APC ta rage wa Mata kuɗin tsayawa takara a Borno
[ad_1]
Jam’iyyar APC reshen Jihar Borno ta rage wa mata kashi 50 cikin 100 na farashin fom ɗin tsayawa takara, makonni gabanin zaɓen kananan hukumomi da za a gudanar a ranar 13 ga Disamba, 2025.
Da yake sanar da hakan a Maiduguri, shugaban jam’iyyar APC na jihar, Alhaji Bello Ayuba, ya ce an ɗauki matakin ne domin magance matsalar ƙarancin kuɗi da ke hana mata shiga siyasa da tsayawa takara.
“Wannan wani ɓangare ne na ƙoƙarin da muke yi na samar da daidaito ga mata a fagen siyasa.
“Muna son ganin mata da yawa suna jagoranci a matakin ƙasa, suna ba da gudummawa da ƙarfinsu wajen gudanar da mulki,” in ji Ayuba.
A cewarsa, “an ƙayyade farashin fom ɗin neman kujerar shugaban ƙaramar hukuma ga maza kan naira miliyan 2, yayin da fom ɗin kansila zai ci ₦500,000, amma mata za su biya rabin wannan adadi — ₦1 miliyan da ₦250,000.”
Ya ƙara da cewa an kafa kwamitocin tantancewa da sasantawa domin tabbatar da cewa zaɓen fidda gwani zai gudana cikin gaskiya da lumana a dukkan ƙananan hukumomi 27 da gundumomi 112 na jihar.
“Za a gudanar da zaɓen fidda gwani a lokaci guda a ƙarshen wannan watan domin guje wa maguɗin zaɓe,” in ji shi.
Ayuba ya jaddada aniyar jam’iyyar ta tabbatar da sahihin zaɓe, inda ya ce Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Jihar Borno (BOSIEC) za ta gudanar da babban zaɓen a ranar 13 ga Disamba, 2025.
“Mun himmatu wajen tabbatar da ɗorewar dimokuraɗiyya ta hanyar adalci, daidaiton jinsi, da kuma gudanar da zaɓe cikin lumana,” in ji shi.
“Mata na da matuƙar muhimmanci ga shugabanci, kuma wakilcinsu yana ƙarfafa tsarin mulki.”
Masu sa ido da ƙungiyoyin kare haƙƙin mata sun yaba da matakin jam’iyyar APC, inda suka bayyana shi a matsayin muhimmiyar hanya ta ƙara daidaiton jinsi a siyasar Jihar Borno.
Sun ce rage kuɗin fom ɗin tsayawa takara ga mata ba kawai zai ƙarfafa gwiwar mata masu neman tsayawa takara ba, har ma zai zaburar da ƙananan ‘yan mata su ga shugabanci a matsayin abin da za su iya cimma.
Wannan mataki dai ya yi daidai da kiraye-kirayen ƙasa da ƙasa na ƙara shigar da mata cikin harkokin mulki, tare da ƙarfafa imanin cewa dimokuraɗiyya na bunƙasa ne idan maza da mata suka haɗa kai wajen tsara makomar al’ummarsu.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link