Category: Latest News

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda, Sun Ceto Mata Da Yara A Zamfara

    [ad_1]

    Dakarun rundunar ‘Operation FANSAN YAMMA (OPFY)’ sun kashe ‘yan ta’adda da dama tare da kubutar da wasu mutane tara da aka yi garkuwa da su a karamar hukumar Sabon Birni ta Jihar Sakkwato.

    A wata sanarwa da jami’in yada labarai na rundunar OPFY, Kaftin Adewusi David, ya fitar, ya ce an samu nasarar hakan ne a wani harin kwanton bauna da aka kai a karamar hukumar Shinkafi ta jihar Zamfara da yammacin ranar Lahadi, 31 ga watan Agusta, 2025.

    Ya ce, harin ya biyo bayan sahihan bayanan sirri da suka tabbatar da cewa, anga tafiyar wasu ‘yan ta’adda a wani fitacce wuri tsakanin Isa zuwa Shinkafi zuwa Kaura Namoda, wanda ya hada jihohin Zamfara da Sokoto.

    Ya kara da cewa, sojojin sun yi kwanton bauna ne domin farmakar ‘yan ta’addan, amma da suka lura da kasancewar sojojin a yankin, sai suka yi yunkurin boyewa jikin mutanen da suka yi garkuwa da sun.

    “Amma sojojin sun fatattake su cikin dabara da kaifin hikima wanda hakan ya haifar da kashe wasu daga cikin ‘yan ta’addan yayin da sauran suka tsere da munanan harbin bindiga” in ji Kaftin David




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Xi Ya Gabatar Da Jawabin Bude Taron Majalisar Shugabannin Kasashe Membobin Kungiyar SCO

    [ad_1]

    Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da jawabin bude taro na 25 na majalisar shugabannin kasashe membobin kungiyar hadin kai ta Shanghai wato SCO, a yau Litinin a birnin tashar ruwa na Tianjin.

    Cikin jawabin nasa, shugaba Xi ya ce SCO ta bunkasa zuwa kungiyar shiyya mafi girma a duniya, wadda ke kunshe da adadin kasashe da suka kai 26, tare da hade sama da yankuna 50, da jimillar kimar tattalin arziki da ta kusa dala tiriliyan 30.

    Shugaban na Sin ya kara da cewa, har kullum SCO na goyon bayan sassan kasa da kasa a fannin tabbatar da gaskiya da adalci, da yin tafiya tare da dukkanin sassa, da koyi da juna tsakanin mabanbantan wayewar kai, tana kuma adawa da danniya da siyasar nuna fin karfi, don haka ta zama ginshikin wanzar da zaman lafiya a duniya. A hannu guda kuma darajar jimillar hada-hadar cinikayya tsakanin kasar Sin da kasashe membobin SCO ta kai dala tiriliyan 2.3, adadin da ya dara wanda aka yi hasashe tun kafin cikar wa’adin.

    Har ila yau, shugaba Xi ya ce cikin wannan shekara, Sin za ta samar da tallafin yuan biliyan biyu, kimanin dalar Amurka miliyan 280.5 ga kasashe membobin SCO. Kazalika, za ta samar da rancen yuan biliyan 10, kimanin dalar Amurka biliyan 1.4 ga tsarin hada-hadar bankunan kasashe membobin kungiyar cikin shekaru uku dake tafe. (Mai fassara: Saminu Alhassan)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • NAPTIP Da Hisbah Sun Ceto Mata 12 Da Aka Yi Safararsu A Kano Zuwa Saudiyya

    [ad_1]

    Hukumar hana fataucin mutane ta kasa reshen jihar Kano, ta tseratar da wasu mata 12 dake da shekaru tsakanin 15 zuwa 50 daga kungiyar masu safarar mutane.

    Kwamandan hukumar ta NAPTIP na shiyyar, Mista Abdullahi Babale, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Litinin a Kano yayin da yake karbar wadanda aka ceton daga hukumar Hisbah ta jihar Kano, wadda ta gudanar da aikin ceton tare da hadin gwiwar hukumar.

    A cewar Babale, an kama matan ne a ranar 31 ga watan Agusta a babban titin yammacin jihar Kano da ke Hotoro, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa Ghana zuwa Saudiyya.

    Ya bayyana cewa, matan sun fito ne daga jihohin Kano, Katsina, Borno, Jigawa, da Zamfara, inda aka yi musu alkawuran samun ingantattun ayyukan yi a kasar ta Saudiyya.

    An kama daya daga cikin wadanda ake zargi da safarar matan mai suna Mohammed Saleh mai shekaru 45 da haihuwa.

    Babale ya ce, ana ci gaba da kokarin damke wasu da ake zargi da hannu wajen safarar mutanen.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Sanin Ya Kamata

    [ad_1]

    Babban magatakardar Majalisar Dinkin Duniya, Antonio Guterres, wanda ya shigo kasar Sin don halartar taron koli na kungiyar hadin-kai ta Shanghai wato SCO na bana, ya zanta da dan jaridan babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG a birnin Tianjin, inda ya ce, Xi Jinping shugaban kasa ne mai sanin ya kamata wajen tsara manyan tsare-tsare.

    Guterres ya ce, akwai misalai da dama da suke iya tabbatar da haka. Alal misali, shugaba Xi ya taba sanar da burin gina na’urorin samar da wutar lantarki bisa makamashin da ake iya sabuntawa, wadanda karfinsu ya zarce kilowatt biliyan 1.2 zuwa shekarar 2030 a kasar Sin, wanda aka riga aka cimma shi.

    Kazalika, ya yi alkawarin cimma nasarar kaiwa ga kololuwar fitar da sinadarin carbon a kasar Sin kafin shekarar 2030, wanda tuni aka cimma nasararsa. Har wa yau, yayin da kasashe da dama ke tunanin dabarun kyautata motoci dake aiki da man diesel, tun shekaru da dama da suka wuce kasar Sin ta kuduri aniyar kara raya kirar motoci dake aiki da lantarki, kuma a halin yanzu irin wadannan motocin na mamaye kasuwannin dukkanin fadin duniya.

    Guterres ya kuma ce, yayin da duniyarmu ke fuskantar tarin yanayin rashin tabbas, abu ne mai wuya a iya tsara manufofi masu dorewa, don haka, sanin ya kamata da shugaba Xi ke da shi wajen tsara manufofi na da matukar muhimmanci. (Murtala Zhang)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • An kama ɗan shekara 60 kan yi wa mai shekara 24 fyaɗe

    An kama ɗan shekara 60 kan yi wa mai shekara 24 fyaɗe

    [ad_1]



    Rundunar ’yan sandan Jihar Legas ta kama wani dattijo mai shekaru 60, Ajayi Femi, bisa zargin yi wa wata budurwa mai shekaru 24 fyaɗe.

    Mai magana da yawun rundunar, CSP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar da faruwar lamarin a jiya Lahadi.

    Ya bayyana cewa an gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu ta hannun sashen da ke bincike cin zarafin mata na rundunar da ke Ikeja.

    A cewar Hundeyin, lamarin ya faru ne a ranar 22 ga watan Agusta, 2025, inda ƙanwar wacce abin ya faru da ita ta kai rahoto ofishin ‘yan sanda na Meiran, daga nan kuma aka miƙa lamarin zuwa sashen bincike na musamman.

    Binciken farko da ya haɗa da gwajin likitoci ya nuna cewa wanda ake zargi ya zuba wani abu a cikin abin sha na budurwar, wanda ya sanya ta suma, kafin ya aikata lalata da ita ba tare da amincewarta ba.

    “Tuni aka gurfanar da shi gaban kotu inda aka ajiye shi a gidan yari har zuwa lokacin da aka sa ranar sake zama,” in ji Hundeyin.

    Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Lagos, CP Olohundare Jimoh, ya bayyana cewa rundunar ta kuduri aniyar ganin an samu adalci ga duk wanda aka ci zarafinsa, tare da tabbatar da tsaron rayuka da mutuncin al’ummar jihar.

    Ya kuma yi kira ga jama’a da su riƙa kai rahoton duk wani laifi da ya shafi fyaɗe ko cin zarafi zuwa mahukunta mafi kusa domin a ɗauki mataki cikin gaggawa.


    [ad_2]

    Source link

  • Tinubu Ya Yi Adalci Ga Dukkan Yankunan Nijeriya – Ministan Yaɗa Labarai

    [ad_1]

    Gwamnatin Tarayya ta ƙaryata zargin wai ana nuna bambanci wajen rabon ayyuka da naɗin muƙamai a ƙarƙashin shugabancin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, tana mai cewa babu wani yanki da aka ware, kowane ɓangare yana samun kulawa iri ɗaya.

    Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya faɗa a cikin wata sanarwa a ranar Lahadi, cewa gwamnatin Tinubu tana tafiya ne bisa gaskiya, adalci da daidaito wajen rarraba ayyuka da damarmaki.

    Ya ce manyan ayyukan raya ƙasa suna gudana a dukkan yankuna shida, ciki har da tituna, gadaje, layin dogo, wutar lantarki da kuma cibiyoyin kula da lafiya fiye da 1,000 da aka gyara a faɗin ƙasar.

    A cewar sa, yankin Arewa-maso-yamma ya samu kaso mafi girma na ayyuka da ya kai naira tiriliyan 5.97, Kudu-maso-kudu ya samu naira tiriliyan 2.41, Arewa-ta-tsakiya naira tiriliyan 1.13, Kudu-maso-gabas naira biliyan 407, Arewa-maso-gabas naira biliyan 400, yayin da Kudu-maso-yamma (ban da Legas) ya samu naira biliyan 604.

    Idris ya ce dukkan waɗannan yankuna suna amfana da manyan hanyoyi, layukan dogo da kuma hukumomin raya yankuna.

    Ministan ya ce daga cikin muhimman ayyukan da ake aiwatarwa akwai Titin Bakin Teku na Legas zuwa Kalaba, da Babban Titin Sakkwato zuwa Badagiri, da gyaran layin dogo daga Fatakwal zuwa Maiduguri, da kuma Hanyar Gadar Neja ta 2.

    Haka kuma, gwamnati ta samar da fiye da naira biliyan 250 don ayyukan jirgin ƙasa a Kano da Kaduna, yayin da ake gudanar da ayyukan layin dogo na Cikin gari a Legas da Ogun. Gaba ɗaya, an ƙiyasta cewa waɗannan ayyuka za su samar da fiye da ayyukan yi 250,000 a faɗin ƙasar.

    Idris ya ƙara da cewa an farfaɗo da Tashar Wutar Lantarki ta Kaduna mai ƙarfin megawat 255, ana ci gaba da aikin iskar gas na AKK, tare da bunƙasa haƙo mai a yankin Kolmani (a Bauchi da Gombe).

    Ya ce naɗin muƙaman da Shugaban Ƙasa Tinubu ya yi ya nuna haɗin kai, yana mai jaddada cewa abin da ke jagorantar shi shi ne ƙwarewa da kuma haɗin kan ƙasa.

    Idris ya tabbatar wa ‘yan Nijeriya da cewa Shirin Sabunta Fata zai ci gaba da tabbatar da daidaito a cigaban ƙasa.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Xi Jinping Shugaban Kasa Ne Mai Hangen Nesa

    [ad_1]

    Yayin da yake zantawa da ’yar jaridar babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin wato CMG, firaministan kasar Pakistan Shehbaz Sharif, ya bayyana cewa, Xi Jinping shugaban kasa ne mai matukar hangen nesa.

    A cewar firaministan, Xi Jinping, shugaban kasa ne wanda ke mayar da hankali sosai kan kyautata rayuwar jama’a, kuma a karkashin jagorancinsa, kasar Sin ta samu nasarar yaki da matsanancin talauci, al’amarin da ke bukatar matukar hangen nesa da babbar hikima. Kazalika, shugaba Xi yana amincewa da ra’ayin cudanyar sassan kasa da kasa.

    Firaminista Shehbaz ya kara da cewa, ba sauya yanayin tattalin arzikin kasar Sin kawai shugaba Xi ya yi ba, har ma ya mayar da kasar zuwa matsayi na biyu a karfin tattalin arziki a duniya, kuma babbar kasa mai karfin soja. Ya ce abu mafi muhimmanci a nan shi ne, shugaba Xi ya dade yana dukufa kan taimaka wa sauran kasashe ta yadda za su mori nasarorin da kasar Sin ta samu, tare da kokarin inganta hadin-gwiwa tsakanin Sin da sauran kasashe, ta yadda kasashe masu karamin karfi su ma za su iya cin gajiya, kuma jama’arsu za su iya ficewa daga kangin talauci, da jin dadin nasarorin da aka samu wajen raya al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya. (Murtala Zhang)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Ina Da Yaƙinin Tinubu Ne Zai Lashe Zaɓen 2027 — Wike

    [ad_1]

    Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), Nyesom Wike, ya bayyana ƙwarin gwuiwar cewa Shugaba Bola Tinubu zai sake lashe zaɓen shugaban ƙasa na shekarar 2027, inda ya ce ya shirya yin “alwashi” akan wannan nasara.

    Wike ya yi wannan bayani ne a yayin wata tattaunawa da manema labarai a Abuja, yana mai ƙaryata hasashen tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, wanda ya ce Tinubu ba zai yi nasara ba a zaɓen mai zuwa. Wike ya ce, “Ina da tabbacin Shugaba Bola Tinubu zai yi nasara a zaben 2027. Na ji wani yana cewa zai zo na uku, ban san irin lissafin da ya yi ba. Idan zai zo na uku, to waye zai zama na farko da na biyu?”

    A ranar da ta gabata a wata hira da Channels Television, El-Rufai ya yi hasashen cewa Tinubu zai ƙare a mataki na uku a zaben 2027, yana mai cewa APC ba ta da wata hanyar kaiwa ga nasara. Ya ƙara da cewa ‘yan Nijeriya su ne ya kamata su tantance yadda gwamnati take gudanar da mulki da kuma irin tasirin da take yi a rayuwarsu.

    Sai dai Wike ya ce siyasar ƙasar ta sauya daga lokacin zaben 2023, inda ya yi watsi da barazanar da Peter Obi na Labour Party zai iya kawo wa Shugaba Tinubu. Ya ce, “A zaben 2027, Peter Obi ba zai zama barazana ba. A 2023 ya samu ƙuri’u sama da miliyan shida, amma a 2027 lissafin siyasar zai bambanta kwata-kwata.”




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Simon Ekpa: An ɗaure ɗan Nijeriya kan laifin ta’addanci a Finland

    [ad_1]



    Wata kotu a ƙasar Finland ta yanke wa ɗan Najeriya mai rajin ɓallewar ƙasar Biyafara, Simon Ekpa, hukuncin ɗaurin shekara shida a gidan yari bisa laifukan da suka shafi ta’addanci, zamba da karya doka.

    Kotun ta tabbatar da cewa Ekpa ya aikata laifuka da suka haɗa da ƙoƙarin hargitsa jama’a da nufin ta’addanci da kuma shiga cikin ayyukan ƙungiyoyin masu ɗaukar makami.

    Haka kuma, kotun ta ce an same shi da laifin zamba ta haraji da keta wasu dokokin Finland.

    A cewar kotun, daga watan Agusta 2021 zuwa Nuwamba 2024, Ekpa ya yi amfani da kafafen sada zumunta wajen yaɗa shirye-shiryen neman ɓallewar Biyafara daga Najeriya, da kuma ingiza mabiyansa su aikata laifuka.

    Rahoton kotun ya ce ƙungiyoyin da yake jagoranta sun kafa wasu tsageru masu ɗaukar makami, waɗanda aka bayyana a matsayin ƙungiyoyin ta’addanci. Har ila yau, an tabbatar da cewa ya samar musu da makamai, harsasai da abubuwa masu fashewa ta hannun wasu mabiyansa.

    An ce duk waɗannan ayyukan Ekpa ya ke gudanarwa ne daga garin Lahti na ƙasar Finland, duk da cewa shi ya musanta zarge-zargen a kotu.

    Sai dai alƙalin ya bayyana cewa hukuncin ba shi ne na ƙarshe ba, inda ake tsammanin Ekpa zai iya ɗaukaka ƙara zuwa kotu mafi girma.

    Martanin Gwamnatin Najeriya

    Bayan yanke hukuncin, Gwamnatin Tarayya ta bayyana jin daɗinta, tana mai cewa wannan hukunci “babban lamari ne” wajen tabbatar da adalci da kuma ƙarfafa dangantaka tsakanin Najeriya da Finland.

    A wata sanarwa da Ministan Yaɗa Labarai, Mohammed Idris, ya fitar a ranar Litinin, ya ce: “Tsawon wasu shekaru wutar da Ekpa ya rura ta haddasa bala’i kan rayukan ɗaruruwan ‘yan Najeriya.

    “Iyalai sun tarwatse, kasuwanci sun lalace, yara sun zama marayu, al’umma kuma sun riƙa rayuwa cikin tsoro.

    “Saboda haka wannan hukuncin ya tabbatar da matsayar da Najeriya ta riƙa, tare da nuna wa masu tsattsauran ra’ayi cewa duniya na kallonsu, kuma doka za ta cim musu.”

    Ya ƙara da cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu za ta ci gaba da kare mutuncin Najeriya da ɗaukakar ‘yan ƙasa ta kowace fuska—ta hanyar diflomasiyya, soja, shari’a da sauran hanyoyin da suka dace.

    Ministan ya kuma yi kira ga duk wanda ya bi hanyar Ekpa ko sauran masu tayar da zaune tsaye su ajiye makami ya rungumi zaman lafiya, yana mai cewa: “Najeriya ƙasa ce mai faɗi, kuma za ta iya ɗaukar kowa, amma ba a samun ci gaba a kowace al’umma da ke fuskantar tashin hankali da rarrabuwar kawuna.”

    A ƙarshe, gwamnatin ta gode wa ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, rundunar soji, ’yan sanda da sauran hukumomin tsaro, bisa jajircewa wajen kare ƙasar daga duk wani ƙalubale.


    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnan Neja ya rushe kwamishinoninsa

    [ad_1]



    Gwamna Mohammed Umaru Bago na Jihar Neja ya rushe majalisar kwamishinoninsa.

    Sakataren Yaɗa Labarai na gwamnan, Bologi Ibrahim, ya ce gwamnan ya sanar da rushe majalisar kwamishinoninsa ne a yayin taron Majalisar Zartarwa ta jihar a safiyar Litinin ɗin nan.

    Ya kuma yaba musu bisa gudunmawar da suka bayar wajen kawo ci-gaba mai ma’ana a jihar tare da yi musu fatan alheri.

    Sai dai kuma gwamnan ya sake nada sakataren gwamnatin da shugaban ma’aikatan fadar gwamnati da mataimakinsa a da wasu jami’ai a kan muƙamansu.


    [ad_2]

    Source link