Girgizar ƙasa ta kashe mutum 610 a Afghanistan

[ad_1]



Aƙalla mutum 610 ne suka rasa rayukansu yayin da wasu sama da 1,300 suka jikkata sakamakon girgizar ƙasa mai ƙarfi da ta afku a ƙasar Afghanistan.

Rahotanni daga hukumomi da kafafen watsa labarai na duniya sun ce ibtila’in ya auku ne a yankin gabashin ƙasar Afghanistan, kusa da iyakarta da Pakistan.

Rahoton Hukumar Binciken Ƙasa ta Amurka (USGS) ya bayyana cewa ƙarfin girgizar ƙasar ta kai matakin 6.0, kuma cibiyar ta kasance a wani yanki mai tazarar kilomita 27 daga birnin Jalalabad, inda ake da yawan jama’a kimanin 300,000.

An gano cewa girgizar ta afku a zurfin kilomita takwas kacal daga saman ƙasa, wanda hakan kan ƙara tsananta illarta.

Kamfanin Dillancin Labarai na AP ya rawaito cewa akwai yiwuwar adadin mutanen da suka mutu zai ƙaru yayin da ake ci gaba da binciko gawarwaki da kuma ceton waɗanda ke cikin ɓaraguzan gine-gine.

Haka zalika, New York Times ta ce an ji girgizar a Kabul — babban birnin Afghanistan — da ke tazarar kilomita 160 daga Jalalabad, duk da cewa ba a tabbatar da samun mace-mace a can ba.

Mai magana da yawun gwamnatin Taliban, Zabihullah Mujahid, ya wallafa a shafinsa na X cewa, “Muna cikin alhini kan asarar rayuka da asarar dukiya da wannan girgizar ƙasa ta haddasa a wasu yankunan gabashin ƙasarmu. Jami’ai da mazauna yankin suna ci gaba da aikin ceto.”

Me ke kawo yawon girgizar ƙasa a Afghanistan?

Afghanistan na fuskantar yawan girgizar ƙasa saboda matsayinta na tectonic.

Wannan yanayi ne da ke haifar da fashewar ƙasa akai-akai, musamman a yankunan tsaunuka da ke gabashin ƙasar.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *