Category: Latest News

  • Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

    [ad_1]

    “Kasa da kasa su kasance suna zaman daidaito da juna wajen sa hannun gudanar da harkokin duniya da ma yanke shawara da cin moriya” “Kada a tilasta kakaba dokokin cikin gida na wasu kasashe a kan sauran kasashe” “Nuna rashin amincewa da daukar matakai na kashin kai” “A yi kokarin daidaita gibin da ke tsakanin kasashe masu tasowa da kasashe masu ci gaba” “A dauki hakikanan matakai na hadin gwiwa”. A ranar 1 ga wata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya jagoranci taron kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai (SCO) Plus a birnin Tianjin da ke arewacin kasar Sin, inda ya gabatar da Tsarin Shugabanci na Duniya wato “GGI” a takaice, shawarar da ta samar da mafita ga duniyar da ke fama da tashe-tashen hankula a halin yanzu.

    A duniyar yau, aukuwar rikicin shiyya shiyya da matsalolin ci gaban tattalin arziki da rashin bin ka’idoji da dokoki da daukar matakai na kashin kai da kariyar ciniki da rashin tsarin shugabanci nagari a duniya, duk suna addabar kasashen duniya. Ta yaya za a inganta tsarin shugabanci na duniya, ya zama abin da ke bukatar a gano bakin zaren warware shi ga gamayyar kasa da kasa. To, faduwa ta zo daidai da zama bisa yadda kasar Sin ta gabatar da shawarar GGI.

    “Ya kamata mu bi tsarin daidaito a kan ‘yancin yankunan kasa sau da kafa, ya kamata mu kiyaye bin dokokin kasa da kasa, ya kamata mu aiwatar da tsarin mu’amala da bangarori daban daban, ya kamata mu yi yekuwar amfani da tsarin da zai fi mayar da hankali a kan al’umma, kana ya kamata mu mai da hankali kan daukar matakai na hakika.” Ka’idoji biyar ke nan da ke cikin shawarar GGI, wadanda suka mai da hankali a kan ainihin matsalolin da ake fuskanta a tsarin shugabanci na duniya, tare da bayyana matsayi da dabarun da suka kamata a dauka domin gyara tsarin. Daga cikinsu “tsarin daidaito a kan ‘yancin yankunan kasa” ya zama tushen tsarin shugabanci na duniya. Kasa da kasa, manya da kanana, masu karfi ko marasa karfi, ya kamata su kasance daidai-wa-daida wajen sa hannu ga harkokin duniya. Ya zama dole a kawo karshen yadda wasu ‘yan tsirarrun kasashe kawai ke fada a ji a harkokin duniya, kuma ya kamata “a kara wakilcin kasashe masu tasowa da fito da muryoyinsu a duniya”, don kara inganta adalcin tsarin duniya. Sa’an nan, dokokin kasa da kasa su kasance masu tabbaci ga tsarin shugabanci na duniya, wadanda ya kamata kasa da kasa su rubuta su, da kiyaye su, da ma aiwatar da su. Har wa yau, yin mu’amala da bangarori daban daban ya zama hanyar da za a bi wajen gudanar da tsarin shugabancin duniya, kasancewar tsarin shugabancin duniya na shafar kowa da kowa, ya kamata a daidaita hadin gwiwa da juna a maimakon nuna fin karfi. Kazalika, ya kamata a mai da hankali a kan al’umma, a sabili da yadda kyautata rayuwar al’umma shi ne jigon ainihin burin da ake neman cimmawa wajen inganta tsarin shugabanci na duniya. Daga karshe, daukar hakikanan matakai ya kasance ginshiki na tsarin shugabancin duniya, don daidaita matsalolin da ke addabar kasa da kasa, musamman ma kasashe masu tasowa.

    Bana ake cika shekaru 80 da samun nasarar yaki da mulkin danniya a duniya da ma kafa majalisar dinkin duniya(MDD). A shekaru 80 da suka wuce, al’ummun duniya sun hada karfi da karfe wajen samun nasarar yaki da mulkin danniya, kuma kasancewar kasar Sin daga cikin muhimman kasashen da suka cimma nasarar yakin, ta hada kai da kasa da kasa wajen kafa MDD. A yau kuma, lokacin da tsarin shugabanci na duniya ke fuskantar sabbin matsaloli, kasar Sin a matsayinta na babbar kasa da ke kokarin sauke nauyin da ke bisa wuyanta, za ta tsaya tsayin daka wajen kiyaye tsarin duniya da ke karkashin ginshikin MDD, ta hada kai da kasashe masu neman ci gaba, don dada yin kokarin gina al’ummar duniya mai kyakkyawar makoma ta bai daya, da ma tabbatar da zaman lafiya da ci gaba ga dukkanin bil Adama.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnatin Tarayya ta ɓullo da sabon manhajin karatun firamare da sakandire

    [ad_1]



    Gwamnatin Tarayya ta ɓullo da sabon manhajin karatu na makarantun firamare zuwa sakandire wanda zai fara aiki a sabon zangon karatu na bana da za a soma a watan Satumbar nan.

    Wannan na zuwa ne bayan kammala nazari mai zurfi kan manhajoji karatu a fannin ilimi a matakin farko da na manyan makarantun sakandire da kuma fannin fasaha.

    Gwamnatin ta ce ta ɗauki wannan matakin ne da nufin rage nauyin karatu kan ɗaliban da kuma inganta tsarin koyarwa a faɗin ƙasar.

    Ƙaramar Ministar Ilimi, Farfesa Suwaiba Sa’id Ahmad, ce ta bayyana hakan a madadin Ministan Ilimi, Dakta Maruf Tunji Alausa a ƙarshen makon jiya.

    Ministar ta ce an gudanar da bitar ce tare da haɗin gwiwar Hukumar Bincike da Cigaban Ilimi ta Nijeriya (NERDC), da Hukumar Ilimin Bai-ɗaya a Matakin Farko Universal Basic Education Council UBEC, da NSSEC, da NBTE, da sauran masu ruwa da tsaki.

    “Sabon tsarin zai kawo daidaito a darussan da ake koyarwa wajen zurfafawa da kuma koyar da ilimi a aikace.

    “A matakin farko, ɗaliban Firamare na aji 1-3 za su ɗauki darussa 9-10, yayin da waɗanda ke Firamare aji 4-6 za su ɗauki darussa 10-12.

    “A Ƙaramar Makarantar Sakandare yawan darussan za su kai 12-14 ne; ɗaliban babbar sakandare za su ɗauki darussa 8-9; sai kuma makarantun fasaha za su ɗauki darussan 9-11,” in ji ta.

    Farfesa Ahmad ta jaddada cewa, manhajojin da aka yi wa kwaskwarima an tsara su ne domin rage yawan abubuwan da ke ciki, da ba da ƙarin lokaci don koyo, da kuma tabbatar da cewa ilimi ya ci gaba da dacewa da abubuwan da suke faruwa a duniya a yau.

    Ma’aikatar ta yaba wa masu ruwa da tsaki bisa jajircewar da suka yi tare da ba su tabbacin cewa za a aiwatar da sabbin manhajoji tare da sanya ido sosai don tabbatar da samun karbuwa mai inganci da samun sauyi cikin sauƙi a makarantu a fadin Nijeriya.


    [ad_2]

    Source link

  • NDLEA Ta Kama Haramtattun Magungunan Gargajiya A Jihar Kano

    [ad_1]

    Hukumar NDLEA a Kano ta kama kwalabe 8,000 na Akuskura da ake zargin na ɗauke da ƙwayoyi, tare da tabar wiwi guda 48.

    An cafke wani mutum mai shekara 37, Ali Muhammad, bayan an gano kayan a cikin tirela ɗauke da kekuna a kan hanyar Zariya zuwa Kano a Gadar Tamburawa.

    NDLEA ta ce tana tsare da wanda ake zargin da kuma kayayyakin, yayin da ake ci gaba da bincike.

    Hukumar ta buƙaci jama’a su riƙa sanar da ita duk wani abin da suka zarga na da alaƙa da miyagun ƙwayoyi.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Ndume ya koka kan sabbin hare-haren Boko Haram a Borno

    [ad_1]



    Sanata Mohammed Ali Ndume, ya koka kan yawaitar sabbin hare-haren mayaƙan Boko Haram ƙananan hukumomin Gwoza da Askira/Uba, inda suka kashe mutanen da ba su ji ba ba su gani ba a ƙarshen mako.

    A safiyar ranar Asabar din da ta gabata a garin Ngoshe da ke Gwoza an kashe manoma biyar a lokacin da suke aiki a gonakinsu.

    Haka zalika, a yankin Mussa da ke Askira/Uba, wasu ’yan bindiga sun kai farmaki ƙauyen a ranar asabar da daddare, inda suka kashe matasa uku, kafin su ƙona wasu gidaje da shaguna da ƙauyen.

    Waɗannan munanan hare-haren sun jefa al’ummomin cikin zaman makoki wanda ya ƙara nuna damuwa kan rashin kare rayuka da dukiyoyin al’ummar yankin.

    Sai dai kuma Sanata Ndume ya yaba da sadaukarwar da sojoji rundunar‘Operation Hadin Kai’ da ke Arewa maso Gabas, bisa nasarorin da aka samu a kan ’yan ta’adda.

    Ndume ya bayyana duka abubuwan da suka faru a baya-bayan nan a matsayin “abin takaici” tare da cewa ci gaba da kai hare-hare a kan al’ummar yankin da ba su ji ba ba su gani ba, musamman manoma da matasa, wani abu ne mai muni na rashin tsaro da ke ci gaba da wanzuwa a Borno ta Kudu.

    Sanata Ndume ya tabbatar wa al’ummar Ngoshe, Mussa, da ma ɗauƙacin yankin Borno ta Kudu, kan y\ƙudurinsa na tsayawa tare da su a wannan mawuyacin lokaci.

    Ya kuma jaddada cewa, yana aiki kafaɗa da kafaɗa da gwamnatocin tarayya da na jihar Borno, da kuma rundunar sojojin Nijeriya da sauran hukumomin tsaro, domin ƙarfafa matakan tsaro a yankunan karkara.

    Ya kuma yi qira ga mazauna yankunan da su kasance masu lura da kuma bayar da cikakken haxin kai ga jami’an tsaro domin daƙile hare-haren da za a iya kaiwa nan gaba.

    Ya buƙaci a haɗa kai a tsakanin al’ummomi, yana mai jaddada muhimmancinsu wajen tinkarar ƙalubalen ’yan tada ƙayar baya.


    [ad_2]

    Source link

  • Ƙarfafa wasannin gargajiya zai hana matasa aikata laifi — ALGON

    [ad_1]



    Ƙungiyar Shugabannin Ƙananan Hukumomi na Najeriya (ALGON), ta yi kira ga Ƙungiyar ’Yan Jarida Masu Rubuta Labaran Wasanni (SWAN) da ta ƙara mayar da hankali wajen yada labarai kan wasannin gargajiya, irin su langa da kokawa.

    Shugaban Ƙaramar Hukumar Gombe wanda shi ne shugaban ALGON reshen Gombe, Barista Sani Ahmad Haruna, ya bayyana haka ne a lokacin da shugabannin SWAN na jihar suka kai masa ziyarar ban girma, inda suka nemi goyon bayansa kan babban taron bita da ƙungiyar ke shirin gudanarwa.

    A cewarsa, ƙara bayar da muhimmanci ga wasannin gargajiya zai taimaka wajen jan hankalin matasa zuwa harkokin ci-gaban rayuwa, tare da rage yawan fadawa cikin laifuka da shan miyagun ƙwayoyi.

    Ya kuma shawarci SWAN da ta ƙulla alaƙa da Hukumar Ci-gaban Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC) domin haɗa kai wajen yada labarai kan wasannin da ake gudanarwa a yankunan ƙarƙara.

    Shugaban na ALGON ya tabbatar da cewa ƙungiyarsa za ta ci gaba da tallafa wa SWAN da kuma sauran shirye-shiryen wasanni da suka dace da manufofin gwamnati a jihar.

    A nasa jawabin, Sakataren SWAN na jihar, Williams Attah, wanda ya wakilci shugaban ƙungiyar, Mark Nuhu Mabudu, ya gode wa shugaban ALGON bisa alƙawarin goyon baya, tare da tabbatar da cewa ƙungiyar za ta haɗa kai da shi a cikin shirye-shiryenta.


    [ad_2]

    Source link

  • ’Yansanda Sun Kama Masu Safarar Makamai A Katsina, Sun Ƙwato Makamai

    [ad_1]

    ’Yansanda a Jihar Katsina sun kama wasu mutane biyu da ake zargi da safarar makamai tare da ƙwato bindiga da harsasai.

    Mai magana da yawun ’yan sanda na ƙasa, Olumuyiwa Adejobi, ya ce an kama mutanen biyu; Abdussalam Muhammed (mai shekaru 25) da Aminu Mamman (mai shekaru 23) da safiyar ranar Litinin, da misalin ƙarfe 4:35 na sace a kan titin Ingawa zuwa Karkarku, a mota ƙirar Volkswagen Golf.

    Binciken cikin motar ya gano bindiga ƙirar GPMG ɗaya da harsasai sama da 1,200 da aka ɓoye a ciki.

    ’Yansanda sun ce an yi safarar makaman ne daga Jihar Jigawa zuwa Katsina domin bai wa ’yan ta’adda.

    A yanzu haka, mutanen biyun suna hannun ’yansanda yayin da ake ci gaba da bincike.

    Sufeto Janar na ’Yansanda, Kayode Egbetokun, ya yaba wa jami’an da suka gudanar da aikin, tare da yi  kira ga jama’a da su ci gaba da bayar da bayanai masu amfani domin taimaka wa yaƙi da laifuka.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Mutum 2 Sun Shiga Hannu Kan Sace Adaidaita Sahu A Borno

    [ad_1]

    Rundunar ’Yansandan Jihar Borno, ta kama wasu mutane biyu bisa zargin satar adaidaita sahu a unguwar Jajeri da ke Maiduguri.

    Kakakin rundunar, ASP Nahum Daso, ya ce lamarin ya faru ne a ranar 4 ga watan Agusta, 2025, lokacin da wani Abubakar Tijani ya kai rahoton cewa an sace mass adaidaita sahu.

    Bayan rahoton, rundunar Crack Squad ta kama wasu mutum biyu; Yakubu Musa da Adamu Musa, dukkaninsu daga Jajeri.

    Lokacin gudanar da bincike, sun amsa laifin, kuma an samo adaidaita sahun a wajensu.

    Kwamishinan ’Yansandan jihar, Naziru Abdulmajid, ya yaba wa jami’an bisa jajircewarsu tare da tabbatar wa jama’a cewa ’yansanda za su ci gaba da yaƙi da laifuka a jihar.

    Ya kuma roƙi jama’a da su ci gaba da ba da sahihan bayanai don taimakawa wajen tabbatar da tsaro a jihar.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnatin Kaduna Ta Gargaɗi El-Rufai Kan Yunƙurin Tayar Da Rikici A Jihar

    [ad_1]

    Gwamnatin Jihar Kaduna ta zargi tsohon gwamna Nasir El-Rufai da shirin tayar da fitina a jihar, tare da gargadɗnsa da ya daina duk wani yunƙuri na ta da hankalin al’umma.

    A cikin wata sanarwa da Kwamishinan Tsaron Cikin Gida, Dokta Suleiman Shuaibu, ya fitar, Gwamnatin ta ce al’ummar jihar sun wahala, an zubar da jininsu tare da samum rabuwar kai a lokacin mulkin El-Rufai.

    Sanarwar ta bayyana cewa abubuwan da El-Rufai ke yi a kwanakin nan ba siyasa ce kawai ba, barazana ce kai-tsaye ga zaman lafiya da ci gaban jihar.

    Gwamnatin ta zarge shi da ƙoƙarin jefa Kaduna cikin rikicin ƙabilanci da addini, rashin tsaro da matsalolin tattalin arziƙi.

    Gwamnatin ta ce El-Rufai ba ya jin daɗin ci gaban da aka samu a ƙarƙashin Gwamna Uba Sani, wanda aka yaba da salon mulkinsa ta hanyar haɗa kan jama’a da mayar da hankali kan tsaro.

    Ta ce cikin ƙasa da shekara biyu, Kaduna ta fito daga durƙushewar tsari zuwa zama jihar da ake ganin tsari.

    Haka kuma, gwamnatin ta yi zargin cewa El-Rufai ya ƙara ƙoƙarin tayar da rikici bayan abokan siyarsarsa sun sha kaye a zaɓen cike gurbi na ranar 16 ga watan Agusta.

    Ta ce sakamakon ya nuna rashin amincewa da salon mulkin El-Rufai na “rabuwar kai da wariya” tare da amincewa da salon mulkin Gwamna Uba Sani.

    An yi ƙoƙarin jin ta bakin El-Rufai kan waɗannan zarge-zarge, amma ba a iya samun shi ba zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Kurame na buƙatar masu fassara a asibitoci

    [ad_1]



    Al’ummar kurame sun koka bisa matsalolin da suke fuskanta a fannin kiwon lafiya, sakamakon rashin masu yi musu fassara a asibitoci a Jihar Yobe.

    Malam Kolo Abba, Shugaban Ƙungiyar Kurame a Ƙaramar Hukumar Damaturu, ya ce kurame majinyatan sukan koƙarta wajen fahimtar ƙa’idojin likitoci da na kiwon lafiya, amma duk da hakan suna cikin haɗari.

    Abba ya yi wannan kira ne ta bakin wani mai fassara a taron masu ruwa da tsaki kan shirye-shiryen tattaunawa kan kasafin kuɗin shekarar 2026 da aka shirya don inganta aiki.

    Ya ce rashin masu fassara a asibitoci alama ce ta rashin kula da kurame a jihar, don haka akwai buƙatar ɗaukar matakan gaggawa don tabbatar da samun damar gudanar da ayyukan yau da kullum gare su.

    “Matsalarmu ba kiwon lafiya kaɗai ta shafa ba, a fannin ilimi, akwai makaranta ta musamman a faɗin jihar nan, kuma an bar yaranmu da dama a baya. Muna buƙatar ingantacciyar makarantar sakandaren kurame a jihar,” in ji shi.

    Abba ya kuma yi kira da a sanya masu fassara a cikin shirye-shiryen gwamnati da kuma taron jama’a, don tabbatar da cewa bayanai kan manufofi da dama sun isa ga kurame.

    Ya kuma bukaci gwamnati da ta tallafa wa mambobin ƙungiyar da jarin fara aiki, yana mai jaddada cewa da yawancinsu suna son yin kasuwanci amma ba su da hali.

    Baba Kucici, sakataren ƙungiyoyin fararen hula a Jihar Yobe, shi ma ya gabatar da jerin tarin bukatun ’yan kasa a wurin taron.

    Ya jaddada bukatar gwamnati ta samar da hanyar da za ta riƙa bibiyar ayyuka da shirye-shirye kai tsaye, yana mai cewa hakan zai nuna ɗaukar nauyi da kuma samun amincewar jama’a.

    Aminiya ta ruwaito cewa tattaunawar ta tattaro masu ruwa da tsaki daga gwamnati, ƙungiyoyin farar hula, da ƙungiyoyin al’umma don daidaita abubuwan da ’yan qasa suka sa a gaba kafin kasafin 2026.


    [ad_2]

    Source link

  • Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Zawarcin Peter Obi

    [ad_1]

    Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya gargaɗi jam’iyyar PDP da kada ta dawo da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar Labour LP, Peter Obi, cikin jam’iyyar.

    Wike ya ce dawo da Obi PDP zai zame wa jam’iyyar babbar illa.

    Yayin hira da ’yan jarida a Abuja a ranar Litinin, Wike ya zargi PDP da rashin ɗaukar darasi daga kura-kuran da ta yi a zaɓen 2023.

    Ya ce jam’iyyar ta sha kaye ne saboda ta yi watsi da tsarin rabon mulki da adalci, inda ta bari shugaban jam’iyya da ɗan takarar shugaban ƙasa duka suka fito daga Arewa.

    “Na yi gargaɗi tun farko. Ba za ku iya samun ɗan takarar shugaban ƙasa da shugaban jam’iyya daga yanki ɗaya ba. Na faɗa musu zai jawo mana koma baya, kuma hakan ne ya faru,” in ji Wike.

    Kan batun yiwuwar Obi zai koma PDP, Wike ya yi watsi da shi, ya ce hakan zai jawo wa jam’iyyar matsala.

    “Obi ya zargi PDP, ya ce jam’iyyar ta lalace. Yanzu kuma jam’iyyar ta gyara kenan a gare shi? Wannan zai kashe jam’iyyar,” in ji shi.

    Wike ya ce dawo da Obi saboda kawai neman mulki zai rusa ƙa’idoji da mutuncin jam’iyyar.

    Ya dage cewa hanyar da PDP za ta sake bi domin farfaɗowa ita ce bin tsarin rabon mulki, adalci da gaskiya, ta yadda shugabancin ƙasa zai koma Kudu.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link