Yau ake sake gurfanar da majinyaci ya lakaɗa wa likita duka a asibiti
[ad_1]
A yau ake gurfanar da wani majinyaci mai shekaru 40, zai gurfana a kotu, bisa zargin cin zarafin wata likita mai suna Fatima Umar Gamsa a asibitin Ƙwararru na tunawa da marigayi Janar Sani Abatch da ke Damaturu Jihar Yobe.
Shugaban Ƙungiyar Likitocin Najeriya reshen Jihar Yobe, Dakta Umar Aji, ya ce kungiyar ta kai ƙara gaban ’yan sanda kuma tana jiran hukuncin da kotu za ta yanke.
“A yanzu shari’ar tana gaban kotu, kuma ƙungiyar ba za ta ce komai ba har sai ta ji sakamakon hukuncin kotun,” Aji ya jaddada.
Wanda ake zargin, Ahmed Usman mazaunin rukunin gidajen Abba Ibrahim da ke Damaturu an tsare shi a gidan yari na Potiskum har zuwa lokacin da za a saurari ƙarar.
Kakakin ’yan sandan jihar, SP Dungus Abdulkarim, ya ce, “Mun rigaya mun miƙa ƙarar ga kotu domin ta tantance ranar da za a saurari ƙarar.”
Babbar kotun majistare ta 1 ta tabbatar da cewa an ɗage sauraren ƙarar domin ci gaba da sauraren ta, tare da tsare wanda ake tuhuma a gidan yari.
Wasu ma’aikatan hukumar kula da asibitocin jihar Yobe da suka buƙaci a sakaya sunansu saboda rashin ikon yin magana a kan lamarin, sun yi qarin haske kan lamarin.
A cewar ma’aikatan, “Majinyacin, Ahmed Usman, ya je asibitin ne tun farko domin duba lafiyarsa tare da likitan da ke bakin aiki. “Lokacin da likitan ya kira sunansa, baya nan, shi ne aka ajiye babban fayil ɗinsa a gefe yayin da majiyyaci na gaba ya je wurin ya bayyana.
”Bayan hakan majiyyacin ya fusata, yana jin an yi watsi da shi. A cikin wani yanayi, marar lafiyan ya fita waje, ya yanko bulala daga bishiya, ya yi amfani da ita don cin zarafin likitan.”
Sun ƙara da cewa, jami’an tsaron asibitin sun shiga tsakani don shawo kan lamarin, kuma an kai rahoton lamarin ga ‘yan sanda.
Kokarin tattaunawa da Dr. Fatima Umar Gamsa ya ci tura, domin tana kwance don jinya daga lamarin.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link