Kundin Tsarin Mulkin Nijeriya Bai Yadda Da Tauye Haƙƙin Addini Ba – Minista

[ad_1]


Ministan Harkokin Waje, Yusuf Tuggar, ya ce kundin tsarin mulkin ƙasar ba ya goyon bayan wani nau’i na zalunci ko wariyar addini.

Tuggar ya faɗi haka ne a birnin Berlin na ƙasar Jamus bayan Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi barazanar ɗaukar matakin soja a kan Nijeriya bisa zargin kisan Kiristoci.

“Ba zai yiwu gwamnati a kowane mataki ta goyi bayan zalunci ba,” in ji Tuggar.

Ya bayyana cewa Nijeriya ƙasa ce da ke cike da bambance-bambancen addinai, kuma matsalar tsaro na shafar Musulmi da Kiristoci baki ɗaya, don haka zargin cewa ana zaluntar Kiristoci kaɗai ba gaskiya ba ne.

Tuggar ya kuma gargaɗi masu ƙoƙarin raba Nijeriya ta fuskar addini, cewa hakan na iya haifar da rikici irin na Sudan.

Ya jaddada cewa Nijeriya tana da cikakken ’yancin addini da bin doka, tare da kiran maganganun Trump a matsayin marasa tushe.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *