Wakilin Kasar Sin: Rikici A Yankin Gulf Ba Zai Amfanawa Kowa Da Komai Ba

[ad_1]

Manzon musamman na kasar Sin a yankin Gabas ta Tsakiya Zhai Jun, ya jaddada muhimmancin dakatar da bude wuta da rikici a yankin Gulf, yayin da ake fargabar rikicin dake gudana tsakanin Iran da Amurka da Isra’ila ka iya kara dagula al’amura.

Yayin ganawarsa da Sheikh Abdullah bin Zayed Al Nahyan, mataimakin firaminista kuma ministan harkokin wajen Hadaddiyar Daular Larabawa a jiya, Zhai Jun wanda ke rangadi a yankin Gabas ta Tsakiya, ya ce kasar Sin ta damu matuka da yanayin da yankin ke ciki.

Wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen Sin ta fitar ta ruwaito Zhai Jun na cewa, rikici da tashe-tashen hankula ba za su amfani muradun kowa ba. Yana mai cewa dakatar da bude wuta ita ce mafita ga yanayin da ake ciki. (FMM)

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *