Author: Hausanews

  • An Gudanar Da Ayyukan Share Kaburbura A Fadin Kasar Sin A Rana Ta Biyu Ta Hutun Qingming

    [ad_1]

    Yau Lahadi ce kuma ranar bikin Qingming ta gargajiyar kasar Sin, wato bikin gargajiya na al’ummar Sinawa da ake gudanarwa domin girmama mamata da tunawa da magabata, inda a yau din adadin masu share kaburbura a duk fadin kasar ya yi matukar karuwa fiye da jiya.

    Kamar yadda ma’aikatar harkokin jama’a ta kasar Sin ta bayyana, a yau sassan ba da hidimomin jana’iza kimanin 66,200 sun tallafa wajen bayar da hidimomin share kaburbura, baya ga ma’aikata 446,000 da suka shiga ayyukan ba da tabbaci a fannin. A dai yau din, an karbi masu share kaburbura sama da miliyan 30 a fadin kasar, kuma wannan adadin ya karu da kashi 59 da wani abu cikin dari, idan aka kwatanta da na jiya. Cikin adadin, wadanda suka zabi hanyoyin share kaburbura irin na rage gurbatar iska, kamar amfani da furanni sun kai kusan miliyan 20, wanda ya wuce kashi 63 cikin dari na adadin masu share kaburburan. Har ila yau, dandamali 859 na share kaburbura ta yanar gizo sun ba da hidima ga mutane 353,800.

    Hukumomin lura da harkokin jama’a, da na ba da hidimar jana’iza a wurare daban-daban, sun tabbatar da dukkan matakan ba da hidima sosai, kana sun gudanar da ayyukan saukaka wa jama’a da amfanin jama’a, don jagorantar jama’a wajen zaben hanyoyin share kaburbura irin na rage gurbata iska. (Bilkisu Xin)

    [ad_2]

    Source link

  • David Mark Ya Ƙaryata Jita-jitar Murabus, Ya Ce Ƙarya Ce Tsagwaronta

    [ad_1]

    Jam’iyyar ADC ta yi fatali da rahotannin da ke yawo cewa Shugabanta na ƙasa, Sanata David Mark, ya yi murabus daga muƙaminsa, tana mai bayyana zargin a matsayin ƙarya tsagwaronta da aka ƙirƙira domin jefa ruɗani da rikici a cikin jam’iyyar a wannan lokaci mai muhimmanci na siyasa.

    A cikin wata sanarwa da ofishin yaɗa labarai na shugaban jam’iyyar ya fitar, ADC ta bayyana cewa wannan jita-jita wani “ƙagaggen labari ne maras tushe” da wasu marasa kishi ga ci gaban jam’iyyar ke yaɗawa, tana mai cewa babu wani shiri ko tunani daga David Mark ko shugabannin jam’iyyar na yin murabus daga jagoranci a halin yanzu.

    • 2027: ADC Na Duba Yiwuwar Fitar Da Dan Takarar Shugaban Kasa Ta Hanyar Yarjejeniya — Kakakin Jam’iyya
    • 2027: Obi Da Kwankwaso Za Su Fafata Da Atiku Wajen Neman Takarar Shugaban Kasa A ADC

    Sanarwar ta jaddada cewa Sanata David Mark har yanzu shi ne cikakken shugaban jam’iyyar na ƙasa, tana mai cewa duk wanda ke yaɗa irin waɗannan rahotanni yana ƙoƙarin tayar da tarzoma da kuma raunana haɗin kan jam’iyyar, musamman a daidai lokacin da ake shirin manyan sauye-sauyen siyasa gabanin zaɓen shekarar 2027.

    Haka kuma, jam’iyyar ta bayyana cewa shugabancinta na ci gaba da kasancewa a haɗe, mai ƙarfi da kuma mai himma wajen tabbatar da ingantacciyar dimokuraɗiyya da samar da sahihin jagoranci ga ‘yan Nijeriya, tana mai gargaɗin cewa duk wani yunƙuri na kawo cikas ga tafiyarta zai gamu da turjiya daga mambobinta da masu goyon baya.

    A ƙarshe, ADC ta buƙaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da jita-jitar da ake yaɗawa, tana mai tabbatar da cewa jam’iyyar na nan daram kuma za ta ci gaba da taka muhimmiyar rawa a fagen siyasar ƙasar, tare da aniyar tabbatar da cewa an kare tsarin jam’iyyu da dimokuraɗiyya daga duk wani yunƙuri na rushewa.

    [ad_2]

    Source link

  • ADC ba za ta taɓa lashe zaɓe a Kano ba — Gwamna Abba

    [ad_1]



    Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ce jam’iyyar ADC ba za ta iya lashe zaɓe a jihar ba.

    Ya bayyana haka ne a ranar Lahadi a Fadar Gwamnati da ke Kano, bayan dawowarsa daga tarukan siyasa da aka yi a Abuja da Kaduna.

    Gwamnan, ya ce yana da tabbacin zai sake lashe zaɓe a ƙarƙashin jam’iyyar APC, yana mai cewa gwamnatinsa na ƙoƙarin inganta rayuwar jama’a.

    “Falle ɗaya ne a jam’iyyar NNPP za mu yi, za kuma mu yi falle na biyu a APC. Amma ADC da suka koma, ba za ta samu ko falle ɗaya ba,” in ji shi.

    Abba, ya bayyana ADC da sauran jam’iyyun adawa a matsayin marasa ƙarfi waɗanda ba za su iya samun gagarumar nasara a siyasa ba.

    “Kano da Najeriya gaba ɗaya suna tare da APC… kada mutane su ruɗe da abin da ake kira ADC da sauran jam’iyyu,” in ji shi.

    Ya kuma yi alƙawarin ƙara ƙoƙari idan aka sake zaɓarsa, musamman a fannoni kamar gine-gine, ilimi, lafiya, noma da samar da ruwa.

    “Kun ga irin ƙoƙarinmu a cikin shekaru biyu zuwa uku da suka wuce. Idan kuka sake ba mu dama, za mu ƙara yin fiye da haka,” a cewarsa.

    Gwamnan, ya yaba wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu, kan ƙoƙarinsa na inganta tattalin arziƙi da gina ababen more rayuwa.

    “Shugaban ƙasa yana ƙoƙari… yana aiki domin tabbatar da ci gaba a faɗin ƙasar nan,” in ji shi.

    Haka kuma, Gwamna Abba, ya ce mutanen Kano za su goyi bayan Tinubu a 2027.

    “Mu a Jihar Kano muna tare da Shugaban ƙasa kuma za mu sake zaɓensa a 2027,” in ji shi.


    [ad_2]

    Source link

  • Sin Da Tanzania Sun Karrama Ma’aikatan Da Suka Rasu Yayin Gina Layin Dogo Na TAZARA

    [ad_1]

    Jami’an gwamnatocin Sin da Tanzania, sun karrama gomman ma’aikata Sinawa da suka rasa rayukansu, yayin ginin layin dogo na TAZARA, wanda ya hada kasashen Tanzania da Zambia, a gabar da ake bikin cikar layin dogon shekaru 50 da fara aiki.

    A jiya Asabar, jami’an gwamnatocin kasashen biyu sun halarci makabartar birnin Dar es Salaam, inda aka binne gawawwakin Sinawan da suka sadaukar da rayukansu yayin ginin layin dogon, kana sun aza furanni kan kaburburan mamatan, a wani mataki na tunawa da gudummawarsu da kuma martaba su, albarkacin bikin sharar makabarta na “Qingming”, wato bikin gargajiya na al’ummar Sinawa da ake gudanarwa domin girmama mamata da tunawa da magabata.

    Da yake tsokaci yayin ziyartar makabartar, ministan harkokin cikin gida na Tanzania Patrobas Katambi, ya jinjinawa layin dogon na TAZARA, yana mai bayyana shi a matsayin shaida ta zahiri ta hadin gwiwar kasashe masu tasowa, kana wata alama dake nuni ga juriyar kawancen dake tsakanin Tanzania da Sin. Kazalika, Katambi ya jaddada bukatar kare kima, da zamanantar da layin dogon a matsayin wani bangare na ajandar farfado da shi.

    A nata bangare kuwa, jakadiyar Sin a Tanzania Chen Mingjian, cewa ta yi sama da ma’aikata Sinawa 50,000 ne suka shiga aikin ginin layin dogon da aka gudanar cikin shekarun 1970, inda kuma 70 daga cikinsu suka rasu yayin gudanar da shi.

    Bugu da kari, yayin bikin, babban manajan hukumar sufurin jiragen kasa ta Tanzania da Zambia Bruno Ching’andu, da mataimakin ministan harkokin wajen Tanzania da harkokin hadin gwiwar gabashin Afirka James Kinyasi Millya, sun gode wa kasar Sin, suna masu yabawa kawancen gargajiya dake wakana tsakanin kasashen biyu. (Saminu Alhassan)

    [ad_2]

    Source link

  • Motoci 3 Masu Amfani Da Gas (CNG) Sun Yi Bindiga A Tashar Mota A Kaduna

    [ad_1]

    Aƙalla motoci uku na alfarma masu amfani da iskar gas (Compressed Natural Gas (CNG), mallakar kamfanin sufuri na Silver Transport, sun ƙone ƙurmus sakamakon wata fashewa da ta auku da asubahin ranar Lahadi a tashar mota ta Kawo da ke jihar Kaduna, lamarin da ya tayar da hankalin jama’a tare da jawo damuwa kan tsaron amfani da irin wannan fasahar makamashi.

    Rahotannin shaidu sun nuna cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 3:00 na dare yayin da aka ajiye motocin domin shirin ɗaukar fasinjoji zuwa jihohi daban-daban da safe, inda fashewar ta auku a lokaci guda ta janyo gobara da ta ƙone motocin gaba ɗaya, duk da cewa babu wani mutum a ciki a lokacin da abin ya faru.

    • Gwamna Uba Sani Ya Tsawaita Shirin Sufurin Motocin CNG Kyauta Ga Al’ummar Jihar Kaduna
    • Gwamna Yusuf Ya Mika Motocin Bas Na CNG Guda 10 Ga Kungiyar NLC Reshen Kano

    Wani manaja a ɗaya daga cikin kamfanonin sufurin da ke aiki a yankin Mando Motor Park, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa motocin sabbi ne kuma suna cikin shirin fara aiki ne kafin wannan ibtila’i, yana mai godewa Allah da babu wanda ya jikkata ko ya rasa ransa, duk da girman ɓarnar da aka yi.

    Sai dai ya bayyana damuwa kan amfani da motocin CNG, yana mai cewa akwai buƙatar ƙarin shiri da tsauraran matakan tsaro kafin a rungumi wannan fasaha gaba ɗaya, inda ya ce “har yanzu ba mu kai matakin da za mu iya sarrafa wannan tsarin ba yadda ya kamata,” yana mai nuni da yiwuwar matsalolin fasaha ko rashin isasshen horo.

    A halin yanzu, jami’an ƴansanda da sauran hukumomin da abin ya shafa sun isa wurin domin gudanar da bincike kan musabbabin fashewar, yayin da ake sa ran sakamakon binciken zai fayyace ko matsalar ta samo asali ne daga tsarin gas ɗin ko wasu dalilai na daban, yayin da aka tabbatar da cewa babu asarar rayuka a lamarin.

    [ad_2]

    Source link

  • Esta: Wahalhalun da ake fuskanta a Najeriya ba za su dawwama ba — Shettima

    [ad_1]



    Mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima, ya tabbatar wa ’yan Najeriya cewa wahalhalun da ake fuskanta a yanzu ba za su dawwama ba.

    Ya ce al’amura za su inganta ƙarƙashin manufofin Shugaba Bola Tinubu.

    “Ina da tabbaci cewa idan muka haɗa kai, muka yi sadaukarwa, kuma muka yi imani da ƙasarmu, za mu shawo kan waɗannan ƙalubalen,” in ji shi.

    Shettima, ya bayyana haka ne a ranar Lahadi a Abuja, ta bakin mai magana da yawunsa, Stanley Nkwocha, a sakon bikin Esta.

    Ya ce gwamnati na aiki tuƙuru domin samar da zaman lafiya, farfaɗo da tattalin arziƙi, da kuma gina ci gaba mai ɗorewa.

    Ya ƙara da cewa gyaran ƙasa na buƙatar haƙuri, sadaukarwa da haɗin kai daga jama’a.

    Mataimakin shugaban ƙasar, ya ce yana da ƙwarin gwiwa cewa Najeriya za ta shawo kan matsalolin tattalin arziƙi da na tsaro da ake fuskanta a yanzu.

    Ya ƙara da cewa duk da wahalhalun da mutane ke ciki, ƙasar ba ta taɓa kasa cimma manufofinta ba.

    Shettima ya buƙaci ’yan Najeriya su ci gaba da zama a haɗe tare da goyon bayan gyare-gyaren da gwamnati ke yi.

    Ya ce ci gaba na buƙatar haƙuri da juriya, tare da haɗin kai.

    Haka kuma, ya roƙi jama’a su guji rabuwar kawuna, su rungumi abubuwan da ke haɗa su a matsayin al’umma ɗaya.

    Ya ce bambancin da ke tsakanin ’yan Najeriya yana daga cikin manyan ƙarfinsu.

    Da yake magana kan muhimmancin Esta, Shettima, ya ce wannan lokaci yana tunatar da Kiristoci muhimmancin sadaukarwa da kuma sabuwar rayuwa.

    Ya bayyana cewa Esta alama ce ta nasara kan baƙin ciki da kuma haske a kan duhu.

    “Esta tana tunatar da mu cewa waɗanda ba su yanke ƙauna ba za su yi nasara. Tana nuna yadda fata na gari ke tasiri a kan wahala,” in ji shi.


    [ad_2]

    Source link

  • Yadda Fatar Ki Za Ta Yi Laushi Da Sheki

    [ad_1]

    Gyaran fata abune mai matukar kyau ga mace, idan kina so ki ganki kullum cikin kyau tofa sai kin cire kiwa kina kokarin gyaran fata. Za kiga fatanki tana sheki, ta yi laushi, ruwa ko zama baya yi akai.

    Abubuwan bukata:

    Man zaitun, Lalle, Kurkur, Madara peak.

    Yadda ake hadawa:

    Za ki hade wadannan kayan hadin da na ambata a guri daya, sai ki kwaba su ki shafe jikinki da fuskarki, za kiyi wannan hadin kafin ki shiga wanka. Idan ya bushe a jikinki sai ki murje sannan sai ki shiga wanka jiki yana yin kyau yayi sheki.

    Gyaran jiki 2

    Wannan hadin shi akecewa kafi Turgewa.

    Abubuwan da ake bukata:

    Kur-kur, Dulka, Zuma, Kwai, Lemun tsami.

    Yadda ake hadawa:

    Ki hade su guri daya ki kwaba kamar yadda ake kwaba lalle, amma yafi kwabin lalle ruwa, sai ki shafe fuskarki.

    Idan kuma har dajiki kike so, sai ki shafa harda jiki bayan awa daya sai ki shiga wanka za ki ga yadda jikinki zai goge.

    Gyaran jiki 3

    Fata ta yi laushi da sheki

    Abubuwan da ake bukata:

    Lalle, Kwaiduwar kwai guda 3, Manja cokali 3, Kur-kur:

    Yadda ake hadawa:

    Sai ki kwaba su guri daya ki shafe jikinki zuwa awa daya, sai kiyi wanka da ruwan dumi, Sannan ki kara shafe jikinki da ita sai ki kuma yin wanka.

    Kyan fuska 1:

    Abubuwan da ake bukata:

    Dettol, Sabulun Ghana, Garin zogale, Farar albasa.

    Yadda ake hadawa:

    Sai ki hade su guri daya ki kirba su cikin Turmi, ki mulmula ki rinka wanke fuska za ki ga yadda fuskar ki za tayi.

    Gyaran fuska 2

    Wanna hadin wanda ya kesa fuska tayi haske da annuri ta kuma kore kurajen fuska.

    Abubuwan da ake bukata:

    Bawon kankana.

    Yadda ake hadawa:

    A samu bawon kankana sai a rinka goge fuska da shi yana gyara fuska tayi sumul.

    Gyaran Fata 1

    Abubuwan da ake bukata:

    Lemun tsami, bawon kwai, Kur-kur.

    Yadda ake hadawa:

    Za ki hade su guri daya sai ki daka su, ki rinka wanka dashi fatar mace za ta goge tayi kyawun gaske.

    Gyaran fata 1

    Abubuwan da ake bukata:

    Ganye magarya, Sabulun salo.

    Yadda ake hadawa:

    Za ki daka Ganyan magarya sai ki zuba a cikin sabulun salo ki rinka wanka yana gyara jiki.

    Gyaran fata 2

    Abubuwan da ake bukata:

    ganyan magarya, Man zaitun, Man habbatussauda.

    Yadda ake hadawa:

    Ana daka ganyan magarya a zuba cikin Man zaitun da Man habbatussauda shi ma yana gyara.

    Gyaran fata 3

    Abubuwan da ake bukata:

    Lalle, Garin ridi.

    Yadda ake hadawa:

    Ana amfani da Lalle kafin ki shiga wanka sai ki kwaba ki zuba garin ridi ki shafe jikinki zuwa awa daya sai kiyi wanka.

    Maganin tabo a jiki:

    Ki samu khal babban cokali daya sai ki hada da ruwa Kofi biyu ki tafasa bayan ya huce sai ki rinka shafawa a jiki da fuskar.

    Maganin Nankarwa

    alama) A turance

    Nankarwa shine irin wannan zanen da yake fitowa a cikin mace da zaran ta fara haihuwa ko kuma in tayi kiba a ciki, mace ya kan fitowa ya sanya fatar cikin duk ta yamutse ana amfani da Man Dodon kodi a shafa a ciki, yana gyara fatar ciki ta koma kamar ba ta haihu ba.

    Maganin nankarwa 2

    Abubuwan bukata:

    Man kadanya, Man zaitun, Lemun tsami.

    Yadda ake hadawa:

    Ki hada Man kadanya da Man zaitun guri daya, ki matsa lemun tsami a kai, amma ba da yawa ba, ki matsa sosai sannan sai ki dinga sharewa ki yawaita yi.

    Maganin nankarwa 3

    Ana shafa zuma farar saka da daddare, idan za ki kwanta barci da safe sai ki samu ruwan dimi ki wanke.

    [ad_2]

    Source link

  • ’Yan sanda 4 sun mutu a harin ’yan ta’adda a Borno

    [ad_1]



    Aƙalla jami’an ’yan sanda huɗu da wani mafarauci ɗaya sun mutu a wani hari da ake zargin mayaƙan Boko Haram da ISWAP ne suka kai a wasu yankuna na Jihar Borno.

    Mai magana da yawun ’yan sanda a jihar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya bayyana cewa lamarin ya faru ne da tsakar dare a ƙananan hukumomin Nganzai da Mobbar.

    Ya ce a ranar Asabar, 4 ga Afrilu da misalin ƙarfe 1:00 na dare, ’yan ta’addan suka kai hari hedikwatar ’yan sanda ta Nganzai da zummar ƙwace garin.

    Sai dai ya ce jami’an ’yan sanda tare da haɗin gwiwar rundunar MOPOL da kuma ƙungiyar Crack Squad sun fafata da maharan a wani gumurzu, inda suka daƙile harin tare da hana su shiga garin.

    Haka kuma, ya ce maharan sun yi amfani da manyan makamai ciki har da rokoki, lamarin da ya janyo lalata wani ɓangare na ofishin ’yan sanda har da ƙona wata tsohuwar motar sulke.

    “Amma abin takaici, jami’an ’yan sanda huɗu sun rasa rayukansu a bakin aiki,” in ji shi.

    A wani hari makamancin haka da ya faru da misalin ƙarfe 2:40 na dare a ranar Asabar, ’yan ta’adda sun kai farmaki sansanin ’yan gudun hijira na Malam Fatori da ke Damasak a Ƙaramar Hukumar Mobbar.

    Rahoton ya ce maharan sun nufi wurin sintiri na haɗin gwiwar CJTF da mafarauta a ƙofar sansanin, inda wani mafarauci mai suna Atom Abua mai shekara 40 ya rasa ransa.

    Haka kuma, an yi asarar gidaje kusan 20 da rumfunan ƙasa a sakamakon harin.

    ASP Daso ya ƙara da cewa an daƙile harin yayin da haɗin gwiwar jami’an tsaro da suka haɗa da ’yan sanda, sojoji, CJTF da mafarauta suka tari hanzarin cikin gaggawa.

    Ya ce Kwamishinan ’yan sanda na jihar, CP Naziru Abdulmajid, ya aika da ƙarin jami’ai da kayan aiki zuwa wuraren domin ƙarfafa tsaro da kuma hana sake aukuwar irin wannan lamari a nan gaba.

    Ya kuma yaba da jarumtar jami’an da suka fuskanci maharan, yana mai miƙa ta’aziyya ga iyalan waɗanda suka rasu.

    “Hukumar za ta ci gaba da farautar waɗanda suka aikata wannan aika-aika domin gurfanar da su a gaban kotu,” in ji shi.

    Ya buƙaci jama’a da su kwantar da hankalinsu, su kasance masu lura, tare da bai wa jami’an tsaro cikakken haɗin kai ta hanyar bayar da sahihan bayanai.


    [ad_2]

    Source link

  • Mutum 2 sun mutu, 10 sun jikkata a Gombe

    [ad_1]



    Hukumar kiyaye haɗura ta ƙasa FRSC ta tabbatar da mutuwar mutane biyu tare da jikkatar wasu 10 a wani hatsarin mota da ya afku a kan hanyar Gombe zuwa Yola.

    Hatsarin ya faru ne da misalin ƙarfe 7:40 na yammacin ranar Juma’a a yankin Gona, inda rahotanni suka nuna cewa fashewar taya ce ta haddasa shi.

    Kwamandan FRSC na jihar, Mista Samson Kaura, ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai, yana mai cewa hatsarin na mota guda ɗaya ne.

    Ya ce mutanen da suka jikkata sun samu raunuka iri-iri da suka haɗa da na kai, kurjewa da sauransu.

    A cewarsa, an garzaya da waɗanda suka samu raunuka zuwa Asibitin Koyarwa na Tarayya domin samun kulawar likitoci, yayin da aka kai gawarwakin waɗanda suka rasu ɗakin ajiye gawa na asibitin.

    Ya ƙara da cewa binciken farko ya nuna fashewar taya ce ta janyo hatsarin, wanda ka iya nasaba da tuƙin ganganci, ɗaukar kaya fiye da ƙa’ida ko gudun wuce ƙima.

    Kaura ya yi kira ga direbobi da su kiyaye dokokin hanya, su guji lodin da ya wuce ƙima da kuma gudun wuce sa’a, yana mai jaddada muhimmancin tsaron rayuka.

    “Dole ne direbobi su fifita lafiyarsu da ta fasinjoji fiye da gaggawa ko neman riba, domin iyalansu na jiran dawowarsu lafiya,” in ji shi.


    [ad_2]

    Source link

  • Amurka_Isra’ila Akan Iran: Rikicin Gabas ta Tsakiya Ya Fara Daukar Sabon Salo

    [ad_1]

    Tun bayan barkewar zanga-zangar tsadar rayuwa da ta rikide ta koma tarzomar kin jinin gwamnati daga wasu acikin al’ummar Iran a karshen Disamba 2025 da farkon Janairu 2026, an samu karuwar muhawara tsakanin Iran da Amurka, ciki har da tsauraran kalamai da barazanar juna tsakanin shugabannin kasashen biyu.

    Amurka ta nuna goyon baya ga masu zanga-zangar ta Iran, tana kira ga gwamnatin Tehran da ta daina yin amfani da karfi wajen murkushe su, wanda hakan ya sanya Shugaba Donald Trump ya yi barazanar cewa, Washington na iya “taya” masu zanga-zangar ko ma daukar matakai idan hukumomin Iran suka yi amfani da karfi wajen kashe mutane.

    • ASUU Ta Ba Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana Hudu Kan Sabon Tsarin Albashi
    • UBEC Ta Kaddamar Da Tsarin Dala Miliyan 552 Domin Ilimin Bai-daya

    A nata martanin, Iran ta zargi Amurka da tsoma baki sosai a harkokinta na cikin gida, tana cewa wannan wani yunkuri ne na kifar da gwamnatinta, wanda kuma ba za ta lamunci hakan ba. A cikin martanin da aka fitar a hukumance, Tehran ta yi gargadin cewa, duk wani yunkurin Washington na kai hari Tehran zai dagula zaman lafiyar yankin, inda ta sha alwashin mayar da martanin hari kan duk wani sansanin sojin Amurka dake yankin da kuma duk kasar da ta bari Amurka ta yi amfani da kasarta ko sararin samaniyarta wurin kai mata (Iran) hari.

    Amma Amurka ta yi biris da duk wannan martanin, inda a ranar 28 ga watan Fabrairu, ta hada kai da Isra’ila suka kaddamar da hare-hare cikin Iran wanda hakan ya yi sanadin mutuwar Babban jagoran addini na kasar, Ayatullah Alkamnei tare da wasu kwamandojin sojojin juyin juya hali (IRGC) na Iran.

    Rahotanni na nuna cewa, bayan wata guda da fara hare-haren hadin gwiwa tsakanin Amurka da Isra’ila kan Iran, yankin Gabas ta Tsakiya na kara fadawa cikin rikici mai tsanani, inda yawan mace-macen fararen hula ke karuwa, yayin da rikicin ke kara yaduwa zuwa wasu sassa na yankin.

    Bincike ya nuna cewa, wannan rikici bai zama dole ba, domin akwai hanyoyin diflomasiyya da za a iya bi kafin fara hare-haren amma aka yi watsi da su, sabida rashin girmama tsarin doka na Majalisar Dinkin Duniya, lamarin da ya kara dagula al’amura maimakon kawo mafita.

    Masana harkokin kasa da kasa sun bayyana damuwa kan yadda aka kaddamar da wannan hare-haren na son rai, musamman dangane da rashin samun amincewar Majalisar Tsaro ta Majalisar Dinkin Duniya kafin daukar matakin soja, wanda hakan na iya kawo cikas ga dokokin kasa da kasa da kuma rage darajar tsarin doka a duniya.

    Rahotanni sun nuna cewa, maimakon samun kwanciyar hankali da Amurka ta yi ikirarin samarwa, hare-harenta sun kara jefa yankin cikin wani hali mawuyaci. Tarihi ya nuna cewa, irin wadannan matakan hare-hare na Amurka, ba sa haifar da komai sai dai haddasa rashin zaman lafiya mai dorewa, kamar yadda aka gani a sauran kasashen da irin hakan ta faru da su, kamar Libya, Iraq, Afghanistan da Syria.

    Masana sun jaddada cewa, hanyar soja kadai ba za ta iya kawo cikakken tsaro ba. Sun ce yankin na bukatar zaman lafiya, ci gaba da tattaunawa, da kuma hanyoyin siyasa domin warware matsalolin da ke akwai.

    Sam bai dace ba, manyan kasashe su rika take kanana, kamar ana rayuwar dabbobin daji. Ya dace, kasashen duniya su guji daukar matakai na kashin kai, su kuma mutunta dokokin kasa da kasa domin tabbatar da adalci da zaman lafiya a duniya.

    [ad_2]

    Source link