Ƙarin Farashin Fetur: Ƙungiyar Ƙwadago Ta Nemi A Dakatar Da Karɓar Haraji

[ad_1]

Ƙungiyar ƙwadago ta Nijeriya, NLC, ta buƙaci gwamnati ta ba ma’aikata ƙarin alawus na tsadar rayuwa, ƙarin albashi na wucin gadi da kuma rangwamen haraji domin rage wahalar da karin farashin fetur ya jawo.
A wata sanarwa da shugaban NLC, Joe Ajaero, ya sanya wa hannu mai taken “Ce to ‘yan Nijeriya daga wannan firgici: taimakon gaggawa ya zama dole”, ƙungiyar ta kuma bukaci gwamnati ta gaggauta farfaɗo da matatun man fetur na Nijeriya.
  • Boko Haram Sun Sake Kai Hari Kan Wani Sansanin Sojoji A Borno
  • Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya A Birnin Paris
NLC ta bayyana cewa ƙarin farashin man fetur ya ƙara tsananta wahalar tattalin arziki ga ma’aikata da sauran ‘yan Nijeriya ke fuskanta a halin yanzu.
Kungiyar ta jaddada cewa ba daidai ba ne gwamnati ta jingina matsalar kawai da rikicin da ke faruwa a Gabas ta Tsakiya, tare da cewa hakkin gwamnati ne ta ɗauki matakan gaggawa domin kare jama’a daga wahala.
NLC ta kara da cewa, bai da ce gwamnati ta ki ɗaukar matakan da za su sauƙaƙa wa jama’a ba, musamman a irin wannan lokaci na tsadar rayuwa.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *