Ousmane Dembele zai buga wasan PSG da Bayern Munich

[ad_1]



Dan wasan gaban Paris Saint-Germain (PSG) ɗan asalin ƙasar Faransa, Ousmane Dembele, zai kasance cikin tawagar da za ta fafata da Bayern Munich a wasan Champions League da za a buga yau Talata.

Dembele, wanda ya zura ƙwallo a wasan da PSG ta doke Bayern Munich da ci 2–0 a gasar Club World Cup zagaye na kwata-final a watan Yuli, bayan mako guda ya fice daga wasa sakamakon jin ciwo a cinyarsa ta dama a fafatawar da suka yi da Lorient.

Kocin PSG, Luis Enrique, ya tabbatar da cewa dan wasan ya murmure daga raunin kuma zai iya buga wasan yau.

“Dembele yana cikin ƙoshin lafiya, ya koma atisaye cike da karsashi, kuma zai kasance cikin jerin ‘yan wasan da za su buga wasan da Bayern,” in ji Enrique.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *