’Yan bindiga sun sace dalibai a wata makarantar Neja

[ad_1]



’Yan bindiga sun kai hari makarantar Katolika ta St. Mary da ke cikin yankin Papiri a ƙaramar hukumar Agwara ta Jihar Neja, sannan suka sace ɗalibai da malaman da ba a kai ga tabbatar da adadinsu ba.

Har zuwa yanzu dai babu cikakkun bayanai a kan harin, amma majiyoyi sun shaida wa wakilinmu cewa an yi awon gaba da ɗalibai da dama yayin harin da aka kai makarantar.

Wata majiya daga ɗaya daga cikin coci-cocin Katolika a jihar ta tabbatar da lamarin, tana mai cewa har yanzu makarantar na kan tattara bayananta a kan harin.

“Eh, gaskiya ne, amma ba ni da ikon bayar da cikakkun bayani. Coci za ta fitar da sanarwa a hukumance daga baya a yau,” in ji shi.

Da aka tuntubi mai magana da yawun rundunar ’yan sandan Jihar Neja, SP Wasiu Abiodun, ya ce zai bayar da cikakkun bayanai daga baya.

Sai dai shugaban sashen bayar da agaji na ƙaramar hukumar Agwara, Ahmed Abdullahi Rofia, ya tabbatar da harin ta wayar salula.

Ya ce ’yan ta’addan sun kai hari kan makarantar ne tsakanin ƙarfe 2:00 zuwa 3:00 na dare, yana mai cewa ba a kai ga tabbatar da adadin ɗalibai da malaman da aka sace ba tukuna, domin har yanzu hukumomi na ci gaba da tantancewa.

Lamarin ya faru ne kwanaki kaɗan bayan irin wannan hari a Maga, Jihar Kebbi, inda aka yi garkuwa da ɗalibai mata 25, abin da ya ƙara tayar da hankula kan tabarbarewar tsaro a makarantu a yankin.

Ko a ranar Alhamis, sama da makarantu 50 aka rufe a Jihar Kwara sakamakon barazanar ta’addancin ’yan bindiga.

Shugaba Bola Tinubu ya soke tafiyarsa zuwa kasashen Afirka ta Kudu da Angola domin jagorantar dakile matsalolin tsaron.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *