Sojoji Sun Daƙile Hare-haren Boko Haram, Sun Kashe Mutane 29 A Borno, Yobe


Sojojin Operation Hadin Kai (OPHK) sun kashe ‘yan ta’adda 29 a wasu hare-hare da dama a jihohin Borno da Yobe tsakanin Asabar da Lahadi, inda suka kai hari kan sansanonin ‘yan ta’adda da kuma wadanda ke kokarin kutsa kai cikin sansanonin sojojin.

An kashe ‘yan ta’addan a kauyen Lamusheri, karamar hukumar Gujba, Yobe, da kuma sansanin rundunar tsaro da ke Limankara da Kukawa, jihar Borno.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi, jami’in yada labarai na rundunar hadin gwiwa (Arewa maso Gabas), Laftanar Kanar Sanni Uba, ya ce wannan matakin ya nuna “tsauraran matakan da rundunar ta dauka akan ‘yan ta’addan da hanyoyin aiwatar da muggan ayyukansu na ta’addanci.”



Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *