Ambaliya: NEDC ta raba wa mutum 2,200 kayan agaji a Yobe

[ad_1]



Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC), ta raba wa mutum 2,261 da ambaliyar ruwa ta shafa a Potiskum, Nangere da Jakusko a Jihar Yobe, kayan agaji.

An raba kayan ne a unguwanni 21 na Potiskum, ƙauyukan Kolo da Ajim a Nangere, da kuma kauyukan Dachia, Yim, Saminaka, Garin Maji da Amshi a Jakusko.

Kayan da aka bayar sun haɗa da shinkafa, taliya, man girki, da kuma tufafi, kayan mata da shadda.

Sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Yobe (SEMA), Dokta Mohammed Goje, ya ce Gwamna Mai Mala Buni ya ba da umarnin gaggauta tallafa wa al’ummar da ambaliyar ta shafa.

Ya kuma roƙi jama’a da su yi amfani da kayan agajin yadda ya dace.

A nasa jawabin, babban daraktan NEDC, Mohammed Goni Alkali wanda Dokta Ali Ibrahim Abbas ya wakilta, ya gode wa gwamnatin Yobe bisa shirin.

Ya ce wannan tallafi wani ɓangare ne na manufar NEDC na taimaka wa al’ummar Arewa Maso Gabas wajen magance matsalolin yankin.

An sa ran wannan tallafin zai rage wa jama’a wahalhalun da ambaliyar ruwa ta jawo a jihar.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *