Tsohon gwamnan soji na Filato, Sanata Muhammad Mana ya rasu

[ad_1]



Tsohon Gwamnan mulkin Soji na Jihar Filato, kuma Sanatan da ya wakilci Adamawa ta Arewa, Kanal Muhammad Mana, ya rasu.

Ya rasu ne da yammacin ranar Juma’a a Abuja, kwanaki biyu bayan sallamarsa daga asibiti.

Ɗan uwansa, Sarkin Fulani na Mubi, Abdurrahman B. Kwaccham ne, ya tabbatar da rasuwar a daren ranar Juma’a.

Mana, ɗan asalin Ƙaramar Hukumar Maiha a Jihar Adamawa, ya shugabanci Jihar Filato a matsayin shugaban mulkin soja daga Disamban 1993 zuwa Agustan 1996, a zamanin mulkin marigayi Janar Sani Abacha.

Daga baya ya zama Kwamandan Rundunar Shugaban Ƙasa a lokacin mulkin Janar Abdulsalami Abubakar, kafin daga bisani ya zama Sanata mai wakiltar Adamawa ta Arewa a shekarar 2007.

Kwaccham, ya ce marigayin ya rasu ya bar matansa da ’ya’yansa.

Za a yi jana’izarsa da misalin ƙarfe 2 na ranar Asabar a Masallacin Juma’a na Ƙasa da ke Abuja.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *