Nijeriya Za Ta Fara Ɗaukar Mataki Kan ‘Yan Ƙasashen Ƙetare Da Bizarsu Ta Ƙare

[ad_1]

Daga ranar 1 ga Oktoba, 2025, hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya (NIS) za ta fara ɗaukar mataki a duk faɗin ƙasar kan ‘yan ƙasashen ƙetare da suka tsallake kwanakin bizarsu ko kuma suka saɓa ka’idojin shigowa ƙasar.

Dokar za ta fara aiki akan waɗannan rukunin ‘yan ƙasashen wajen da suka haɗa da:

Masu riƙe da bizar zuwa ziyara (VoA), bizar kasuwanci da kuma bizar ‘yancin zama (CERPAC).

‘Yan ƙasashen ƙetare da suka karya dokar shige da fice ta Nijeriya za su fuskanci hukunci, wanda zai iya haɗawa da tara, kora, ko kuma yiwuwar hana sake shigowa Nijeriya nan gaba.




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *