Babu wani hari da aka kai sakatariyar NUJ a Yobe — ’Yan Sanda




Rundunar ’yan sandan Jihar Yobe, ta ƙaryata rahotannin da ke nuna cewar an kai hari sakatariyar ƙungiyar ’yan jarida ta Najeriya (NUJ) da ke Damaturu.

Wannan na cikin wata sanarwa da rundunar ta fitar a ranar Juma’a.

Kakakin rundunar, SP Dungus Abdulkarim, ya ce abin da ya faru shi ne wani jami’in tsaro da ke gadin wajen ne ya samu rauni a ƙafarsa ta hagu.

A cewarsa, raunin ba shi da alaƙa da harbin bindiga, kamar yadda wasu shafukan Internet suka wallafa.

Lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:45 na daren ranar 19 ga watan Satumba, 2025.

Rundunar ta ce babu wani ɗan jarida ko ma’aikacin NUJ da aka kai wa hari ko aka yi wa barazana.

SP Abdulkarim, ya ƙara da cewa ana ci gaba da bincike kan lamarin, kuma ya bai wa jama’a tabbacin cewa za a ɗauki matakan da suka dace.

Rundunar ta kuma yi kira ga ’yan jarida da su guji yaɗa labarai ba tare da tabbatarwa ba, domin hakan na iya haifar da tashin hankali.




Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *