An Sasanta Da Malam Lawal Triumph Da Majalisar Shura Ta Kano



Wani zama na sasanci tsakanin Majalisar Shura ta Jihar Kano da malamin addini, Malam Lawal Abubakar Triumph, ya gudana a ofishin Hukumar Tsaro ta DSS da ke Kano a ranar Litinin.

An gudanar da taron ne ƙofa rufe, inda mambobin Majalisar suka shawarci malamin da ya riƙa yin taka-tsantsan da natsuwa a cikin bayanansa na addini. Rahotanni sun nuna cewa malamin ya nemi afuwa a yayin tattaunawar.

Bayan kammala zaman, Malam Lawal Triumph ya wallafa kalmar “Alhamdulillah” a shafinsa na Facebook abin da jama’a da dama suka fassara a matsayin alamar cewa an kammala sasanci lafiya tsakaninsa da Majalisar Shura.

Jaridar LEADERSHIP ta rawaito a baya cewa Gwamnatin Jihar Kano ta miƙa lamarin ga Majalisar Shura domin bincikar zarge-zargen da ake yi wa Malam Triumph na yin kalaman batanci a cikin wani wa’azi da ya yi, wanda ya jawo cece-kuce da ƙorafe-ƙorafe daga sassa daban-daban na al’umma.

Zamu kawo muku cikakken bayani idan sun bayyana.



Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *