutsowa, suna ganin idonta ya bude ba za su iya auren ta ba, kuma wasu ba haka suke ba, gaskiya wasu ke bata wasu. A’a gaskiya saboda ‘yan boko mutane ne kamar mu, ina son na yi amfani da wannan damar gun janyo hankalin maza masu wannan ra’ayin na gun mata ‘yan boko in mace ta yi karatun boko za ta taimaki al’umma ne bakidaya, saboda maza masu kudun mata ‘yan boko su bari. Shawara ta a nan ita ce, maza masu gudun ‘yan boko shi ne idan ka auri ‘yar boko ko bata yi aiki ba, za ta taimake ka a gida ko gun yaranku. Ilimi shi ne gishirin zaman duniya, Allah ya bamu dacewa.
Sunana Muktari Sabo Jahun A Jihar Jigawa:
E! to, babu shakka wasu mazan suna gudun mata ‘yan boko masu ilimi da wayewa, ba don komai ba sai dan matsalolin da ake samu da wasu daga irin wadannan matan ta dalilin wayewar da suke ganin suna da ita, zamantakewar aure da su tana zuwa da matsala sosai. Kin auren nasu bai dace ba, domin duk wayewar ta in ka aure ta, za ka iya canza ta indai kai ma ka waye. Amma idan ta sami wanda bai waye ba, to fa ta sami rakumi da akala sai yadda ta yi da shi. To, masu irin wannan tunani ya kamata su duba, domin ba kowacce ‘yar boko ce take da matsala ba. Masu matsalar tun a soyayyar ku, za ka gane ko wacece ita indai kana nazartar ta.
Sunana Hassana Yahaya Iyayi (Maman Noor), Daga Jihar Kano:
Hmmm to wani lokacin ne su ‘yan boko sai a hankali amma fa ba duka ba. Gaskiya dai basu da wani matsala a nawa ganin dai. Sam bai dace ba wallahi ai shi ilimi abin so ne, wasu suke bata wasu cikin ‘yan boko, kuma ma dai ina ga masu wannan hali to, boko akida ne babu ilimin addini. To su dai nemi zabin Allah, dan wasu masu ilimin boko wallahi hmm adai yi shiru kawai. Babbar shawara a nemi zabin Allah shi ne.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
A yau Asabar, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da firaministan kasar Masar Mostafa Madbouly, a birnin tashar ruwa na Tianjin dake arewacin kasar Sin.
Yayin zantawarsu, shugaba Xi ya ce alakar Sin da Masar na cikin wani yanayi mafi kyau a tarihi, ya kuma yi kira da a yi amfani da damar bikin cika shekaru 70 da kafuwar huldar diflomasiyya tsakanin kasashen biyu a shekara mai zuwa, wajen cimma nasarar gina al’ummar Sin da Masar mai makomar bai daya a sabon zamani, da kara bayar da gudummawa don wanzar da zaman lafiya da daidaito a duniya, da bunkasa ci gaba da walwalar sassan kasa da kasa.
A dai yau din, shugaba Xi ya gana da firaministan Cambodia Hun Manet, da mukaddashin shugaban Myanmar, Min Aung Hlaing, da firaministan Nepal KP Sharma Oli, da shugaban kasar Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev, wadanda suka isa birnin Tianjin domin halartar taron koli na kungiyar hadin kai ta Shanghai wato SCO na bana.
A gobe Lahadi ne za a bude taron kolin na kungiyar SCO na shekarar bana, wanda zai gudana a birnin na Tianjin, har zuwa jibi Litinin 1 ga watan Satumba. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Gwamnonin Jihohin Arewa maso Gabas, sun koka kan matsalolin da suka shafi ayyukan jin-ƙai da kuma gina muhimman ababen more rayuwa duk da ci gaban da aka samu a yaƙin da ta’addanci a yankin.
Wannan bayani ya fito ne daga sanarwar ƙarshen taronsu karo na 12 da aka gudanar a Jalingo, Jihar Taraba.
Taron ya gudana ne ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙungiyar, Gwamnan Jihar Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum.
A yayin taron, gwamnonin sun nuna damuwa kan yiwuwar samun ambaliyar ruwa a wasu jihohin yankin.
Don haka sun buƙaci a ɗauki matakan gaggawa da kuma neman taimakon Gwamnatin Tarayya da hukumar NEDC domin gyara manyan gadojin da ruwa ya lalata.
Haka kuma, sun koka kan tsadar kayan aikin gona da suka ce na iya janyo ƙarancin amfanin gona a shekara mai zuwa.
Saboda haka, sun buƙaci a ƙara bai wa manoma tallafi da kuma bunƙasa shirin noman rani.
Bayan haka, gwamnonin sun amince da gudanar da bikin baje kolin kasuwanci na Arewa maso Gabas a Maiduguri a watan Disamban 2025, tare da haɗin gwiwar ƙungiyar NECCIMA.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA), ta raba wa mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a Ƙaramar Hukumar Potiskum ta Jihar Yobe, kayan tallafi.
Darakta Janar na hukumar, Zubaida Umar, ta amince da fara wannan tallafi a Potiskum, inda ta samu wakilcin Abdullahi Garba, ko’odinetan ofishin NEMA na Maiduguri.
A cewarta, wannan mataki ya biyo bayan ambaliyar ruwa da ta auku a ranar 15 ga qatan Agusta, 2025.
Ambaliyar ta shafi dubban jama’a kuma ta lalata gidaje da dama.
Binciken da NEMA tare da wasu ƙungiyoyin agaji suka gudanar ya nuna cewa gidaje 2,557 ne abin ya shaf, inda wasu suka rushe baki ɗaya.
Wuraren da ambaliyar ta fi shafa sun haɗa da tsohon gidan yari, Filin Mashe, Unguwar Makafi, Unguwar Jaje, Tsangaya, Rugan Fulani, da Bayan Sabon Gidan Yari.
Zubaida, ta bayyana cewa rabon kayan agaji kamar abinci, kayan masarufi, da kayan gini na nufi rage wa jama’a raɗaɗin da iftila’in da ya same su.
Ta ƙara da cewa: “Wannan mataki ya nuna cewa NEMA da abokan hulɗarta suna da niyyar taimaka wa al’umma domin rage musu raɗaɗin da ya faru.”
Hukumar ta yi rabon kayan ne tare da haɗin gwiwar Hukumar Agajin Gaggawa ta Jihar Yobe (SEMA) da kuma hukumomin tsaro a jihar.
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya ce har kullum kasar Sin za ta kasance amintacciyar abokiyar huldar MDD, kuma a shirye take ta zurfafa hadin gwiwa da majalisar, da tallafa mata, ta yadda MDDr za ta taka muhimmiyar rawar jagoranci a harkokin kasa da kasa, da hada karfi da karfe wajen sauke nauyin dake wuyanta na kare yanayin zaman lafiyar duniya, da ingiza ci gaba da walwalar dukkanin sassa.
Shugaba Xi, ya bayyana hakan ne a Asabar din nan, yayin da yake ganawa da babban magatakardar MDD Antonio Guterres, a birnin tashar ruwa na Tianjin. Ya ce tarihi ya nuna yadda cudanyar mabambantan sassa, da goyon baya da hadin gwiwa, suka kasance amsa ga tarin kalubalen dake addabar duniya.
Mista Guterres, ya isa birnin Tianjin ne domin halartar taron koli na kungiyar hadin kai ta Shanghai ko SCO na shekarar nan ta 2025. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Domin samun fata mai laushi, sumul, da haske kamar kwai.
1. Maganin kurajen da Laushin fuska
Abubuwan hadawa:
Bawon lemon tsami, bawon kwai, ruwa
Yadda ake hadawa:
Ki shanya bawon lemon tsami da na kwai su bushe, ki daka su sosai har su yi laushi. Ki kwaba da ruwa kadan, sannan ki shafa a fuskarki kafin wanka.
2. Gyaran Fuska da tumatir
Abubuwan hadawa:
Tumatir, madara
Yadda ake amfani:
Ki markada tumatir, ki zuba madara, ki kwaba. Ki shafa a fuska, ki bar shi na minti 30, sannan ki wanke da ruwan dumi.
3. Gyaran fuska da garin alkama
Abubuwan hadawa:
Garin alkama, Zuma, madara
Yadda ake amfani:
Ki hada su wuri guda, ki shafa a fuska kafin ki shiga wanka. Zai sa fata ta yi laushi sosai.
4. Laushin fata da lemo tsami
Abubuwan hadawa:
Lemon tsami, Zuma
Yadda ake amfani:
Kafin kwanciya barci, ki hada lemon da zuma ki shafa. Da safe, ki wanke da ruwan dumi, zai haskaka fata kuma ya hana kuraje.
5. Man shafawa domin Laushin jiki
Abubuwan hadawa:
Man kwakwa, man kade, man angurya, man zaitun, Almond oil, baby oil, madarar turare, cocoa butter
Yadda ake amfani:
A hada dukkan mayukan, a zuba a kwalba. Ki rika shafawa bayan wanka. Jikinki zai yi laushi, santsi da kamshi.
6. Sabulun wanka na musamman
Hade-haden sabulun:
Sabulun Zaitun, Tetmosol, sabulun salo da na gana, sabulun karas, sabulun kukumba, Kurkur (turmeric)
Yadda ake amfani:
Ki hada su su yi sabulu guda. Ki rika amfani da shi duk wanka. Zai tsabtace jiki, ya magance kuraje, ya hana duhu.
7. Hadin maganin kuraje
Abubuwan hadawa:
Zuma, ruwan khal, man zaitun
Yadda ake amfani:
A dafa su kadan a wuta, a kara ruwa, a juya sosai. Ki wanke fuskarki da sabulu, ki goge da auduga mai jika da wannan hadin. Yana kawar da kuraje da dattin fuska.
8. Steaming na fuska (Tururin Gyara Fuska)
Hadin farko:
Kwai, zuma, nono
Yadda ake amfani:
A hada a shafa a fuska, sannan a turara da ruwan zafi. Yana kashe kuraje.
Hadi na biyu:
Kindirmo (nono), man zaitun zuma
Yadda ake amfani:
A hada, a shafa a fuska, sannan a sa ruwa mai zafi a kwano, ki kara fuska a kai, ki lullube fuskar na minti 10 zuwa 15. Daga nan ki wanke da ruwan sanyi.
9. Domin hasken fata
Har zuwa 1:
Itacen sandal wood, Kurkur, madara
Har zuwa 2:
Kurkur, madara
Kwaiduwar kwai
Yadda ake amfani:
Ki shafa kafin wanka safe da yamma. Yana sa fata ta haskaka kamar zinariya.
A dora a wuta su dan yi zafi, ki kara ruwa kadan. Ki tsoma auduga ki rika goge fuska bayan kin wanke da sabulu. Yana cire duhu da tabo, ya sanya fuska ta yi fes.
Daga Sirrin Rike Miji
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
A watan Yulin shekarar 2024 da ta gabata, kasar Belarus ta shiga kungiyar hadin kai ta Shanghai ko (SCO) a hukumance. Kuma a kwanan nan, shugaban kasar Aleksandr Lukashenko, ya zanta da wakiliyar babban rukunin gidajen rediyo da talibijin na kasar Sin wato CMG a takaice, a fadar gwamnatinsa, inda ya ce shigar Belarus cikin kungiyar SCO, wani kuduri ne da aka cimma bisa tsanaki, kuma an yi shi bayan zurfin tunani, duba da rawar gani da kungiyar ke kara takawa a harkokin siyasar duniya.
Lukashenko ya kara da cewa, a yau, kungiyar SCO na kara tasirinta a duniya, kuma kasarsa ma ta kasance daya daga cikin mambobin kungiyar. Ya ce, kaso 75% na adadin cinikayyar kasarsa na fitowa ne daga cinikayyar da kasarsa ke yi da kasashe mambobin kungiyar SCO, wanda hakan babban kaso ne mai girma.
Shekarar da muke ciki, “shekarar kasar Sin” ce ga kungiyar SCO. Kuma yayin da yake tsokaci game da ayyukan da kasar Sin ke aiwatarwa a matsayinta na mai rike da shugabancin kungiyar a wannan karo, Lukashenko ya bayyana cewa, kasar Sin tamkar inji ne dake inganta ci gaban kungiyar.
A cewarsa, kasar Sin tana kokarin ba da jagoranci ta hanyar aiwatar da hakikanin ayyuka, kuma tana ba da gudummawa mai tarin yawa ga kungiyar. Ya ce wannan shekara ta Sin, wadda kuma kasar ke rike da ragamar shugabancin kungiyar, tana da muhimmanci kwarai da gaske, yana kuma fatan Sin za ta kara ba da gudunmawa ta gaske ga ci gaban kungiyar SCO, da kuma kara wa kungiyar sabon kuzarin ci gaba. (Bilkisu Xin)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe