Category: Latest News

  • ’Yan sanda sun kama ɗan bindiga da shanu 10 a Kebbi

    [ad_1]



    Rundunar ’yan sandan Jihar Kebbi ta cafke wani ɗan bindiga da ake zargin ɗan ƙungiyar Lukurawa ne tare da shanu goma da ya sato, a wani samame da aka kai kasuwar shanu ta Bachaka.

    Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, CSP Nafi’u Abubakar, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadin da ta gabata.

    A cewarsa, “bayan samun sahihan bayanan sirri, an kama wani Salihu Umar, mai shekaru 42, ɗan asalin Dogon Dutse a Jamhuriyar Nijar, wanda ya shiga kasuwar shanu ta Bachaka da shanu 10 da ya sace wa wani Usman Aliyu na garin Zogirma a Ƙaramar Hukumar Bunza.”

    Ya ce shanun na daga cikin guda 68 da ake zargin ’yan bindigar Lukurawa sun sace sannan suka tsallaka da su zuwa Nijar a ranar 20 ga watan Agusta.

    Kwamishinan ’yan sanda na Jihar Kebbi, CP Bello M. Sani, ya jinjina wa DPO na Bachaka da tawagarsa bisa wannan nasara, yana mai kira gare da su ƙara jajircewa wajen kare al’umma.

    Kwamishinan ya kuma jaddada cewa rundunar za ta ƙara ƙaimi wajen cafke duk mambobin ƙungiyar tare da ƙwato sauran shanun da aka sace.

    Ya roƙi al’ummar jihar da su kasance masu lura da gaggauta bayar da bayanai kan duk wani motsi da ba su aminta da shi ba zuwa jami’an tsaro mafi kusa domin daƙile ayyukan ’yan ta’adda.


    [ad_2]

    Source link

  • Sabuwar Ajandar Kasar Sin Ta Inganta Magance Gibin Kudi A Duniya

    [ad_1]

    Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da ajandar mulkin duniya a taron “SCO+” na birnin Tianjin a jiya Litinin. Wannan ajanda, ta nuna hanyar da za a bi, tare da ba da jagoranci ga aiwatar da ayyukan gina tsarin mulkin duniya mai adalci da dacewa, a karkashin yanayin duniya mai fuskantar manyan sauye-sauye, da kuma jagorancin cike gibin kudi na samar da ci gaba da bunkasa.

    Sabuwar ajandar mulkin duniya da Xi Jinping ya gabatar, ta yi magana kai tsaye kan wasu muhimman abubuwa guda uku a tsarin jagorancin duniya, wato rashin daidaiton iko, da rarrabuwar ra’ayoyi, da kuma rashin daukar matakai.

    Ajandar, wadda ta fitar da wasu ka’idoji guda biyar, wato tabbatar da daidaiton ikon mulkin kasa, da bin dokokin kasa da kasa, da aiwatar da ra’ayin bangarori daban-daban, da ba da shawarar kula da bukatun jama’a, da kuma mai da hankali kan aiwatar da matakai na samar da wata hanya a fayyace ga kasashen duniya ta gudanar da ayyuka cikin adalci, yayin da ake jagorancin duniya, kamar shiga ayyuka, da yanke shawara da kuma samun fa’ida.

    Misali, ajandar ta jaddada cewa, “Akwai bukatar inganta wakilci da murya tsakanin kasashe masu tasowa,” wannan hakan ya dace da fatan kasashe masu tasowa na samar da tsari mai adalci. Kazalika, shawarar “Kaucewa amfani da ma’aunai biyu, wato kauracewa kakaba ‘dokokin gida’ na wasu kasashe a kan sauran kasashe”, wanda hakan ya nuna rashin amincewa da ra’ayin bangare guda daya. (Safiyah Ma)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Kuri’ar CGTN Ta Nuna Gamsuwar Al’ummu Da Rawar Da Sin Ta Taka Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na 2

    [ad_1]

    A gobe Laraba ne kasar Sin za ta gudanar da gagarumin bikin murnar cika shekaru 80 da cimma nasarar yaki da mamayar dakarun kasar Japan, da yakin kin tafarkin murdiya a matsayinta na kasa.

    Game da hakan, kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar da kuri’ar jin ra’ayin al’umma, wadda ta kunshi mutane 11,613 daga kasashe 39, kuri’ar da ta nuna gamsuwar al’ummun kasa da kasa da rawar da Sin ta taka a matsayinta na babban filin dagar gabashin duniya na fafata yakin duniya na biyu. Masu bayyana ra’ayoyin sun gamsu da babbar gudummawar da Sin din ta bayar, da matukar sadaukarwarta ga burin cimma nasarar yakin.

    A tsawon shekaru 14 na yakin, sojojin kasar Sin da ma fararen hular kasar, sun yi asarar rayuka miliyan 35, da tattalin arziki na sama da dala biliyan 600, kuma kasar ta yi tsayin daka, har ta kai ga murkushe aniyar mamayar dakarun kasar Japan, inda daga karshe Sin din ta zamo muhimmin fage a gabashin duniya da aka gwabza yakin duniya na biyu.

    Kuri’ar jin ra’ayin jama’ar ta nuna yadda kaso 73.6 bisa dari na masu bayyana mahangarsu, suka jinjinawa babbar gudummawar Sin ga cimma nasarar yakin kin tafarkin murdiya. Cikin masu bayyana ra’ayoyin daga kasashe 39, al’ummun kasashe 36 sun amince da kasancewar Sin babban fagen dagar gabashin duniya a yakin duniya na biyu, adadin da ya kai kaso 92.3 bisa dari na jimillar kasashen da aka ji ta bakinsu.

    Wani abun lura a nan shi ne dukkanin al’ummun kasashe takwas na nahiyar Asiya da aka gudanar da binciken, sun yarda cewa Sin din ce babban fagen dagar gabashin duniya a yakin duniya na biyu, inda sama da kaso 70 bisa dari na masu bayyana ra’ayoyi daga kasashen Indiya da Malesiya suka aminta da hakan. (Mai fassara: Saminu Alhassan)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnatin Kano za ta sake yi wa zawarawa da ’yan mata auren gata

    [ad_1]



    Gwamnatin Kano ta sanar da cewa tana shirye-shiryen gudanar da auren zawarawa da ’yan mata, wanda ya zarce na baya da ta yi.

    Babban Kwamanda Hisbah na Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ne bayyana hakan a yayin ziyarar gaisuwa da ya kai wa Fadar Sarkin Rano a ranar Litinin.

    Sheikh Daurawa ya ce a wannan karon angwaye da amaren za su mori gwaggwaban tanadi na musamman daga Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf.

    Ana iya tuna cewa, a watan Oktoban 2023 ne Gwamnatin Kano ta ɗaura auren mata 1,800 da angwayensu 1,800 wanda ta ɗauki watanni tana shiryawa.

    Tun bayan hawansa mulki ne, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanar da cewa zai yi wa matan da ba su da galihu auren gata, ta hanyar samar musu da dukkan kayayyakin da mace ke bukata a gidan aure da kuma yi musu walicci.

    A wancan lokacin, ɗaura aurarrakin ne a wasu masallatan Juma’a a dukkan ƙananan hukumomi 44 da ke faɗin jihar.

    A babban Masallacin Juma’a na gidan Sarkin Kano kawai an daura auren kusan mutum 300 wanda shi ne Gwamna Abba Kabir Yusuf da Shugaban Hisbah Sheikh Daurawa, wanda shi ne jagoran hidimar suka halarta.

    Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ne ya yi walicin angwaye yayin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya zama waliyyin amare a kan sadaki Naira 50,000 ga kowace amarya.

    Gwamnan Jigawa Umar Namadi na daga cikin waɗanda suka harlaci daurin auren.


    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnatin Kano za ta sake aurar da zawarawa da ’yan mata

    [ad_1]



    Gwamnatin Kano ta sanar da cewa tana shirye-shiryen gudanar wa auren zawarawa da ’yan mata, wanda ya zarce na baya da ta yi.

    Babban Kwamanda Hisbah na Kano, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ne bayyana hakan a yayin ziyarar gaisuwa da ya kai wa Fadar Sarkin Rano a ranar Litinin.

    Sheikh Daurawa ya ce a wannan karon angwaye da amaren za su mori gwaggwaban tanadi na musamman daga Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf.

    Ana iya tuna cewa, a watan Oktoban 2023 ne Gwamnatin Kano ta ɗaura auren mata 1,800 da angwayensu 1,800 wanda ta ɗauki watanni tana shiryawa.

    Tun bayan hawansa mulki ne, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya sanar da cewa zai yi wa matan da ba su da galihu auren gata, ta hanyar samar musu da dukkan kayayyakin da mace ke bukata a gidan aure da kuma yi musu walicci.

    A wancan lokacin, ɗaura aurarrakin ne a wasu masallatan Juma’a a dukkan ƙananan hukumomi 44 da ke faɗin jihar.

    A babban Masallacin Juma’a na gidan Sarkin Kano kawai an daura auren kusan mutum 300 wanda shi ne Gwamna Abba Kabir Yusuf da Shugaban Hisbah Sheikh Daurawa, wanda shi ne jagoran hidimar suka halarta.

    Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ne ya yi walicin angwaye yayin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya zama waliyyin amare a kan sadaki Naira 50,000 ga kowace amarya.

    Gwamnan Jigawa Umar Namadi na daga cikin waɗanda suka harlaci daurin auren.


    [ad_2]

    Source link

  • Rashin Shugabanci Nagari Ne Har Yanzu Kananan Yara Ke Mutuwa Saboda Cutar Cizon Sauro

    [ad_1]

    Tsohon shugaban kasa Cif Olusegun Obasanjo ya yi Allah-wadai da ci gaba da mace-macen yara kanana daga cututtukan da za a iya magance su kamar zazzabin cizon sauro, yana mai bayyana hakan a matsayin babbar gazawar shugabanci nagari.

    Obasanjo wanda ya bayyana hakan a ranar Talata a wajen kaddamar da cibiyar kiwon lafiya ta CARE 365 a Abuja, ya ci gaba da cewa, ba za a amince da cewa, har yanzu miliyoyin ‘yan Nijeriya na tafiya mai nisa don samun kiwon lafiya, duk da ‘yancin kai da aka samu shekaru da dama.

    Tsohon shugaban, wanda ya jagoranci kaddamar da cibiyar, ya ce, bayar da kiwon lafiya ba gata ga masu hannu da shuni ko mazauna birni ba ce kawai, hakki ne ga kowane dan Nijeriya.

    Ya yaba da Cibiyar Kiwon Lafiya ta CARE 365 a matsayin “mai canza tsari” wanda za ta iya bayar da damar samun ingantacciyar lafiya kuma mai araha.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Wang Yi Ya Yi Bitar Nasarorin Da Aka Cimma Yayin Taron Kolin SCO Na Tianjin

    [ad_1]

    Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya yi bitar nasarorin da aka cimma yayin taron kolin kungiyar hadin kai ta Shanghai ko SCO na shekarar nan ta 2025 da ya gudana a birnin Tianjin.

    Taron na SCO irin sa mafi girma da aka gudanar tun kafuwar kungiyar a shekarar 2001, ya hallara shugabannin kasashe sama da 20, da jagororin hukumomin kasa da kasa 10.

    Wang, wanda kuma memba ne a hukumar siyasa ta kwamitin kolin JKS, ya ce an amince da kudurorin bunkasa ayyukan SCO tsakanin shekarun 2026 zuwa 2035, wanda za su saita alkiblar bunkasa kungiyar cikin shekaru 10 masu zuwa.

    Yayin taron manema labarai da ya jagoranta tare da babban sakataren kungiyar ta SCO mista Nurlan Yermekbayev, Wang Yi ya ce an fitar da sanarwar taron na bana, mai kunshe da goyon baya ga nasarar da aka cimma, ta kawo karshen yakin duniya na biyu. Kazalika, cikin wata sanarwar ta daban da aka fitar, kungiyar SCO ta bayyana cikakken goyon bayanta ga tsarin cudanyar cinikayya tsakanin mabanbantan sassa.

    Har ila yau, a cewar Wang, yayin taron, an kaddamar da sabbin cibiyoyin SCO guda hudu, wadanda aka dorawa alhakin shawo kan barazanar tsaro da sauran kalubale, da aikin dakile laifukan da ake yi tsakanin iyakokin kasashe daban daban, da kyautata tsaron bayanai, da karfafa hadin gwiwa a fannin dakile yaduwar miyagun kwayoyi.

    Bugu da kari, kasashe membobin kungiyar sun amince da kafa bankin bunkasa harkokin SCO, wanda a cewar Wang, zai yi matukar bunkasa samar da ababen more rayuwa, da raya tattalin arziki da zamantakewar al’ummun kasashe membobin kungiyar.

    Dadin dadawa, kasar Sin ta sha alwashin kafa sabon dandalin hadin gwiwa, da cibiyoyi masu nasaba da makamashi, da samar da ci gaba marar gurbata yanayi, da tattalin arzikin dijital, da kirkire-kirkiren kimiyya da fasaha, da ilimi mai zurfi, da na koyar da sana’o’i da fasahohi. An kuma fitar da tsarin ingiza ci gaba mai inganci, wanda ya kunshi sassa irinsu na makamashi, da masana’antun sarrafa hajoji ba tare da gurbata yanayi ba, da tattalin arzikin dijital, da kirkirarriyar basira ko AI da kirkire-kirkiren fasaha. (Mai fassara: Saminu Alhassan)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Zabarmawa Sun Bayyana Dalilin Bai wa Gwamnan Kebbi Sarautar Garkuwa

    [ad_1]



    Kungiyar Zabarmawa ta Najeriya ta karrama Gwamnan Jihar Kebbi, Dakta Nasir Idris, da sarautar Garkuwan Zabarmawa, saboda gudummawar da ya bayar wajen ci gaban al’umma da tallafa wa ƙungiya.

    Da yake bayyana dalilin bai wa gwamnan sarautar a madadin shugaban ƙungiyar na ƙasa, Sarkin Zabarmawa, Alhaji Bello Zabarmawa, ya ce: “An ba da wannan sarauta ne domin nuna gamsuwa da irin ci gaban da Gwamna Idris ya kawo wa talakawa.

    “Mun tuntubi mutane da yawa kafin a zaɓe shi, kuma kowa ya tabbatar cewa shi ya cancanta.”

    A nasa jawabin, Sarkin Zabarmawa na Jihar Kebbi, wanda kuma shi ne tsohon shugaban majalisar dokokin jihar, Abdulmuminu Kamba, ya yaba da irin goyon bayan da gwamnan ke bai wa ƙungiyar da kuma al’ummar jihar.

    Shi ma Gwamna Idris, bayan godewa ƙungiyar, ya bayyana cewa wannan karramawar za ta ƙara masa kwarin gwiwa.

    “Na yi alƙawari gwamnatina ta talakawa ce. Zan ci gaba da yin iya ƙoƙarina wajen tallafa wa mutanen Jihar Kebbi da kuma kare martabar wannan sarauta da aka damƙa min,” in ji shi.

    Kabilar Zabarmawa, wadda aka fi sani da Zabarmawa ko Zabaruma, na daga cikin manyan ƙabilu a Najeriya da Jamhuriyar Nijar, inda suka shahara wajen kasuwanci da jajircewa a fannin neman arziki.


    [ad_2]

    Source link

  • Cibiyar Ayyukan Daular Usmaniyya za ta karrama Sarkin Zazzau

    [ad_1]



    Cibiyar Ayyukan Daular Usmaniyya da ke Sakkwato ta bayyana aniyar karrama Mai Martaba Sarkin Zazzau, Malam Ahmed Nuhu Bamalli CFR, da lambar yabo ta musamman saboda rawar da ta ce yana takawa wajen ƙarfafa haɗin kai da raya zumunci tsakanin ’ya’yan Daular Usmaniyya.

    A cikin sanarwar da cibiyar ta fitar mai ɗauke da sa hannun shugabanta kuma Wazirin Sakkwato, Farfesa Sambo Wali Junaidu, ta ce za a karrama Sarkin tare da wasu fitattun ’yan Najeriya guda shida a babban taron shekara-shekara da cibiyar ke shiryawa.

    Taron zai gudana ne a ranar Alhamis, 11 ga watan Satumba, 2025, a Cibiyar Karatun Alƙur’ani da Addinin Musulunci ta Sultan Muhammadu Maccido da ke Sakkwato.

    Cibiyar ta ce kakan Sarkin Zazzau na yanzu, Malam Musa Kaka, na cikin dakarun da suka taka muhimmiyar rawa a yaƙin Tafkin Kwato, wanda aka fi sani da Muhajiruna wal-Ansar, yaƙin da ya taimaka wajen ginawa da kuma ƙarfafa Daular Usmaniyya.

    Ana sa ran fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Isa Talatan Mafara, zai gabatar da kasida mai taken: “Muhajiruna wal-Ansar: Kafuwar Gidajensu wajen Haɓaka Daular Usmaniyya.”


    [ad_2]

    Source link

  • NSCDC Ta Kama Mutane 6 Da Ake Zargin Barayin Wayoyin Wutar Lantarki Ne A Kano

    [ad_1]

    Jami’an hukumar tsaron farin kaya ta Nijeriya reshen jihar Kano, sun cafke wasu barayi shida da ake zargi da barnatarwa da kuma sace kayan wutar lantarki a unguwar Hayin Da’e da ke Hotoro a karamar hukumar Tarauni ta jihar.

    Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar, Ibrahim Abdullahi ya fitar a ranar Talata.

    Abdullahi ya ce, cafke wadanda ake zargin ya biyo bayan samun sahihan bayanan sirri da ‘yan banga da ke aiki yankin suka samu.

    “Hukumar NSCDC ta kama wadanda ake zargin tare da wayoyin wutar tiransifoma da ake kyautata zaton sato su aka yi a tsakar dare a yankin,” in ji shi




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link