Category: Latest News

  • Sabuwar Ajandar Mulkin Duniya Ta Nuna Alhakin Da Kasar Sin Ta Dauka

    [ad_1]

    Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar da ajandar mulkin duniya a taron “SCO+” na birnin Tianjin a jiya Litinin, kasa da kasa sun mai da hankali sosai ga wannan batu.

    Ajandar, wadda shugaba Xi ya fitar ta kunshi wasu ka’idoji guda biyar, wato tabbatar da daidaiton ikon mulkin kasa, da bin dokokin kasa da kasa, da aiwatar da ra’ayin bangarori daban-daban, da ba da shawarar kula da bukatun jama’a, da kuma mai da hankali kan aiwatar da matakai na samar da wata hanya a fayyace ga kasashen duniya wajen gudanar da ayyuka cikin adalci. Wannan ya shaida cewa, ka’idojin biyar suna shafar tushe, da tabbaci, da hanya, da daraja da kuma muhimman ka’idojin mulkin duniya, wadanda suke daidai da ka’idojin kundin tsarin mulkin MDD, da bin begen yawancin kasashen duniya. Alal misali, ajandar ta jaddada cewa, “Akwai bukatar inganta wakilci da murya tsakanin kasashe masu tasowa,” da shawarar “Kauracewa kakaba ‘dokokin gida’ na wasu kasashe a kan sauran kasashe”, da “nuna rashin amincewa da ra’ayin bangare guda daya” da sauran ra’ayoyi suna nufin yanayin rashin adalci da daidaito kan tsarin siyasa da tattalin arzikin duniya, da kuma samar da hanyar daidaita matsalolin.

    Gabatar da ajandar mulkin duniya ya shaida cewa, Sin ta sa kaimi ga kyautata tsarin mulkin duniya bisa yanayin da ake ciki, da samar da hanya ga dan Adam wajen tinkarar kalubale da shimfida duniya mai zaman lafiya da wadata. A halin yanzu, Sin ta kara samar da gudummawarta wajen daukar alhakinta a matsayin babbar kasa a duniya. (Zainab Zhang)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

    [ad_1]

    Yau kimanin shekaru tamanin ke nan da samun gagarumar nasarar Sin a kan yakinta da maharan kasar Japan da kuma yaki kan mummunar akidar nan ta mulkin danniya, wato fascism a Turance, a fadin duniya. Yunkurin na Japan na afkawa Sin ya faro ne tun shekarar 1931, yayin da maharan na Japan suka afkawa yankin Manchuria, suka fara aiwatar da kisan kare dangi kan fararen hula ba gaira ba dalili. Daga bisani a watan Disamban shekarar 1937, suka kutsa kai a birnin Nanjing, wato babban birnin kasar Sin a wancan lokaci, inda maharan suka hallaka fararen hula da fursunonin yaki sama da dubu 300.

    A bana ce dai kasar ta Sin take bikin cika shekaru 80 da samun nasara a kan maharan Japan da kuma yakin duniya kan akidar nan ta mulkin danniya.

    Shekaru 14 ne sojojin na Sin suka kwashe suna gumurzu da maharan na Japan, inda daga bisani suka samu galaba a kan maharan na Japan.

    Wannan dai shi ne yaki mafi dadewa kuma mafi tsada a tarihin kasar Sin da sojoji suka aiwatar domin ‘yanto da ‘yan kasa.

    Mutane masu hangen nesa da sanin ya kamata ne daga Sin da sauran kasashen duniya suka matsa kaimi da sadaukar da kai ba tare da sanyi a gwiwa ba, suka hada karfi da karfe wajen kawo karshen mummunar akidar nan ta mulkin danniya, abin da ya kawo sauyi mai ma’ana a tarihin karni na 20, tare da bude wani sabon babi na yin watsi da akidar yaki tare da rungumar akidar zaman lafiya.

    Alal hakika, akidar mulkin danniya akida ce wadda take tarnaki ga ci gaba da wayewa ta bil Adam, kuma yaduwar wannan akida barazana ce ga daukacin bil Adam. Don haka yaki da wannan akida ta bazu kamar wutar daji tsakanin sama da kasashe 80 daga nahiyoyin Asia, Turai, Afirka da Oceania. An kuwa tafka asarar rayukan da za su kai sama da miliyan 100, wadanda daga cikinsu sojoji da fararen hula miliyan 35 ne Sin ta yi asara.

    Kasar Sin ta taka muhimmiyar rawa wajen yaki da wannan mummunar akida ta mulkin danniya, yayin da ta shiga cikin sahun sojojin sauran kasashe a yakin duniya na biyu. Kafada da kafada suka yi gumurzu wajen murkushe maharan kasashen Japan, Jamus da Italiya.

    A wannan gabar, za mu fahimci cewa, samun nasarar da Sin ta yi a kan maharan na Japan da kalubalantar akidar mulkin danniya ya amfanawa sauran kasashen da suke da tunani iri daya da Sin na samar da kyakyawar makoma ga al’umma.

    A yau an wayi gari ana samun sauye-sauye cikin hanzari irin wadanda ba a taba gani ba a cikin karni daya. Ana yawan samun barkewar rikici tsakanin yankuna, yayin da kuma kalubaloli a duniya suke ta kara yawaita a kullum. Don haka kamata ya yi a rinka koyon darasi daga tarihi. Ana iya shawo kan irin wadannan matsaloli ta hanyar adalci, daidaito da kuma tsarin yin garambawul a kan manufofin zamantakewa na duniya. (Lawal Mamuda)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Inda Akwai Fata, Akwai Mafita

    [ad_1]

    Ba ni da kokwanto akan cewa, Dauda Lawal na ɗaya daga cikin gwamnonin da suka fi kowa kwarjini a Nijeriya. Amma abu ɗaya da nake yawan samun ƙalubalen bayyana wa mutane shi ne shekarun sa.

    Mutane su kan yi ihun ‘kai!’ wasu kuma su kan kalli idona cikin wasa da dariya su ƙaryata ni. Duk saboda na bayar da sahihin bayanin da na tabbata ɗari bisa ɗari akan cewa Dauda Lawal zai cika 60 a ranar 2 ga Satumba, 2025 (wato yau).

    Wani lokaci, na kan gaji da bayyani. Ko da a ƙarshe sun yarda da shekarun sa, wasu mutane suna cusa musu shakku daga baya. Wasu suna nuna cewa ya bayyana a matsayin matashi kuma yana gyara kan sa ne saboda yana da dukiya.

    Kun tuna jita-jitar ake yaɗawa game wai arzikin sa ya kai Naira Tiriliyan 9? Kuma Mutane da yawa sun gaskata.

    A matsayin sa na gwamnan jihar Zamfara, ina da abubuwa da yawa da zan iya cewa game da Dauda Lawal, musamman da yake ina cikin makusantan sa, mai yin aiki kafaɗa da kafaɗa da shi a matsayin kakakin sa sama da shekaru biyu.

    A shekarun baya na yi rubuce-rubuce da dama a kan Dauda Lawal, ma’aikacin banki kuma mai taimakon al’umma.

    Amma, yayin da ya cika shekara 60 a yau, zan so in fitar da wasu ’yan muhimman abubuwa da Dauda Lawal ya yi a matsayin gwamna, wanda ke mayar da Jihar Zamfara daga kufai da aka manta da ita zuwa babban birnin.

    Dukkan abubuwan da mutane ke faɗi game da shi natsuwa, kamun kia, da tsabta daidai ne. Ya canja ɗabi’ar ma’aikata, musamman waɗanda ke gidan gwamnatin Zamfara, waɗanda ke aiki a kan kujerar mulki. Salon rayuwarsu ta canja, ba kamar da ba.

    Gusau, babban birnin jihar, an gyara ta a matsayin cibiyar birane, kamar yadda ya kamata. An shimfiɗa titi tare da saka fitilu masu haske a ko’ina. Gusau, wacce ba ta da fitilun warware cunkoson ababen hawa a 2023 kafin zabe, yanzu haka tana da fitilun a duk faɗin birnin. Garin ya ƙawatu saboda a hankali ɗabi’un mutane yana canjawa.

    A matsayina na mai fafutukar nuna ma’amala ta ƙwarai, ɗaya daga cikin manyan makarantun tunani na zamantakewar al’umma, na lura da yadda ƙa’idar ‘Kallo Ta Cikin Gilashi’ ta Charles Horton Cooley ke aiwatarwa a tafiyar Gwamna Dauda Lawal a Zamfara. Za ku iya cewa ta ya.

    Kallo Ta Cikin Gilashi ra’ayi ne da ke bayyana yadda mutane ke yin tunanin kansu dangane da yadda suke tunanin wasu na fahimtar su. Ta hanyar hulɗar zamantakewa, mutane suna amfani da maganganun wasu a matsayin “madubi” don tantance ƙimarsu, ɗabi’a, da halayensu.

    A da, abin da mutane ke gani game da Zamfara idan suka kalli madubi, shi ne halin da ake ciki na ƙaƙani-ka-yi, jihar da ’yan bindiga da talauci suka kusa kawar da ita. Ita ce ƙarshe baya da fannin ilimi da kiwon lafiya. Dauda Lawal, masanin kimiyyar siyasa, ya canja wannan labari ta hanyar haɗa ƙa’idojin zamantakewa na aiki da ma’amala mai kyau.

    Jihar Zamfara da mutane ke gani a madubi a yanzu, jiha ce da ke takara a matsayin jiha mafi inganci a fannin tattalin arzikin cikin gida, ilimi, cibiyoyi masu tasowa, kiwon lafiya, da sauransu.

    Aikin ceto na Gwamna Dauda Lawal ya bayyana a dukkan ƙananan hukumomi 14 na jihar Zamfara, ba wai a Gusau, babban birnin jihar kaɗai ba.

    Waɗannan manyan ayyuka sun shafi sassa daban-daban, waɗanda suka haɗa da kiwon lafiya, ilimi, ababen more rayuwa, da sauran muhimman wurare masu.

    Gwamna Lawal ya mayar da Babban Asibitin Anka zuwa wani katafaren asibiti na zamani mai ɗauke da na’urorin kiwon lafiya na zamani a ƙaramar hukumar Anka. An yi wa asibitin gyaran ciki da waje.

    Gwamnatinsa ta kafa makarantar Tsangaya ta zamani a Ƙaramar Hukumar Gummi, makarantar da aka tsara don shigar da Almajirai cikin tsarin ilimi na zamani.

    A ƙaramar hukumar Bakura, Gwamna Lawal ya gyara Kwalejin Kimiyyar Aikin Gona tare da samar mata da kayan aiki, inda ya samar da damarmaki ga matasa don bunƙasa sana’ar su ta noma — ƙashin bayan tattalin arzikin Zamfara.

    A Ƙaramar Hukumar Bukkuyum, ya ɗaukaka darajar PHC Nasarawa Burkullu zuwa babban asibitin zamani da na’urori na zamani domin amfanin al’ummar yankin. Bugu da ƙari, ya bayar da kwangilar gina titunan garin domin haɗa dukkan garuruwan da ke cikin ƙaramar hukumar.

    Gwamna Dauda Lawal ya gyara babban asibitin da ke Ƙaramar Hukumar Maru tare da cikakken kayan aiki. Asibitin, wanda a baya ya yi fata-fata, yanzu an gyara shi yadda ya kamata.

    A Ƙaramar Hukumar Talatar Mafara, Gwamna Dauda Lawal ya ƙaddamar da aikin gina sabon babban asibiti, domin a halin yanzu asibitin ya lalace. Sauran ayyukan a Talata Mafara sun haɗa da gyare-gyare a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Jihar Zamfara.

    A Ƙaramar Hukumar Maradun, Gwamna Lawal ya inganta tare da gyara babban asibitin Maradun, inda ya mayar da shi Cibiyar Kula da Lafiya ta Zamani mai ɗauke da duk wasu kayayyakin jinya na zamani. Ya kuma gyara babban asibitin Maru tare da samar da na’urori na zamani.

    Hakazalika, a ƙaramar hukumar Kauran Namoda, Gwamna Lawal ya gyara babban asibitin Kaura Namoda tare da samar da kayan aiki, ya gina makarantar Tsangaya na zamani, ya kafa cibiyar koyar da sana’o’i da ta dace domin samar da ayyukan yi ga matasa, da kuma gina ƙarin gidajen kwana a Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Kauran Namoda.

    A Ƙaramar Hukumar Shinkafi, Gwamna Lawal ya amince da sake gina babban asibitin Shinkafi da kuma aikin sake gina makarantar Attahiru Bafarawa.

    A Ƙaramar Hukumar Tsafe, Gwamna Dauda Lawal ya gyara babban asibitin Tsafe tare da samar da kayan aiki, ya kuma gudanar da gyaran gaba ɗaya na Makarantar Koyon Fasaha ta Tsafe, ya sake gina babbar tashar mota ta zamani ta Tsafe, da sake gina babbar kasuwa.

    A Ƙaramar Hukumar Bungudu, Gwamna Lawal yana gina titin mahaɗa na Furfuri, titin Rawayya, aikin gyaran makarantar da aka amince da shi gaba ɗaya, da kuma aikin gyara da kayan aiki na makarantar sakandaren Ɗan Gwaggo.

    Ina da abubuwa da yawa da zan faɗa, musamman game da dangantakar mutane da gwamna na. Na yi alƙawari zan yi shi a hankali, ba a lokaci guda ba. Yau rana ce da za a yi bikin mai nasara. Alhamdu lillah, barka da cika shekaru 60 ga mutum mai kyakkyawar zuciya.

    Barka da Ranar Haihuwa, Oga!

    Sulaiman shi ne kakakin gwamnan jihar Zamfara.

    Fassarar MAHDI MUSA MUHAMMAD




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Sin Ta Taka Rawar Gani Sosai Wajen Cimma Nasarar Yakin Duniya Na Biyu

    [ad_1]

    Babban sakataren MDD António Guterres, wanda ya halarci taron kolin kungiyar hadin gwiwar Shanghai wato SCO da aka gudanar a birnin Tianjin dake kasar Sin, ya bayyana cewa, Sin ta taka rawar gani sosai wajen cimma nasarar yakin duniya na biyu. Kuma gudummawar da Sin ta bayar ita ce mabudin nasarar da kawancen kasashen duniya suka samu a yakin duniya na biyu.

    Bugu da kari, Guterres ya jaddada ta hanyar nuna batutuwan tarihi cewa, babbar mamayar da Japan ta yi wa Sin ita ce farkon yakin duniya na biyu na gaskiya. Guterres ya yi imanin cewa, tsayin daka da kasar Sin ta yi wajen yin tir da hare-haren Japan, ya taka muhimmiyar rawa a tsawon shekaru da dama, tare da ba da muhimmiyar gudummawar raunana Japan, kuma a karshe hakan ya kai ga murkushe Japan a karshen yakin duniya na biyu. (Safiyah Ma)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Gwamna Yusuf Zai Kaddamar Da Majalisar Shurah Ta Jihar Kano

    [ad_1]

    A ranar Litinin 8 ga Satumba, 2025 ne gwamnatin jihar Kano za ta kaddamar da sabuwar majalisar Shurah, karkashin jagorancin gwamna Abba Kabiru Yusuf. Za a gudanar da bikin kaddamarwar ne a gidan gwamnati dake Kano.

    Hakan na kunshe ne acikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida na jihar, Ibrahim Abdullahi Waiya ya fitar a 2 ga Satumba, 2025.

    Kafa majalisar Shurah na zuwa ne domin karfafa gudanar da mulki cikin hadin kai, da bayyana gaskiya wajen yanke shawara.

    Ana sa ran majalisar za ta kasance kamar wata kungiya mai ba da shawara ga Gwamnatin Jihar, domin aiwatar da manufofi da shirye-shiryen da za su kawo sauyi da kuma bunkasa ci gaba mai dorewa a jihar.

    Majalisar Shurah ta kunshi manyan mutane masu kima da daraja sosai, da suka fito daga mazabu daban-daban da nufin tabbatar da daidaito da wadataccen wakilci a dukkan bangarori na zamantakewar al’ummar Kano.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Tinubu ya dawo da shugaban NTA da aka sauke

    [ad_1]



    Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin mayar da tsohon Shugaban Gidan Talbijin na Nijeriya, NTA da aka sauke kwanan nan, Salihu Abdullahi Dembos.

    A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban ƙasar Bayo Onanuga ya fitar, ya ce Dembos wanda Shugaba Tinubu ya naɗa a watan Oktoban 2023, a yanzu zai dawo domin kammala wa’adin mulkinsa na shekara uku.

    Haka ma shugaban ƙasar ya bayar da umarnin maido da Mista Ayo Adewuyi a matsayin babban daraktan sashen labarai na NTA, domin shi ma ya ƙarasa wa’adinsa na shekara uku da zai ƙare a 2027.

    A ’yan kwanakin nan ne aka sanar da sauke Dembos sakamakon wasu sauye-sauye da aka gudanar da hukumar.

    Sauke shi dai ya janyo zazzafar muharawa da suka musamman daga yankin arewacin ƙasar, inda Salihu Abdullahi Dembos ya fito.


    [ad_2]

    Source link

  • Alakar Sin Da Rasha Ta Zama Misali Na Kyakkyawar Dangantakar Manyan Kasashe

    [ad_1]

    Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ce alakar Sin da Rasha ta zama misali na kyakkyawar dangantaka tsakanin manyan kasashe, wadda ke kunshe da ingantaccen yanayin kawance na makwafta, da cikakken salon tafiya tare bisa manyan tsare-tsare, da hadin gwiwar cimma moriyar juna. Shugaba Xi ya bayyana hakan ne a Talatar nan, yayin zantawarsa da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin a birnin Beijing.

    A nasa tsokacin kuwa, shugaba Putin ya ce shawarar da shugaba Xi ya gabatar game da tsarin shugabancin duniya ta zo a lokacin da ake matukar bukatarta, kuma wajibi ne a yi aiki da ita, kana za ta taka muhimmiyar rawa wajen magance gibin dake akwai a tsarin shugabancin duniya.

    Ya ce a nata bangare, Rasha a shirye take ta ci gaba da raya hadin gwiwa da bangaren Sin bisa manyan tsare-tsare, da wanzar da musaya bisa matsayin koli, da karfafa hadin gwiwar zahiri da Sin a mabanbantan sassa, da yayata ci gaban alakar sassan biyu bisa matsayin koli.

    Sassan biyu dai sun sanya hannu kan yarjeniyoyin hadin gwiwa sama da 20 a bangarorin da suka hada da na makamashi, da sufurin sama, da AI, da noma, da lura da kare bazuwar cututtuka. Sauran sun hada da fannin kiwon lafiya, da binciken kimiyya, da ilimi da watsa labarai. (Mai fassara: Saminu Alhassan)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • ’Yan bindiga sun sace basarake a Kogi

    [ad_1]



    Wasu ’yan bindiga da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace Hakimin Bagaji Odo a Karamar Hukumar Omala ta Jihar Kogi, David Wada.

    Rahotanni sun ce basaraken ya faɗa tarkon ’yan bindigar ne a ƙauyen Ojuwo Ugweche da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar Litinin, yayin da yake dawowa daga taron sarakunan gargajiya a Abejukolo, hedikwatar ƙaramar hukumar.

    Wani mazaunin yankin, Maji Ahiaba, ya bayyana cewa a ’yan kwanakin nan ƙauyen Ojuwo Ugweche na fuskantar hare-haren masu ta’adar garkuwa da mutane, duk da cewa a baya an taɓa tura jami’an tsaro da ’yan sa-kai domin daƙile ayyukan miyagun.

    Sai dai a cewar mazaunin a wannan karo da abun ya faru, babu jami’in tsaro ko guda a yankin.

    Shugaban majalisar sarakunan gargajiya na ƙaramar hukumar, Sarkin Ife, Mai Martaba Boniface Musa, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya roƙi jami’an tsaro su bi sahun masu garkuwar domin ceto basaraken da aka sace.

    Kakakin rundunar ’yan sanda ta Jihar Kogi, SP Williams Aya, ya ce tuni an tura jami’an tsaro, mafarauta da kuma ’yan sa-kai domin su tsefe dajin da ake zargin an kai sarkin da zummar ceto shi cikin aminci.

    Sai dai har yanzu iyalai da kuma al’ummar yankin na cikin fargaba, la’akari da cewa tun bayan sace basaraken babu wanda masu garkuwar suka tuntuɓa.

    A bara ne wani rikicin ƙabilanci da ya ɓarke a Bagana, Bagaji, Agojeju Odo da Ajokpachi Odo ya bai wa ’yan bindiga damar kashe ɗaruruwan mutane a yankin, lamarin da aka samu aminci bayan Gwamna Usman Ahmed Odo ya tura sojoji da jami’an tsaro.


    [ad_2]

    Source link

  • Xi Jinping Ya Jagoranci Taro Karo Na Bakwai Tsakanin Shugabannin Kasashen Sin Da Rasha Da Mongoliya

    [ad_1]

    Da safiyar yau Talata, shugaban kasar Sin Xi Jinping, tare da takwarorinsa na Rasha Vladimir Putin, da na kasar Mongoliya Ukhnaagiin Khurelsuh, sun gudanar da taro karo na bakwai na shugabannin kasashen Sin, da Rasha, da Mongoliya a babban dakin taron jama’a dake nan birnin Beijing.

    Xi Jinping ya yi nuni da cewa, a cikin ’yan shekarun nan, a kai a kai an yi ta samun bunkasar hadin gwiwa tsakanin kasashen Sin, da Rasha da Mongoliya, kuma an samu sakamako mai inganci. An yi nasarar aiwatar da ayyukan hadin gwiwa tsakanin kasashen uku, ana kuma ci gaba da samun bunkasar ciniki a tsakanin kasashen uku, kana ana ci gaba da zurfafa hadin gwiwa a fannonin raya tattalin arziki, da cinikayya, da kimiyya da fasaha, da kare muhalli, da kuma raya al’adu. A matsayin wata makwabtaciyar abokantaka, kasar Sin a shirye take ta yi aiki tare da Rasha da Mongoliya wajen tabbatar da ainihin burin hadin gwiwa, da kawar da tsoma baki daga waje, da kuma sa kaimi ga bunkasar hadin gwiwa tsakanin kasashen uku.

    A nasa tsokaci, shugaba Putin ya bayyana cewa, kasar Rasha tana son yin hadin gwiwa bisa manyan tsare-tsare tare da Sin, da Mongoliya a nan gaba, bisa daidaito da cimma moriyar juna, ta yadda za a sanya hadin gwiwar bangarorin uku da hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu su dace da juna, kana kuma su habaka juna.

    Shi kuwa shugaba Khurelsuh cewa ya yi, bana shekara ce ta cika shekaru 80 da samun nasarar yakin kin hare-haren sojojin Japan da kasar Sin ya gudanar, da babban yakin kishin kasa na Tarayyar Soviet. Don haka ya kamata al’ummomin Mongoliya, Sin, da Rasha su yi murna, da kuma tunawa da wannan lokaci mai cike da tarihi, da kuma yada madaidaicin ra’ayin tarihin yakin duniya na biyu.

    Bugu da kari, a safiyar yau, shugaba Xi Jinping ya gana da firaministan Pakistan Muhammad Shahbaz Sharif, da shugaban kasar Uzbekistan Shavkat Miromonovich Mirziyoyev a nan birnin Beijing.(Safiyah Ma)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Tinubu Ya Mayar Da Shugabannin NTA Kan Muƙamansu Bayan Dakatar Da Su A Baya

    [ad_1]

    Shugaba Bola Tinubu ya bayar da umarnin a dawo da babban daraktan gidan talabijin na Nijeriya (NTA), Salihu Abdullahi Dembos, wanda aka dakatar bayan wasu sauye-sauye da aka samu a shugabancin gidan.

    Shugaba Tinubu ne ya nada Dembos a matsayin babban darakta na gidan talabijin a watan Oktoban 2023.

    Amma a yanzu zai dawo ya kammala wa’adinsa na ragowar shekaru uku.

    A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga ya fitar, shugaban ya kuma umarci da a maido da babban daraktan yada labarai, Mista Ayo Adewuyi ya kammala wa’adinsa na ragowar shekaru uku, wanda zai kare a shekarar 2027.

    Shugaba Tinubu ne ya nada Adewuyi a shekarar 2024.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link