Category: Latest News

  • Daga Ra’ayin Sin Zuwa Matsayin Da Kasa Da Kasa Suka Cimma

    [ad_1]

    A ranar 20 ga watan Yulin bana, an gano gawarwaki 85 a gefen buhunan abinci masu dauke da tambarin MDD, wadanda suka hada da mata da yara. Wasu na ci gaba da rike buhunan abinci lokacin da aka same su, yayin da wasu yaran ke cikin yanayi na nuna galabaita kafin mutuwarsu.

    Wannan shi ne mummunan sakamakon harin sama da Isra’ila ta kai a wani wurin rarraba kayan agaji a zirin Gaza. Abun takaici shi ne, ba wannan ne karon farko da aka samu irin wannan abun ba. Wani rahoton MDD ya nuna cewa, mutum guda na mutuwa a duk minti uku a fagen yaki a fadin duniya. Mutanen da suka rasa rayukansu sakamakon yaki, su ne mafi daukar hankali a cikin alakar zaman lafiya da ci gaba.

    Yayin da ake rasa zaman lafiya, rayuwar dan Adam na zama mai matukar wahala, balle ma batun samar da ci gaba. Lokacin da ake cika shekaru 80 da samun nasarar yakin duniya na biyu a halin yanzu, manufar samar da ci gaba cikin lumana ta kasar Sin, ta amsa tambaya game da tsarin kiyaye zaman lafiya da samun ci gaba tare, bisa wayewar kanta mai zurfi, da hanyar samun ci gaba mai amfani, da kuma ra’ayinta na kula da kasa da kasa. (Safiyah Ma)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Gwamna Dauda Lawal Zai Yi Jawabi A Taron Kasuwanci Na AFSNET Karo Na Biyar A Ƙasar Algeria

    [ad_1]

    Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, zai yi jawabi a wani taro na habaka kasuwanci karo na biyar wanda AFSNET ke shiryawa.

    Taron zai gudana daga ranar 4 zuwa 10 ga watan Satumba na shekarar 2025, a Cibiyar Habaka Kasuwanci (SAFEX) ta ƙasar Algeria.

    Wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta bayyana cewa an gayyaci Gwamna Lawal don yayi jawabi taron na AfSNET karo na biyar a ranar 6 ga watan Satumba na 2025.

    Sanarwar ta kuma ƙara da cewa, taron zai gudana ne a gefen bikin baje kolin kasuwanci tsakanin ƙasashen Afirka karo na huɗu (IATF2025).

    “Jamhuriyar Dimokaraɗiyyar Aljeriya za ta ɗauki nauyin gudanar da bikin baje kolin kasuwanci tsakanin Afirka (IATF2025) sannan kuma bankin Afreximbank tare da haɗin gwiwar Hukumar Tarayyar Afirka (AUC) da Sakatariyar Yankin Kasuwancin Nahiyar Afirka (AfCFTA) za ta shirya shi.

    “Bikin baje kolin kasuwanci tsakanin Afirka (IATF2025) zai samar da wani tsari na musamman kuma mai ƙima ga ‘yan kasuwa don samun kasuwa guda ɗaya ta Afirka ga sama da mutane biliyan 1.4 tare da habaka tattalin arzikin cikin gida na sama da dalar Amurka tiriliyan 3.5 da aka samar a ƙarƙashin yankin ciniki cikin ‘yanci na Nahiyar Afrika.

    Taken taron na bana shi ne; ‘Ƙarfin Cikin Gida, Tasirin Duniya: Ƙarfafa gwamnatocin ƙasashen Afirka masu cikakken iko don samun ci gaba mai ɗorewa, yana nuna haɗin gwiwarmu don ba da damar gudanar da mulki na cikin gida don samun sakamako mai kyau na nahiyar.

    “Sakamakon nasarar taron AfSNET karo na huɗu da aka gudanar a Kisumu na ƙasar Kenya, wanda ya tara gwamnoni sama da 45, magadan gari, shugabannin ƙananan hukumomi, masu zuba jari, da kuma abokan ci gaba daga ko’ina a nahiyar Afirka, taron na AfSNET ya jaddada muhimman dabaru na ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa wajen inganta kasuwanci cikin ‘yanci na nahiyar Afrika (AfCFTA).

    “Taron ya gabatar da manyan tattaunawa, zaman zurfafa zuba jari, da hada-hadar B2B da B2G, wanda ya baiwa ‘yan ƙasashe damar gabatar da shirye-shiryen ci gaba da kuma gano hanyoyin samar da kuɗaɗe.

    “Tare da mai da hankali sosai kan ci gaba da haɗin gwiwar yanki, taron na Kisumu ya kasance wani muhimmin dandali na tattara albarkatu da ƙarfafa haɗin gwiwa, da tsara hanyoyin da za a iya aiwatarwa da ajandar kasuwanci da ci gaban Afirka daga tushe.”

    “An gayyaci Gwamna Lawal don yayi jawabi akan muhimmin abu cikin tattaunawar da za’ayi lura da ƙwarewar sa akan tattalin arziƙi da shugabanci.”




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Tinubu Ya Naɗa Shugabannin Jami’o’in Ilimi Na Tarayya Da Ke Zariya Da Kano

    [ad_1]

    Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya amince da naɗin Farfesa Yahaya Isa Bunkure a matsayin sabon Shugaban Jami’ar Ilimi Ta Tarayya da ke Zariya (FUEZ), Jihar Kaduna.

    Farfesa Bunkure, fitaccen masani ne a fannin koyar da kimiyya, kuma shi ne yake rike da muƙamin Shugaban Jami’ar Ilimi ta Sa’adatu Rimi da ke Kano a halin yanzu. Sanarwar naɗinsa ta fito ne a ranar Laraba daga mai bai wa shugaban kasa shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai, Bayo Onanuga.

    Jami’ar Tarayya ta Ilimi, Zariya, na daya daga cikin tsofaffin Kwalejojin Ilimi na Tarayya guda huɗu da aka ɗaukaka zuwa matsayin cikakkun jami’o’i a tsakanin shekarar 2022 zuwa 2023. A bisa ga dokokin da suka shafi jagorancin jami’o’i, shugaban jami’a zai yi wa’adin shekaru biyar.

    A wani labarin kuma, Shugaba Tinubu ya amince da naɗin wasu muƙamai a fannin ilimi, inda ya naɗa Injiniya Abdurrazaq Abubakar Nakore a matsayin Shugaban Majalisar Gudanarwa na Jami’ar Ilimi ta Tarayya Yusuf Maitama Sule da ke Kano. Har ila yau, ya naɗa Farfesa Abdullahi Tukur Kodage a matsayin sabon shugaban jami’ar.

    Nakore, memba ne na ƙungiyar Injiniyoyin Nijeriya (NSE), kuma ya taɓa rike muƙamin Sakataren Zartarwa na Hukumar Wutar Lantarki a karkara a Jihar Jigawa. Farfesa Kodage kuwa, kwararre ne a fannin ilimi da yake da gogewa a harkar koyarwa da al’amuran gudanarwa.

    Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa waɗannan naɗe-naɗen na daga cikin ƙoƙarin da gwamnati take yi domin ƙarfafa shugabanci a tsarin ilimi da kuma tabbatar da ingantaccen tsarin tafiyar da sababbin jami’o’in da aka ɗaukaka.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Za a koma rubuta jarabawar WAEC a komfuta

    [ad_1]



    Gwamnatin Nijeriya ta bayyana goyon bayanta kan shirin mayar da rubuta Jarabawar Kammala Sakandare ta Yammacin Afirka (WAEC) da komfuta wato CBT daga shekarar 2026.

    Wannan babban sauyin, wanda aka tsara cewa zai fara aiki a shekarar 2026 ya jawo mabambantan ra’ayoyi a tsakanin masu ruwa da tsaki a fannin ilimi.

    Da yake jawabi a gaban Majalisar Dokoki da manyan masu ruwa da tsaki a wani taron wayar da kai a Abuja, Ministan Ilimi, Tunji Alausa ya ce jarabawa ta tsarin CBT da za a dinga yi a duk faɗin ƙasar, zai ƙarfafa tsarin ilimin ƙasar.

    Alausa ya ce Gwamnatin Tarayya tana goyon bayan rubuta jarabawar WAEC ta komfuta saboda a kawar da satar amsa da kuma tabbatar da an yi sahihiyar jarabawa.

    “Mun ɗau aniyar mayar da rubuta jarabawa ta tsarin fasahar komfuta a matsayin wani mataki na samar wa fannin ilimi martaba.

    “An yi wannan tsari na rubuta jarabawa ta komfuta saboda a rage satar amsa da kare martabar jarabawowinmu. Hakan zai ƙarfafa darajar jarabawowinmu a cikin gida da ma ƙasashen waje.

    Ministan ya ƙara da cewa, duk da cewa wasu sun nuna adawa a farko, amma gwamnati tana ganin ya wajaba a dakatar da dogato tsohon tsarin da aka saba na takarda da biro.

    A nasa bangaren, Shugaban Ofishin WAEC na Ƙasa, Amos Dangut ya ce an samu nasara a wannan sabon sauyin wanda aka fara gwajinsa a kan ɗalibai masu rubuta jarabawar WAEC ta kuɗi mai zaman kanta a shekarar 2024, kuma za a ƙara bunƙasa shi a faɗin kasar.

    Dangut ya bayyana cewa, za a ɓullo da tsarin yin gwaji da koya wa ɗalibai yadda tsarin yake don taimaka musu wajen fahimtarsa sosai, yana mai jaddada cewa babu wani dalibi da za a bari baya.

    Dangane da abubuwan da suka shafi samar da kayan aiki da matsalolin intanet, ya tabbatar wa masu ruwa da tsaki cewa WAEC ta yi nasarar gudanar da jarabawar a wuraren da ke da wahalar isa ba tare da an samu cikas ba.

    Ya ƙara da cewa zuwa yanzu sakamakon ɗaliban da suka rubuta jarabawar gwajin ta komfuta ya yi kyau sosai fiye da jarabawar takarda da aka saba rubutawa.


    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnoni Sun Yi Kira Ga Tinubu Kan Ci Gaba Da Hako Mai A Kolmani Da Tafkin Chadi

    [ad_1]

    Gwamnonin Arewa-maso-Gabas sun bukaci shugaban kasa Bola Tinubu da ya ba da fifiko kan sake dawo da ayyukan hakar mai a rijiyoyin Kolmani da tafkin Chadi a wani bangare na kokarin farfado da tattalin arzikin yankin da kuma rage rashin tsaro.

    Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, wanda ya yi magana a madadin takwarorinsa a ziyarar da suka kai wa shugaban kasa a fadarsa da ke Abuja a ranar Laraba, ya ce, ci gaba da hako man a rijiyoyin zai sake taimaka wa ayyukan soji da kuma habaka ci gaban yankin.

    Zulum ya yaba wa Tinubu kan yadda ya ci gaba da yaki da ta’addanci da kuma yadda ya taimaka wajen dakile illolin ambaliyar ruwa da kwararowar hamada da sauran kalubalen muhalli, inda ya ce yankin ya sha fama da koma bayan muhalli.

    Gwamnonin, a yayin da suke karin haske kan manufofin sabunta fata na shugaban kasa kan samar da abinci da cewa, ya kamata a bayar da kulawa ta musamman ga dazuzzukan da ba bu dan adam, sahara, kwazazzabai da koguna da suka zama maboyar ‘yan tada kayar baya.

    Dangane da batun tsaro, gwamnonin sun bukaci a ci gaba da gudanar da ayyukan soji a wuraren da suka hada da gabar tafkin Chadi, Dajin Madama, tsaunin Mandara, dajin Sambisa, yankunan Mansur, Yelwa, Futuk, Kolmani, dajin Karin Lamido da sauran wurare a yankin Arewa maso Gabas.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Lookman Da Dessers Sun Isa Sansanin Super Eagles A Uyo

    [ad_1]

    Tawagar Super Eagles ta yi maraba da hazikan yan wasanta biyu Ademola Lookman da Cyriel Dessers a sansaninsu na atisaye da ke Uyo babban birnin jihar Akwa Ibom, gabanin fafatawar da za su yi a rukunin C a wasannin neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya ta FIFA na shekarar 2026 da kasashen Rwanda da Afirka ta Kudu.

    Jami’in yada labarai na tawagar Super Eagles, Promise Efoghe ne ya sanar da zuwan yan wasan sansanin a ranar Laraba da yamma, a cewar Efoghe, a halin yanzu yan wasa 18 ne suka iso zuwa sansanin, inda ake sa ran karin yan wasa biyar za su shiga sahun nan gaba kadan wasannin.

    Kwananan, Dessers ya kammala canza sheka zuwa kungiyar Rangers ta kasar Scotland daga Panathinaikos ta kasar Girka, hakazaika Lookman zai ci gaba da zama tare da Atalanta, saboda yunkurinsa na komawa Inter Milan bai yiwu ba, duk da rade-radin da ake yi na alakanta shi da zakarun Jamus Bayern Munich.

    Super Eagles na shirin buga wasannin neman gurbin kofin Duniya, inda za su karbi bakuncin Rwanda a Uyo a ranar Asabar 6 ga watan Satumba, kafin su kara da Afirka ta Kudu bayan kwanaki uku, daga cikin yan wasan da ke sansanin a halin yanzu sun hada da Kyaftin Troost Ekong, Alex Iwobi, Wilfred Ndidi, da Moses Simon, sauran sune, Calvin Bassey, Fisayo Dele-Bashiru da Ola Aina da Bright Osayi.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • An kama wata uwa kan binne jaririyarta a Kebbi

    [ad_1]



    ’Yan sanda a Jihar Kebbi sun kama wata matashiya mai shekara 20, Maryam Atiku, bisa zargin binne jaririyar da ta haifa da ranta a unguwar Nasarawa da ke Kamba a Karamar Hukumar Dandi.

    Hakan na kunshe cikin wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, CSP Nafi’u Abubakar, ya fitar a wannan Larabar.

    Ya ce matashiyar bayan ta haifi jaririyar, ta naɗe ta a cikin wasu zannuwan atamfa guda uku, sannan ta kai ta wani daji da ake kira Malam Yaro a yankin Nasarawa, inda ta tono rami ta binne ta da ranta.

    Sai dai a cewar kakakin ’yan sandan, wani manomi mai suna Alhaji Kabiru Muhammad da ya fita aiki a gonarsa da ke kusa da Malam Yaro, ya lura da alamun an tona wani wuri da ya yi kama da ɗan ƙaramin kabari.

    Hakan ce ta sanya manomin ya yi kururuwar neman a kawo masa agaji, inda mutane suka taru aka taimaka har aka tono jaririyar da ranta.

    Aminiya ta ruwaito cewa an dai garzaya da jaririyar Asibitin Gwamnati na Kamba, inda aka duba lafiyarta aka tabbatar tana cikin ƙoshin lafiya.

    Sanarwar ta ce tawagar ’yan sanda daga sashen binciken manyan laifuka na SCID da ke Birnin Kebbi, ta kama matar nan take, kuma ana titsiye ta a yayin bincike ta amsa laifin, wanda babu wata-wata aka gurfanar da ita a kotu.

    Kwamishinan ’yan sanda na jihar, CP Bello M. Sani, ya yaba wa matar gwamnan Kebbi, Hajiya Zainab Nasare Nasir Idris, bisa alawashin da ta sha na ɗaukar nauyin kula da jaririyar.

    Haka kuma, ya gode wa manomin, Alhaji Kabiru Muhammad bisa irin rawar da ya taka wajen ceto jaririyar.


    [ad_2]

    Source link

  • Yadda Sinawa Ke Girmama Tarihi Da Kiyaye Labarun Abubuwan Da Suka Faru Da Su Na Da Matukar Burgewa

    [ad_1]

    Firaministan kasar Senegal Ousmane Sonko ya bayyana a wata hira da ya yi da wakilin rukunin gidajen rediyo da talabijin na kasar Sin (CMG) a kwanan baya cewa, yadda jama’ar kasar Sin suke mutunta tarihi da kiyaye bayar da labarun abubuwan da suka faru da su ya yi matukar burge shi.

    Sonko ya ce, duk kasar da ba ta iya tuna abubuwan da suka faru da ita a tarihi za ta yi matukar wahala ta dauki darasi daga abin da ya gabata, kuma tana iya saurin maimaita kura-kurai da kuma shan wuyar tashin hankalin da aka shiga a tarihi. Abin da ya yi matukar ba shi mamaki shi ne yadda jama’ar kasar Sin suke mutunta tarihi da kiyaye labarun abubuwan da suka faru da su. Wannan girmamawa da ci gaba da raya tarihi su ne ainihin ginshikin tabbatar da cewa ana gadar wa zuriyoyi da wannan haske.

    Sonko ya ce, al’ummar kasar Sin sun tuna da tarihinsu, wanda hakan ya sa ya zama sinadarin hadin kan kabilu, kuma wani muhimmin karfi da ke kara zaburar da jama’ar kasar Sin su kai ga kokarin bunkasa kasarsu, kana ya ce, hakika wannan yana da matukar muhimmanci. (Abdulrazaq Yahuza Jere)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Hatsarin kwale-kwale ya yi ajalin mutum 29 a Neja

    [ad_1]



    Aƙalla mutum 29 sun rasu a wani hatsarin kwale-kwale da ya auku a gabar kogin Malale da ke cikin Karamar Hukumar Borgu a Jihar Neja.

    Aminiya ta ruwaito cewa, kwale-kwalen wanda ke ɗauke da fasinjoji 90, ya tashi ne daga Tugan Sule da ke yankin Shagunu, inda ya nufi Dugga domin zuwa wata ta’aziyya.

    Majiyoyi sun bayyana cewa cikin waɗanda suka mutu har da mata da ƙananan yara, kuma zuwa yanzu an gano gawarwaki 29, yayin da aka ceto mutum 50 da ransu, sai kuma wasu mutum biyu da har yanzu ake ta ƙoƙarin lalubo su.

    Daraktan Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, wanda Aminiya ta tuntuba ya tabbatar da aukuwar lamarin.

    Haka kuma, wani babban jami’in Hukumar Kula da Hanyoyin Ruwa na Ƙasa (NIWA) a yankin, Akapo Adeboye, ya tabbatar da hakan ta wayar tarho.

    A cewar Daraktan NSEMA: “Mun samu rahoton hatsarin kwale-kwale a wani gari mai suna Gausawa da ke yankin Malale a Borgu.

    “Bisa bayanan da muka samu, kwale-kwalen ya tashi daga Tugan Sule da ke cikin gundumar Shagunu wanda yake ɗauke da mutum 90 ciki har da mata da yara, da nufin zuwa gaisuwar rasuwa a Dugga.

    “Wannan lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11:30 na safiyar ranar Talata, 2 ga Satumba, 2025, a sanadiyar lodin fasinjoji fiye da ƙima sannan kuma kwale-kwalen ya ci karo wani da kututturen itace.”

    Ya ƙara da cewa jami’ai na ci gaba da aikin ceto domin gano waɗanda suka bace.


    [ad_2]

    Source link

  • Mutane 29 Sun Rasa Rayukansu A Wani Hatsarin Jirgin Ruwa A Jihar Neja

    [ad_1]

    Wani sabon hatsarin jirgin ruwa da ya auku a ƙaramar hukumar Borgu ta Jihar Neja ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 29, yayin da mutane biyu suka ɓata, an kuma ceto wasu mutane 50 da rai.

    Binciken jaridar LEADERSHIP HAUSA ya gano cewa hatsarin ya faru ne a yankin Gausawa na Malale, inda jirgin ruwan yake ɗauke da mutane 90 a lokacin hatsarin.

    An bayyana cewa jirgin ruwan ya tashi ne daga kauyen Tugan Sule da ke gundumar Shagunu, inda mafi yawan fasinjojin mata da yara ne, suna kan hanyarsu zuwa Dugga domin kai gaisuwar ta’aziyya.

    Wani da abin ya faru a gabansa ya shaida cewa jirgin ya cika makil da fasinjoji tun daga lokacin da ya bar Tunga Sule, amma matsalar ta fara faruwa a lokacin da suka kai Gausawa, inda jirgin ya kife nan take.

    Shugaban hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da faruwar lamarin.

    “Mun karɓi rahoton hatsarin jirgin ruwa a wani ƙauye mai suna Gausawa da ke yankin Malale a ƙaramar hukumar Borgu,” a cewarsa

    Ya ce, “Bisa rahoton jami’inmu na ‘search and rescue’, jirgin ya tashi daga Tugan Sule da ke gundumar Shagunu dauke da mutane 90, ciki har da mata da yara, suna tafiya Dugga domin gaisuwar ta’aziyya.”

    Ya bayyana cewa hatsarin ya faru ne a sakamakon yawan fasinjoji fiye da ƙima da kuma bugu da katako da ke karkashin ruwa, tare da cewa babu wani daga cikin fasinjojin da ke sanye da rigar kariya (life jacket), duk da umarnin gwamnati game da amfani da ita a jihar.

    Arah ya ce an gano gawarwaki 29, an ceto mutane 50 da rai, yayin da mutane biyu saka ɓace ake ci gaba da neman su.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link