Sanata Natasha ta koma Majalisar Dattawa

[ad_1]



Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan mai wakiltar Kogi ta Tsakiya a Majalisar Dattawa, ta koma ofishinta da ke harabar majalisar bayan ƙarewar wa’adin dakatarwar watanni shida da aka yi mata.

A wani bidiyon komawarta ofis da ya karaɗe shafukan sada zumunta, ’yar majalisar ta zargi Shugaban Majalisar Dattawan, Sanata Godswill Akpabio da ɗaukarta a matsayin baiwarsa.

A cewarta, kamar yadda Akpabio ke matsayin sanata haka ita ma sanata ce.

Sanata Natasha ta ce duk da cewa an dakatar da ita ba bisa ƙa’ida ba, ta riƙa sauke nauyin al’ummar mazaɓarta na Kogi ta Tsakiya, saboda a cewarta ba ta son al’ummarta su ji kamar an yi watsi da su.

Tun da safiyar yau ce rahotanni suka bayyana cewa an buɗe ofishin sanatar da ke Suite 2.05 a cikin ginin Majalisar Dattawan.

Gabanin komawarta, ’yan sanda sun yi amfani da barkonon tsohuwa domin tarwatsa magoya waɗanda suka raka ta zuwa Majalisar Dattawa daga Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja.

Bayanai sun ce magoya bayan sun yi tattaki ne domin raka sanatar zuwa majalisar domin komawa bakin aikinta.

Ana iya tuna cewa mako gabanin komawarta ne Sanata Natasha ta rubuta wa Majalisar Dattawan wasiƙa, wadda ta bayyana a niyyarta ta dawowa aiki bayan dakatarwa na tsawon wata shida, amma majalisar ta ce ta ɗan jira tukuna.

A watan Fabrairu ne dai tankiya ta ɓarke a zauren Majalisar Dattawa tsakanin shugaban majalisar da Sanata Natasha, lamarin dai ya kai ga har Akpabio ya umarci ɗaya daga cikin masu yi wa sandan majalisar hidima da ya fitar da ita daga zauren majalisar, kuma daga bisani aka dakatar da ita na tsawon wata shida.

Wannan lamarin ya kai ga har Sanata Natasha ta yi kira ga Majalisar Ɗinkin Duniya da ta hukunta Majalisar Dattawan Najeriya game da dakatarwar da aka yi mata.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *