Sojoji sun ceto ’yan mata 12 da ISWAP suka sace a Borno
[ad_1]
Sojojin Rundunar Operation Hadin Kai (OPHK), sun samu nasarar ceto ’yan mata 12 da ’yan ta’addan ISWAP suka sace a gundumar Mussa da ke Ƙaramar Hukumar Askira/Uba a Jihar Borno.
An sace su ne ranar 23 ga watan Nuwamba 2025, yayin da suke girbe amfanin gonakin iyayensu.
Yaran ’yan shekaru 15 zuwa 20 ne.
Wannan ya haifar da firgici a yankin, lamarin da ya sa mazauna yankin da dama suka tsere zuwa wasu garuruwa.
Majiyar tsaro ta tabbatar da cewa an ceto su lafiya, duk da cewa ba a bayyana yadda aka ceto su ba.
Har yanzu ba a san ko an biya kuɗin fansa.
Waɗanda aka ceto sun haɗa da Fatima Shaibu (17), Fatima Umaru (15), Hauwa Abubakar (18), Saliha Muhammad (15), Sadiya Umaru (17), Amira Babel (15).
Sauran sun haɗa da Zara Adamu (17), Nana Shaibu (15), Zainab Musa (18), Zainab Muhammad (17), Jamila Saidu (15) da kuma Hauwa Hamidu (17).
An kai su wani waje na musamman domin duba lafiyarsu kafin a sada su da iyayensu.
Wannan na zuwa ne bayan sojoji sun farmaki maɓoyar ISWAP da ke Kudancin Borno.
Iyayen yaran sun bayyana farin cikinsu, inda suka bayyana hakan a matsayin babbar nasara.
Mai dangantaka
[ad_2]
Source link