Category: Latest News

  • Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

    [ad_1]

    Ƙungiyar masu gwanjon kayayyaki ta Nijeriya (NAA) reshen Kano ta ce gwamnatin jihar na asarar a ƙalla Naira biliyan ɗaya duk shekara saboda rashin yin gwanjon tsoffin kayayyakin gwamnati da aka cire daga ofisoshi da wuraren gyare-gyare.

    Sakataren ƙungiyar a jihar, Isah Deneji, ya bayyana hakan a wata hira da manema labarai a Kano, inda ya ce ana cire kayayyaki irin su kujeru, da na’urar sanyaya ɗaki, da interlock sakamakon sabuntawa, amma maimakon a yi gwanjonsu, ana barin wasu ma’aikata su sace su su sayar.

    Ya yi kira ga Gwamna Abba Kabir Yusuf da ya umarci Kwamishinan Kuɗi ya dawo da tsarin yin gwanjon kayayyakin gwamnati da aka ayyana a matsayin tsofaffi, domin hana ɓarna da satar da ake fama da shi a yanzu. Ya ce hakan zai taimaka wajen tabbatar da cewa kuɗin da aka samu ya shiga asusun gwamnati ba tare da salwanta ba.

    Deneji ya ƙara da cewa, akwai rahotannin da ke nuna an sace sama da na’urar sanyaya ɗaki guda 20 daga wurin gyaran gidan gwamnati. Ya kuma jaddada cewa su ƙwararru ne masu lasisi da ake sabuntawa duk shekara, amma gwamnatin jihar ta daina amfani da su.

    A nasa ɓangaren, Kwamishinan aiyuka, Marwan Ahmad, ya ce ba ma’aikatarsa ce ke kula da gwanjon kayayyakin gwamnati ba, sai dai ma’aikatar kudi. Sai dai ya yi Allah-wadai da yadda jama’a ke kwasar kayayyakin gwamnati daga wuraren da ake gudanar da gyare-gyare. Ya ce a baya-bayan nan sun kwato interlock din da aka cire wanda darajarsa ta kai sama da Naira miliyan ɗaya, wanda daga bisani aka sake amfani da shi a wani wuri na gwamnati.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa

    [ad_1]

    Daga shekarar 2021 zuwa ta 2025, kasar Sin ta sake ginawa, da gyara ko kuma fadada wasu zaurukan tunawa da tarihi guda 15, da inganta zaurukan baje kolin kayayyakin tarihi guda 68, domin tunawa da nasarar da kasar ta samu kan zaluncin Japanawa.

    Bisa irin wannan kokari, an kafa tsarin dandali na tunawa da tarihi, kamar yadda mataimakin shugaban hukumar kula da al’adun gargajiya ta kasar Sun Deli ya bayyana, a yayin wani taron manema labarai da ya gudana a yau Lahadi, kan al’amuran da suka shafi bikin cika shekaru 80 da samun nasarar yakin turjiyar jama’ar kasar Sin kan zaluncin Japan da kuma yaki da mulkin danniya a duniya.

    Sun ya kara da cewa, an tabbatar da fiye da kayayyakin al’adu da ba za a iya motsawa ba guda 10,000 da kuma wadanda za a iya motsawa guda 160,000 da suke da nasaba da yakin a duk fadin kasar Sin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Kilishiyar Waja ta tallafa wa matan gidan yari da kayayyaki a Gombe

    [ad_1]



    Kilishiyar Waja, Hajiya Rabee Abubakar Kulani, ta kai ziyara gidan gyaran hali na Gombe, inda ta raba mata fursunoni kayan tsaftar jiki domin su kula da kansu a lokacin al’ada.

    Ta ce ta kai wannan gudummawa ne domin tallafa wa mata fursunoni wajen kare mutuncinsu, ganin cewa sau da yawa ba su da damar samun irin waɗannan muhimman kayayyaki.

    “Ina so su ji kamar sauran mata, su samu tsafta da mutunci duk da yanayin da suke ciki.

    “Shi ya sa na sayi kayayyakin da kaina domin na tallafa musu,” in ji ta.

    A yayin ziyarar, ta kuma tattauna da su kan batun lafiya da haƙƙin haihuwa, tare da jaddada muhimmancin tsaftar al’ada.

    Ta samu rakiyar Hajiya Hauwa Saraki, shugabar NCWS a Gombe, da kuma Hauwa Musa Babaji, mai fafutukar kare haƙƙin mata.

    Sun yaba da yadda aka samu ci gaba wajen kula da jin daɗin fursunoni idan aka kwatanta da shekarun baya.

    Shugaban gidan gyaran hali na Gombe, DCC Victor Odafen, ya gode mata bisa wannan tallafi.

    Ya kuma yi kira ga ƙungiyoyi da mutane masu hali su yi koyi da ita wajen tallafa wa fursunoni.


    [ad_2]

    Source link

  • Jami’an Senegal Sun Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Wajen Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

    [ad_1]

    LJami’an kasar Senegal, da shugabannin siyasa, da masana, sun bayyana irin ci gaban da aka samu wajen aiwatar da sakamakon taron kolin dandalin tattaunawar hadin gwiwar Sin da Afirka (FOCAC) na birnin Beijing, a wani taron da aka gudanar a ranar Jumma’ar da ta gabata a Dakar, babban birnin kasar ta Senegal.

    Ofishin jakadancin kasar Sin da ke kasar Senegal ya karbi bakuncin taron a bikin cika shekara guda da fara aiwatar da sakamakon taron, inda ya tattaro mahalarta kusan 100 da suka hada da manyan jami’an gwamnati, da wakilan jam’iyya, da kuma kwararrun masana.

    Sakatare-janar na jam’iyyar “African Patriots of Senegal for Work, Ethics and Fraternity” da ke mulkin kasar Senegal, Ayib Daffea ya bayyana cewa, kwarewar da jam’iyyar Kwaminis ta kasar Sin ta samu wajen gudanar da harkokin mulki, ta bayar da muhimman darussa ga kasar Senegal wajen lalubo hanyar zamanantarwa da ta dace da yanayin kasar. Ya kara da cewa, jam’iyyarsa a shirye take ta zurfafa mu’amala da kasar Sin, domin kara yaukaka zumunci da hadin gwiwar da ke tsakanin kasashen biyu.

    A nata bangaren, darektar kula da yankin Asiya da Fasifik da Gabas ta Tsakiya a ma’aikatar kula da hadin kan Afirka da harkokin wajen kasar Senegal Cathy Diagne Thioye, ta bayyana dandalin FOCAC a matsayin abin koyi a bangaren hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa. Ta yi kira ga bangarorin biyu da su ci gaba da yin aiki tare don aiwatar da muhimman ayyukan da suka sa a gaba a karkashin tsarin dandalin. (Abdulrazaq Yahuza Jere)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

    [ad_1]

    Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar mazaɓar Ibadan North-West/Ibadan South-West a majalisar wakilai, Adedeji Olajide (wanda aka fi sani da Odidiomo), ya bayyana cewa zai siya wa Gwamnan Jihar Oyo, Seyi Makinde, fom ɗin takarar shugabancin kasa na jam’iyyar PDP a zaben 2027.

    Olajide, wanda ya ke ɗan PDP ne a majalisa zangon na biyu, ya ce PDP ta riga ta kintsa shugabancin ƙasa zuwa yankin Kudu, kuma a cewarsa Makinde shi ne ɗan takara mafi cancanta da zai iya tsayawa da ƙarfin siyasar Shugaba Bola Tinubu.

    A cewar Olajide, wanda shi ne shugaban kwamitin majalisar wakilai kan fasahar sadarwa da tsaro ta yanar gizo, Gwamna Makinde ya cancanci tsayawa takarar shugabanci saboda ilimi, da kwarewar siyasa,da gogewar kasuwanci, da fahimtar duniya da kuma rawar da ya taka a matsayin gwamna na wa’adi biyu. Ya ce Makinde shi ne sabon fuskar siyasar Nijeriya.

    Ya ƙara da cewa tasirin siyasar Makinde a PDP da ma ƙasa baki ɗaya ya sanya shi zama zaɓin da ya fi dacewa wajen jagorantar adawa zuwa ga nasara. Haka kuma ya bayyana salon mulkin Makinde da ya daidaita gina ababen more rayuwa da jin dadin jama’a a matsayin abin koyi ga siyasa mai ma’ana.

    Olajide ya yi kira ga Makinde da ya bayyana niyyarsa cikin gaggawa, yana mai cewa lokaci ya yi da za a samu sabon salo na jagoranci a Nijeriya. Ya yi iƙirarin cewa Makinde shi ne kaɗai babban masallacin karfi daga Kudu maso Yamma da zai iya fuskantar Tinubu a zaben 2027.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnatin Sakkwato za ta fara biyan masallatan Juma’a kuɗi duk wata

    [ad_1]



    Gwamnatin Jihar Sakkwato ta bayyana cewa za ta riƙa bai wa kowane masallacin Juma’a a jihar kuɗi daga Naira 300,000 zuwa 500,000 duk wata domin tallafa musu.

    Haka kuma gwamnatin za ta riƙa biyan limaman masallatan, na’ibansu da ladanai alawus na kowane wata domin sauƙaƙa wa hidimominsu.

    Mai magana da yawun gwamnatin, Abubakar Bawa ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa.

    Ya ce manufar shirin shi ne ƙarfafa karatun Alƙur’ani da koyar da ilimin addini ga yara da matasa a jihar.

    Gwamna Ahmed Aliyu, ya sanar da wannan mataki ne a ranar Asabar yayin yaye ɗalibai 111 da suka kammala haddar Alƙur’ani a makarantar gidauniyar Sheikh Dahiru Bauchi da ke Sakkwato.

    Ya ce alawus ɗin zai taimaka wajen ba malamai damar yin nazari da ci gaba da koyar da darusan addini.

    Gwamnan ya ƙara da cewa gwamnatinsa ta bayar da kwangilar gyara masallatai 65 na Juma’a, inda aka kammala 25, kuma aka riga aka buɗe 15 daga cikinsu.

    Ya ce kula da harkokin addinin Musulunci na daga cikin manufofin gwamnatin sa, kuma ya ce yana da muhimmanci bayan batun tsaro.


    [ad_2]

    Source link

  • Fim Din Kasar Sin Kan Kisan Kiyashin Nanjing Ya Ja Hankulan Masu Kallo A Nijeriya

    [ad_1]

    Wani fim da aka nuna domin tunawa da cika shekaru 80 da samun nasarar yakin turjiyar jama’ar kasar Sin a kan zaluncin kasar Japan, da kuma yaki da mulkin danniya a duniya, ya yi matukar jan hankulan masu kallo a Nijeriya, lamarin da ya haifar da waiwaye game da muguntar da aka tafka a yakin da kuma darussan da za a koya a wannan zamanin. Kallon fim din wanda ofishin jakadancin kasar Sin da ke Nijeriya ya shirya a ranar Jumma’ar da ta gabata, ya samu halartar dimbin ‘yan Nijeriya da Sinawa mazauna kasar.

    Wani mai sharhi kan al’amuran duniya Lawal Sale, ya bayyana cin zalin da Japanawa suka yi wa al’ummar kasar Sin a matsayin “mummunan laifi ga bil’adama,” inda ya kara da cewa, jajircewar da Sinawa suka nuna wajen yin kasada da rayukansu don kiyaye hotunan shaidun irin ta’asar da sojojin kasar Japan suka tafka, sun yi matukar burge shi.

    Da yake jawabi gabanin nuna fim din, jakadan kasar Sin a Nijeriya Yu Dunhai, ya yi kira da a kara zurfafa hadin gwiwa a tsakanin kasashen biyu, yana mai jaddada wajibcin kiyaye zaman lafiya, da adalci, da ka’idojin kafuwar MDD.

    Yu ya ce, kasar Sin ta tafka asarar rayukan sojoji da fararen hula sama da miliyan 35 da kuma asarar tattalin arzikin da ya zarce dalar Amurka biliyan 600 a lokacin yakin duniya na biyu. Ya yi nuni da cewa, tsayin dakan da kasar Sin ta yi ya yi mummunar wargaza mulkin danniya, tare da ba da gudummawa mai tarihi ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a duniya.” (Abdulrazaq Yahuza Jere)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Zaɓen Ribas: APC ta yi nasara a ƙananan hukumomi 20, PDP ta samu 3

    [ad_1]



    Jam’iyyar APC ta yi nasarar lashe ƙananan hukumomi 20 daga cikin 23 a zaɓen ciyammomi da kansiloli da aka gudanar ranar Asabar.

    Jam’iyyar PDP wadda ke mulki a jihar ta samu nasara a ƙananan hukumomi uku ne kacal, a zaɓen da Hukumar Zaɓe ta Jihar Ribas (RSIEC) ta gudanar.

    Shugaban hukumar, Dokta Michael Odey, ne ya bayyana sakamakon a cibiyar hukumar da ke kan titin Aba Fatakwal, da yammacin ranar Lahadi.

    Ƙarin bayani na tafe…


    [ad_2]

    Source link

  • Hatsarin Jirgi: Babu Batun Zagon-ƙasa Ga Harkokin Sufurin Jiragen Ƙasan Abuja-Kaduna

    [ad_1]

    Binciken farko da Gwamnatin tarayya ta yi game da sakin layin da jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna ya yi a makon da ya gabata, ya nuna cewa, babu batun zagon-kasa ga harkokin sufurin jiragen.

    Ministan Sufuri, Saidu Ahmed Alkali ne ya bayyana hakan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a fadar gwamnati a karshen mako, tare da Babban Darakta na Hukumar Jiragen Kasa ta Nijeriya (NRC), Kayode Opeifa.

    Alkali ya ce, ana ci gaba da gudanar da bincike kan hatsarin amma ya jaddada cewa, binciken farko ya nuna babu wani batun zagon kasa.

    Ya tabbatar da cewa, an kwashe dukkan fasinjoji 618 da ke cikin jirgin cikin koshin lafiya. 20 sun samu kananan raunuka, yayin da bakwai ke kwance a asibiti amma tuni an sallame su, kuma NRC ce ta dauki nauyin biyan kudaden kiwon lafiyarsu.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Sojoji sun kashe mayaƙan Boko Haram 12, sun ƙwato makamai a Borno

    [ad_1]



    Dakarun Operation Haɗin Kai (OPHK) tare da Civilian JTF, sun yi nasarar kashe mayaƙan Boko Haram da ISWAP 12 a Jihar Borno.

    A ranar 29 zuwa 30 ga watan Agusta, sojojin sun kai farmaki ƙauyukan Tamsu Ngamdu, Dalakaleri, Gaza da Loskori Kura, inda suka yi artabu da ‘yan ta’addan.

    A Loskori Kura, sojojin sun yi nasara, inda suka kashe ’yan ta’adda 12, suka kuma kwato8 bindiga ƙirar AK-47 guda shida, harsasai guda takwas da magunguna iri-iri.

    Majiyoyin tsaro sun ce wasu daga cikin ’yan ta’addan sun ji raunuka, bayan artabun da suka yi da sojojin.

    Wannan farmaki ya lalata hanyoyin sadarwar ’yan ta’addan da dabarunsu a yankin, ya kuma haifar musu da cikas.

    Wannan nasara na zuwa ne a dai-dai lokacin da dakarun Nijeriya ke ƙara kai hare-hare ta ƙasa da sama a Arewa maso Gabas, musamman a dajin Sambisa, tafkin Chadi da tsaunin Mandara, domin kawo ƙarshen ta’addanci.


    [ad_2]

    Source link