PDP Ta Ɗage Babban Taronta Biyo Bayan Ficewar Wasu Manyan Jiga-jigai

[ad_1]


Jam’iyyar PDP, ta ɗage taron kwamitin zartarwa na ƙasa (NEC) karo na 103 da aka shirya gudanarwa a ranar Laraba, 15 ga watan Oktoba, 2025.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun jam’iyyar, Debo Ologunagba, ya fitar a ranar Litinin, ya ce an yanke wannan shawara ne saboda “sabbin abubuwan da ke faruwa a cikin jam’iyyar,” sai dai bai bayyana cikakkun bayanai ba.

Ya ce, “An shirya gudanar da taron NEC na 103 a ranar 15 ga watan Oktoba, 2025, amma saboda sabbin abubuwan da suka taso, kwamitin na ƙasa (NWC) a wani taro da ya gudanar a ranar 13 ga watan Oktoba, ya amince da ɗage taron zuwa wani lokaci a nan gaba.”

Wannan mataki na zuwa ne a daidai lokacin da PDP ke fuskantar sabon rikicin cikin gida, inda wasu daga cikin manyan jiga-jiganta ke ficewa daga jam’iyyar suna komawa jam’iyyar APC.

Gwamnan Jihar Enugu, Peter Mbah, ya koma jam’iyyar APC a ranar Talata, yayin da rahotanni ke cewa gwamnan Jihar Bayelsa, Douye Diri, da na Jihar Taraba, Agbu Kefas, na shirin komawa APC .

Wannan ci gaban ya zo ne a daidai lokacin da PDP ke shirin gudanar da babban taronta na ƙasa da za a yi a Ibadan, a Jihar Oyo, daga ranar 15 zuwa 16 ga watan Nuwamba.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *