Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

[ad_1]

Dakarun runduna ta 6 ta sojojin Nijeriya mai taken ‘Operation Lafiya Nakowa’ sun yi nasarar kashe ‘yan ta’adda biyu tare da kwato tarin makamai da alburusai a karamar hukumar Takum dake jihar Taraba.

Wannan farmakin na daya daga cikin kokarin da sojoji suke yi na kawar da ‘yan ta’adda da miyagun ayyuka a fadin jihar.

A wata sanarwa da mukaddashin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji ta 3, Aliyu Danja a Jalingo ya fitar, rundunar ta 6 da rundunar sashe ta 3 ta ‘Operation Whirl Stroke’ ne suka gudanar da harin.

Danja ya ce, sojojin a yayin da suke aiki da sahihan bayanan sirri dangane da shirin kai hari kan al’ummar Chanchangi da kungiyar ta’adda ta Bojo ke shirin yi a ranar 15 ga Satumba, 2025, sun yi artabu da ‘yan ta’addan a kan hanyar Demeva zuwa Chanchangi.




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *