’Yan kasar Chadi 3 sun mutu a hatsarin kwalekwale a Borno

[ad_1]



Wani kwalekwale da ke ɗauke da fasinjoji takwas ya kife yayin da yake ƙetare kogin da ke kan iyaka da garin Gamboru na Najeriya da Fotokol a ƙasar Kamaru, inda mutane uku suka mutu.

Lamarin ya faru ne da misalin qarfe 6:30 na yamma lokacin da kwalekwalen, wanda wani Mamman Nur Abbagana na Kasuwan Katako, Gamboru ke tuƙa shi ya kife a tsakiyar ruwa tare da jefa dukkan fasinjoji cikin ruwa.

Majiyoyin tsaro sun tabbatar da cewa dukkan fasinjoji takwas ’yan ƙasar Chadi ne da ke tafiya daga Jos, Jihar Filato, a kan hanyarsu ta zuwa N’Djamena, Jamhuriyar Chadi.

An ceto fasinjoji biyar, waɗanda aka tabbatar da suna raye ba su mutu ba.

Wata mata mai suna Alphosine Makebu Beboroum, mai shekaru 34, da ’ya’yanta mata biyu Centich Mamajibe, mai shekaru 3, da Mamajilem Bebaroum, ‘yan watanni 10, sun nutse kuma har yanzu ba a gano su ba har zuwa Kammala wannan rahoto, duk da ana cigaba da gudanar da aikin ceto da bincike.

A halin yanzu, hukumomin ’yan sanda sun kuma tabbatar da kama mai tuƙa kwale-kwalen saboda karya umarnin gwamnatin Jihar Borno na tilasta wa duk masu aikin kwalekwale da su yi amfani da jakar ceto.

Kakakin rundunar ASP Nahum Kenneth Daso ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan musabbabin faruwar lamarin.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *