Category: Latest News

  • Buƙatun Gwamnonin Arewa maso Gabas

    [ad_1]



    Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya jagoranci tawagar gwamnonin Arewa maso Gabas zuwa fadar shugaban ƙasa domin ganawa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu a ranar Laraba.

    Ganawar  wanda aka gudanar a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja, ta mayar da hankali ne kan muhimman batutuwan da suka shafi yankin Arewa maso Gabas da suka haɗa da kammala muhimman ayyukan gina hanyoyin mota 17 cikin gaggawa, da kuma ci gaba da haƙo mai a rijiyoyin kan iyaka, musamman ma rijiyoyin Kolmani da tafkin Chadi.

    Sauran gwamnonin da suka halarci ganawar sun haɗa da: Gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, Gwamnan Bauchi, Bala Muhammad da Gwamnan Ypbe, Mai Mala Buni da Gwamnan Adamawa, Ahmadu Umaru Fintiri da kuma Gwamnan Taraba Agbu Keffas.

    Da yake gabatar da jawabinsa a yayin taron ganawar, Gwamnan Zulum wanda kuma shi ne shugaban ƙungiyar gwamnonin Arewa maso Gabas, ya buƙaci shugaban ƙasar da ya kammala ayyukan tituna da kuma gina muhimman hanyoyin da suka haɗa jihohi shida na shiyyar.

    Hanyoyin sun haɗa da: Titin Kano zuwa Maiduguri, titin jirgin ƙasa na Fatakwal-Jos zuwa Bauchi zuwa Maiduguri, da titin Bama zuwa Mubi zuwa Yola, da titin Wukari zuwa Jalingo zuwa Yola, da titin Duguri zuwa Mansur (NNPC project, titin Bauchi zuwa Gombe zuwa Biu zuwa Damaturu da titin Damaturu zuwa Geidam da  titin Gombe zuwa Poli-Geidam, titin Gombe-Poli-Ningi da titin Bauchi zuwa Ningi da titin Bauchi-Ningi sai Damaturu-Biu.

    Sauran sun haɗa da titin Alkaleri zuwa Futuk da titin Maiduguri zuwa Damboa zuwa Yola, da titin Gombe-Dukku-Darazo da titin Biu-Gombe da titin Ibi-Shamdam, titin Maiduguri zuwa Monguno-Baga da titin Maiduguri-Ngala zuwa Bama-Banki.

    Gwamna Zulum ya yaba wa shugaban ƙasa, bisa jajircewar da yake yi na ƙoƙarin maido da zaman lafiya a yankin Arewa maso gabas, inda ya ce, “Mun gode maka da ka samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin da kuma ci gaba da yunƙurin ganin an ci gaba da yaƙi da ’yan tada ƙayar baya.

    Ya kuma tabbatar wa shugaban ƙasar kan ƙudirinsu na ganin gwamnatinsa ta samar da horo na musamman ga ma’aikata don samar da fasahar ƙere-ƙere da nufin magance matsalar rashin tsaro da yankin Arewa maso Gabas ke fuskanta.

    “Muna da cikakkiyar daidaituwa tare da kyakkyawan shiri na shugaban ƙasa na horar da ma’aikata da kuma samar da fasaha da nufin kawar da mummunan halin da ake ciki a cikin dazuzzuka, ta yadda za a rage ta’addanci da kuma inganta ci gaban noma tare da sabunta ajandar samar da abinci,” in ji Zulum.


    [ad_2]

    Source link

  • Matasa sun kashe ’yan bindiga 6 sun sha alwashin kare kansu

    [ad_1]



    Matasan Ƙaramar hukumar Shagari sun kashe wasu ’yan bindiga shidda da ake zargin suna cikin waɗanda suka addabi yankin Ƙaramar hukumar Shagari a Jihar Sakkwato.

    Wani matashi ya yi wa wakilinmu bayanin yadda lamarin ya faru ya ce, ’yan bindigar sun zo kan Jakuna a cikin dajin da ba kowa, a safiyar Alhamis inda  mutane da ke tsare gari ba su watse ba suka gansu a nan ne suka yi masu ƙofar raggo, suna tare da shanun da suka sata da wasu baƙin shanu.

    “An gansu su bakwai an kashe shidda daga cikinsu an bar guda raye aka ɗaure shi,  su shiddan ga su a kwance ba rai, mutane sun yanke hukuncin kare kansu don sun ga gwamnatin Sakkwato ba da gaske take kan lamarin tsaro ba.” A cewarsu

    Shugaban Ƙaramar hukumar Shagari, Alhaji Muhammad Maidawa ya ce da safiyar Alhamis labari ya zo masa akwai wasu baƙin Fulani jajaye da aka afkawa a garin Shagari, amma komai ya lafa sojoji sun kwantar da tarzomar.

    Kan maganar adadin waɗanda aka kashe ya ce har yanzu jami’an tsaro ba su gama tantancewa ba, in sun ƙare za su sanar da shi ya ba da bayani.

    Matasa a ƙarƙashin Ƙungiyar Shagari Youths a Ƙaramar hukumar Shagari ta jihar sun yi barazanar ɗaukar matakin kare kansu sakamakon taɓarɓarewar tsaro a yankin.

    Matasan sun kuma zargi gwamnati da sakaci duk da hare-haren ’yan bindiga da ake ta fama da su tare da ƙorafe-ƙorafen jama’a.

    A cikin wata sanarwa da aka fitar a madadin Ƙungiyar ta hannun Bello Bala Shagari, ya bayyana cewa matasan sun yanke wannan shawara ne a wani taro na intanet da suka gudanar ranar Laraba.

    Ya ce: “Da dama sun bayyana cewa, gwamnati ta gaza wajen cika alhakin kare rayuka da dukiyoyin jama’a. Saboda haka, kare kai yanzu shi ne kaɗai zaɓin da ya rage.”

    Ya ƙara da cewa, matasan sun yanke shawarar ɗaukar duk wani mataki da ya dace domin kare kansu daga cin zarafi da hare-haren ’yan bindiga.

    Sai dai Shagari ya bayyana cewa, ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Yabo/Shagari, Umar Yusuf-Yabo, ya yi kira da a yi haƙuri, a bi doka tare da samun ƙarin shawarwari.

    Duk da ya nuna fahimtar takaicin da matasan ke ciki, ya roƙi gwamnati da ta hanzarta ɗaukar mataki domin daƙile abin da ya ce na iya “rikiɗewa zuwa barazana mai girma.”


    [ad_2]

    Source link

  • Matasa sun kashe ’yan bindiga 6 sun sha alwashin kare kansu a Sakkwato

    [ad_1]



    Matasan Ƙaramar hukumar Shagari sun kashe wasu ’yan bindiga shidda da ake zargin suna cikin waɗanda suka addabi yankin Ƙaramar hukumar Shagari a Jihar Sakkwato.

    Wani matashi ya yi wa wakilinmu bayanin yadda lamarin ya faru ya ce, ’yan bindigar sun zo kan Jakuna a cikin dajin da ba kowa, a safiyar Alhamis inda  mutane da ke tsare gari ba su watse ba suka gansu a nan ne suka yi masu ƙofar raggo, suna tare da shanun da suka sata da wasu baƙin shanu.

    “An gansu su bakwai an kashe shidda daga cikinsu an bar guda raye aka ɗaure shi,  su shiddan ga su a kwance ba rai, mutane sun yanke hukuncin kare kansu don sun ga gwamnatin Sakkwato ba da gaske take kan lamarin tsaro ba.” A cewarsu

    Shugaban Ƙaramar hukumar Shagari, Alhaji Muhammad Maidawa ya ce da safiyar Alhamis labari ya zo masa akwai wasu baƙin Fulani jajaye da aka afkawa a garin Shagari, amma komai ya lafa sojoji sun kwantar da tarzomar.

    Kan maganar adadin waɗanda aka kashe ya ce har yanzu jami’an tsaro ba su gama tantancewa ba, in sun ƙare za su sanar da shi ya ba da bayani.

    Matasa a ƙarƙashin Ƙungiyar Shagari Youths a Ƙaramar hukumar Shagari ta jihar sun yi barazanar ɗaukar matakin kare kansu sakamakon taɓarɓarewar tsaro a yankin.

    Matasan sun kuma zargi gwamnati da sakaci duk da hare-haren ’yan bindiga da ake ta fama da su tare da ƙorafe-ƙorafen jama’a.

    A cikin wata sanarwa da aka fitar a madadin Ƙungiyar ta hannun Bello Bala Shagari, ya bayyana cewa matasan sun yanke wannan shawara ne a wani taro na intanet da suka gudanar ranar Laraba.

    Ya ce: “Da dama sun bayyana cewa, gwamnati ta gaza wajen cika alhakin kare rayuka da dukiyoyin jama’a. Saboda haka, kare kai yanzu shi ne kaɗai zaɓin da ya rage.”

    Ya ƙara da cewa, matasan sun yanke shawarar ɗaukar duk wani mataki da ya dace domin kare kansu daga cin zarafi da hare-haren ’yan bindiga.

    Sai dai Shagari ya bayyana cewa, ɗan majalisar tarayya mai wakiltar Yabo/Shagari, Umar Yusuf-Yabo, ya yi kira da a yi haƙuri, a bi doka tare da samun ƙarin shawarwari.

    Duk da ya nuna fahimtar takaicin da matasan ke ciki, ya roƙi gwamnati da ta hanzarta ɗaukar mataki domin daƙile abin da ya ce na iya “rikiɗewa zuwa barazana mai girma.”


    [ad_2]

    Source link

  • Ƙauyuka 43 A Jihohi 14 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa

    [ad_1]

    Gwamnatin Tarayya ta yi gargaɗi cewa ƙauyuka 43 daga jihohi 14 na iya fuskantar ruwan sama mai yawa da ambaliya daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Satumba, 2025.

    Wannan gargaɗin ya fito ne daga Cibiyar da ke Gargaɗi kan Ambaliyar Ruwa da ke ƙarƙashin Ma’aikatar Muhalli.

    Jihohin da abin zai shafa sun haɗa da Ebonyi, Cross River, Kano, Zamfara, Taraba, Abia, Yobe, Plateau, Borno, Imo, Neja, Sakkwato, Kaduna da Akwa Ibom.

    Ambaliyar ruwa ta riga ta raba mutane da dama da muhallansu a Nijeriya, ta lalata gonaki da gidaje.

    Masana sun ce sauyin yanayi da kuma rashin ingantattun magudanan ruwa ne ke ƙara tsananta matsalar.

    A gefe guda kuma, gwamnatin China ta ba da tallafin dala miliyan ɗaya ($1m) domin taimaka wa waɗanda ambaliyar ta shafa a Arewacin Nijeriya.

    Ministan Tsare-tsare da Tattalin Arziƙi, Abubakar Bagudu, ya ce za a yi amfani da kuɗin yadda ya dace, yayin da Jakadan China a Nijeriya, Yu Dunhai, ya nuna goyon baya da jajensa ga mutanen da abin ya shafa.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

    [ad_1]

    Hakimin Bagaji Odo a gundumar Sanata ta Kogi ta Gabas, HRH David Akpa da aka yi garkuwa da shi ranar Litinin ya shaki iskar ‘yanci.

    Hakan ya fito ne a wata sanarwa mai dauke da sa hannun Gift Idoga, sakataren yada labarai na shugaban karamar hukumar Omala, Hon. Edibo Mark.

    Idoga ya ce kokarin shugaban hukumar, jami’an tsaro, mafarauta da ’yan banga ya samar da sakamako mai kyau tare da ceto basaraken da safiyar Alhamis.

    Ya kuma ce, Hakimin da aka ceto a halin yanzu yana gidan Shugaban Hukumar inda yake jinya.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Damfara A Kano

    [ad_1]

    Rundunar ‘yansandan jihar Kano ta kama wasu mutane uku da ake zargin ‘yan damfara ne da suka damfari wani tsabar kudi har Naira Miliyan N1,030,000 ta hanyar ba saja da jami’an tsaro.

    Wadanda ake zargin sun hada da Nasiru Adamu mai shekaru 30 daga jihar Sokoto; Yusuf Sani, 49; da Aliyu Yusuf dan shekaru 25, dukkansu daga karamar hukumar Daura ta jihar Katsina, an kama su ne a ranar 2 ga Satumba, 2025, da misalin karfe 1:30 na rana a unguwar Dan’agundi ta Kano.

    Kakakin Rundunar, Abdullahi Kiyawa, a cikin wata sanarwa da ya rabawa manema labarai a ranar Alhamis, ya bayyana cewa kamen ya biyo bayan kiran gaggawa daga wanda aka damfara, mai suna, Salisu Ibrahim.

    Kakakin ‘yansandan ya ce, binciken farko da aka yi ya nuna cewa wadanda ake zargin sun bayyana kansu ne a matsayin jami’an tsaro kuma sun yi ikirarin cewa suna da kwarewa ta musamman don taimaka wa wanda aka damfarar.

    Ya kara da cewa wadanda ake zargin sun umurci Ibrahim da ya kawo kudin zuwa wani wuri inda suka yi alkawarin taimaka masa.

    Ya kara da cewa jami’an ‘yansanda tare da hadin gwiwar jama’a sun yi nasarar cafke duk wadanda ake zargin.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Mai taɓin hankali ta haihu a tsakiyar kasuwa a Oyo

    [ad_1]



    Wata mata mai tabin hankali da ba a iya gano danginta ba, ta haihu a bainar jama’a a cikin kasuwar garin Aarinoye a karamar hukumar Itesiwaju ta Jihar Oyo.

    Wata majiya ta shaida wa Aminiya cewa matar ta haihu ne da misalin karfe 5:00;na yammacin ranar Laraba, kuma ta haifi jaririnta namiji lami lafiya ba tare da tallafin unguwar-zoma ba.

    Majiyar ta ce kafin matar ta haihu an saba ganinta daga safiya zuwa daren kowace rana dauke da juna biyu tana yawon tsintar dagwalon abinci da shan gurɓataccen ruwa a cikin bola.

    idan dare ya yi kuma, majiyar ta ce matar takan koma bayan ginin gidan rediyo na BCOS na Oke Ogun, inda take kwana a kasa ba tare da shimfida ko mayafi ba.

    Jim kaɗan bayan haihuwar, mazauna yankin sun hanzarta daukar matakin karbar jaririn daga hannun wannan mata sannan suka mika shi ga babban Jami’in ‘yan sanda (DPO) na yankin.

    A nan take ne jami’in ya nemi wasu mata da suka taimaka wajen tsaftace jikin mai jegon da jaririn nata kamar yadda ake yi wa mata masu jego, sannan aka garzaya da ita zuwa wani asibiti a garin Otu hedkwatar karamar hukumar Itesiwaju domin kula da lafiyarta.

    Rundunar ’Yan sanda a Jihar ta Oyo ta nemi al’ummar wannan yanki na Aarinoye da su taimaka da ingantaccen bayanin da zai kai ga gano dangi ko mijin wannan matar mai tabin hankali.


    [ad_2]

    Source link

  • Hatsarin Jirgin Ruwa: Adadin waɗanda suka rasu ya kai 60 a Neja

    [ad_1]



    Adadin mutanen da suka rasu a hatsarin jirgin ruwa da ya auku a yankin Malale, da ke Ƙaramar Hukumar Borgu a Jihar Neja, ya kai 60.

    Jirgin ruwan, wanda ya ɗauko kusan mutum 90, ya tashi daga Tugan Sule a gundumar Shagunu, kuma yana kan hanyarsa ta zuwa Dugga.

    Mutanen da ke cikin sun tafi yin gaisuwar ta’aziyya ne, lokacin da hatsarin ya auku a ranar Talata, 2 ga watan Satumba, 2025 da misalin ƙarfe 11:30 na safe.

    Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA), ta ce hatsarin ya faru ne akamakon dukan wani itace da ke cikin ruwa.

    Da farko, an gano gawarwakin mutum 29, sannan aka ceto mutum 50, yayin da mutum biyu suka ɓace.

    Sai dai daga baya, shugaban Ƙaramar Hukumar Borgu, Abdullahi Baba Ara, ya tabbatar da cewa adadin mutanen da suka rasu ya ƙaru zuwa 60,

    Hakazalika, ya ce ƙarin wasu mutum 10 na cikin mawuyacin hali, yayin da har yanzu ake neman wasu.

    Dagacin yankin Shagunu, Sa’adu Inuwa Muhammad, ya ce ya je wajen bayan aukuwar hatsarin, inda ya tabbatar da cewa jirgin ya ɗauki mutane sama da 100, waɗanda mafi yawansu mata da yara ne.

    Ya ce an gano gawarwakin mutum 31, kuma an binne huɗu daga cikinsu a ranar Talata.

    A halin yanzu dai, ana ci gaba da ƙoƙarin gano waɗanda suka ɓace.


    [ad_2]

    Source link

  • Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

    [ad_1]

    Rundunar Sojin Sama ta Nijeriya (NAF), ta hanyar sashin haɗin gwuiwa na Operation Haɗin Kai (OPHK), ta kai hare-haren sama da suka hallaka a ƙalla ƴan ta’adda 15 a jihar Borno.

    Kakakin rundunar, Ehimen Ejodame, ya bayyana cewa hare-haren sun gudana ne a ranar Laraba, 3 ga Satumba 2025. Ya ce an kai harin ne kan sabuwar mafakar ƴan ta’adda da aka gano a yammacin garin Zuwa da ke cikin dajin Sambisa.

    A cewar shi, an samu sahihin bayanan sirri da kuma binciken jiragen leƙen asiri kafin a kaddamar da harin, wanda ya yi sanadiyar hallaka ƴan ta’adda da dama ciki har da wasu shugabanninsu tare da rusa gine-ginen da suke amfani da su.

    Sanarwar ta ƙara da cewa nasarar wannan hari ta sake tabbatar da ƙudirin NAF na kare rayuka da dukiyoyin ƴan Nijeriya, tare da tallafawa dakarun ƙasa wajen murƙushe cibiyoyin ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

    [ad_1]

    Rundunar Ƴansandan Jihar Kebbi ta cafke wata mata ƴar shekara 20 wacce ake zargi da haifar jaririya sannan ta binne ta da rai a cikin gonar da ke garin Kamba, Ƙaramar Hukumar Dandi.

    Kakakin rundunar, SP Nafi’u Abubakar, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne a ranar 25 ga Yuni, 2025, inda wacce ake zargin ta ɗaure wuyan jaririyar da zani guda uku tare da rufe bakinta, kafin daga bisani ta binne ta a cikin wani daji da ake kira Malam Yaro da ke Kamba.

    Sai dai wani mai gonar yankin, Alhaji Kabiru Muhammad Kamba, ya gano ramin da aka yi amfani da shi wajen binne jaririyar, inda ya sanar da al’umma kuma aka ceto jaririyar da ranta a ranar 26 ga Yuni. An garzaya da ita zuwa Asibitin Kamba, inda likitoci suka tabbatar da cewa tana cikin ƙoshin lafiya.

    Kwamishinan Ƴansanda na jihar, CP Sani Muhammad Bello, ya yi Allah-wadai da lamarin, yana mai jaddada cewa rundunar ba za ta yi ƙasa a gwuiwa ba wajen yaƙar cin zarafin yara. Ya kuma yi kira ga iyaye da al’umma da su ba da kariya ga ƙananan yara tare da kauce wa aikata irin wannan ta’addanci saboda talauci ko wasu dalilai.

    CP Bello ya yaba wa matar gwamnan jihar, Hajiya Zainab Nasare Nasir Idris, bisa kulawa da taimako da ta nuna wajen ɗaukar nauyin kula da jaririyar. Rundunar ta kuma tabbatar da cewa wacce ake zargi za ta fuskanci shari’a bayan kammala bincike a sashin manyan laifuka.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link