Majalisar Dokokin Nasarawa Ta Koka Kan Barazanar Tsaro, Ta Nemi Gwamna Ya Ɗauki Matakin Gaggawa
[ad_1]
Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa ta ce matsalar tsaro na ƙara tsananta a jihar, kuma ba lallai a iya kula da lafiyar jama’a a yanzu ba.
Sun roƙi Gwamna Abdullahi Sule ya ɗauki matakai don dakatar da kashe-kashe da sace-sace da ke ƙaruwa a birane da ƙauyuka.
Kakakin Majalisar, Danladi Jatau ne, ya yi wannan gargaɗi a zaman majalisar na ranar Talata bayan jagoran ɓangaren ‘yan adawa, Luka Iliya Zhekaba, ya koka kan hare-haren da ke addabar al’umma da dama.
’Yan majalisar sun ce duk da cewa Gwamna Sule yana ƙoƙarin magance matsalar tsaro, halin da ake ciki yanzu na buƙatar matakin gaggawa da matakai na musamman.
Yankin kudancin jihar, wanda ke iyaka da Benuwe, ya zama wajen sace mutane, hare-hare, da kashe-kashe, lamarin da ya tilasta wa jama’a da dama barin gidajensu.
A ƙarshen mako, ’yan bindiga sun shiga gidan Yusuf Agbo a Giza, a ƙaramar hukumar Keana, inda suka sace shi tare da matarsa, kuma har yanzu ba a ji labari daga waɗanda suka sace su ba.
A wani harin na daban, wasu sun kai wa ma’aurata hari a gonarsu da ke Barkin Abdullahi, a ƙaramar hukumar Lafia.
Har yanzu rundunar ’yansandan jihar ba ta fitar da wata sanarwa kan waɗannan hare-hare ba.
[ad_2]
Source link