Category: Latest News

  • Sin Da Kasashen Afirka Za Su Rubuta Sabon Babin Hakkin Dan Adam Bisa Ci Gabansu

    [ad_1]

    Abiola Issah ita ce matukiyar jirgin kasa ta farko a kasar Nijeriya. A shekarar 2013, ta shiga shirin bayar da horo da kamfanin CCECC na kasar Sin ya shirya game da guraben aikin yi da za a samar ga al’ummar Nijeriya wajen gudanar da layin dogo na birnin Abuja, wanda kamfanin ya dauki nauyin ginawa. Bayan tsawon shekaru biyar, Abiola ta zama matukiyar jirgin kasa ta farko a kasar Nijeriya, har ma tsohon shugaban kasar marigayi Muhammadu Buhari ya gana da ita. Abiola ta ce, kamar sauran mutane irinta da dama, wannan layin dogo ya canja rayuwarta, ta ce, “sufuri ya zama tushen ci gaban kasa. Hadin gwiwar kasashen Afirka da kasar Sin a fannin sufuri, ba kawai ya inganta ababen more rayuwar kasashen ba, ya kuma farfado da tattalin arzikinsu da kuma samar da guraben ayyuka ga al’ummarsu. Matasa irina mun koyi fasahohi har ma mun samu ayyukan yi.”

    Abin da ya faru ga malama Abiola kyakkyawan misali ne da ya shaida yadda ci gaban kasa ya taimaka ga inganta hakkin dan Adam, wato manyan ababen more rayuwa sun sa kaimin bunkasuwar tattalin arzikin kasa, tare da samar da guraben ayyukan yi ga al’ummarta, kuma ta hakan an kyautata rayuwar al’umma, baya ga karewa da inganta hakkin dan Adam.

    Ke nan hakkin rayuwa da kuma hakkin ci gaba sun kasance na farko daga cikin hakkokin dan Adam. Idan babu ci gaban kasa, babu tushen sauran hakkokin dan Adam ke nan. A don haka ne, a gun taron kara wa juna sani tsakanin Sin da kasashen Afirka kan hakkin dan Adam karo na farko da aka gudanar kwanan baya a birnin Addis Ababa, mahalarta taron sama da 200 da suka zo daga kasashen Sin da Afirka kimanin 44, suka yi musayar ra’ayoyi game da batun “hakkin samun ci gaba”. Matsayar da aka cimma a wajen taron ta kuma yi nuni da cewa, ci gaban kasa tushe ne na warware dukkanin matsalolin hakkin dan Adam.

    A hakika, kwarewar kasar Sin a fannin inganta hakkin dan Adam ta hanyar raya ci gaban kasa, tana da muhimmiyar ma’ana ga kasashen Afirka wajen fid da kansu daga kangin talauci da kuma tabbatar da hakkin dan Adam. A game da hakan, Prof. Melha Rout Biel, shehun malami a cibiyar nazarin tsare-tsare da manufofi ta kasar Sudan ta Kudu ya yi nuni da cewa, “Kasashen Afirka da Sin dukkansu sun taba fuskantar koma baya sakamakon katsalandan da wasu kasashen suka yi musu. Batun hakkin ci gaba da kasar Sin ke magana a kai, abu ne da ya faru gare mu, don haka, muke goyon bayan kasar Sin wajen kokarin tabbatar da hakkinmu na ci gaba.”

    Har kullum, kasar Sin na dukufa a kan “inganta hakkin dan Adam ta hanyar raya ci gaban kasa”, ta kuma gabatar da shawarar raya kasashen duniya, don “kar a bar wata kasa a baya”, kuma ta hanyar inganta hadin gwiwa a tsakanin kasashe masu tasowa, kasar Sin ta aiwatar da hadin gwiwa da kasashen Afirka a wannan fannin tare da cimma kyawawan nasarori. Misali kasar Sin ta taimaka wajen horar da dimbin kwararru na kasashen Afirka, don inganta kwarewar kasashen wajen tabbatar da ci gabansu. A kwanan nan, layin dogon Mombasa zuwa Nairobi da kamfanin kasar Sin ya gina ya cika kwanaki 3000 da fara aiki, wanda ya rage kudaden jigilar kayayyaki kimanin kaso 40% ga al’ummar wurin, tare da samar musu guraben aikin yi dubu 74, kuma hakan ya tabbatar da hakkin ci gaban al’ummar kasar. Har wa yau, Kasar Sin ta kuma yi gine-ginen ababen samar da makamashi mai tsabta sama da 100 a Afirka, ciki har da tashar samar da lantarki daga karfin ruwa ta Zungeru, wadanda suka samar da karfi ga kasashen Afirka wajen tabbatar da dauwamammen ci gabansu.

    Duk da haka, kasashen yamma sun sha yin amfani da batun hakkin dan Adam a matsayin makami wajen tsoma baki cikin harkokin gidan kasashe masu tasowa. A Afirka, kasashen yamma su kan bayar da gudummawar tattalin arziki bisa gindaya sharuda kan batutuwan hakkin dan Adam, sai dai irin katsalandan da suke yi ta fakewa da batun hakkin dan Adam kan haifar da munanan illoli ga kare hakkin dan Adam a kasashen Afirka. Don haka, a matsayar da aka cimma a gun taron, Sin da kasashen Afirka sun jaddada cewa, suna goyon bayan kasa da kasa su zabi hanyar da ta dace da yanayin da suke ciki, kuma suna masu adawa da siyasantar da batun hakkin dan Adam ko kuma mai da shi tamkar makami.

    A yayin da malama Abiola Issah ke samun horo a kasar Sin, ta taba shiga jirgin kasa mai saurin tafiya na kasar. Ta ce ba ta taba ganin jirgi mai sauri haka ba, kuma fatan ta shi ne, wata rana Nijeriya ma ta samu irin jirgin, kuma ta zama matukiya ta farko ta irin wannan jirgin kasa a gida Nijeriya. A ganina, yayin da ake aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya, tare da tabbatar da sakamakon da aka cimma a gun taron dandalin hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka, burinta zai cika nan bada jimawa ba, kuma Sin da kasashen Afirka za su tabbatar da ci gabansu na bai daya bisa hadin gwiwarsu, a yayin da za su dada kyautata rayuwar al’ummunsu da kuma kara inganta hakkin dan Adam bisa ci gaban kasashensu.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • ’Yan bindiga sun kashe mutum ɗaya, sun sace ɗan kasuwa a Kaduna

    [ad_1]



    ’Yan bindiga sun kai hari garin Hunƙuyi da ke Ƙaramar Hukumar Kudan, a jihar Kaduna, inda suka kashe mutum ɗaya tare da sace wani ɗan kasuwa.

    Mutanen yankin sun ce maharan sun kai hari  ne da misalin ƙarfe 12:30 na dare.

    Maharan sun shiga yankin ne ta ɓangaren Katsina ɗauke da bindigogi, inda suka dinga harbi a sama.

    Sun harbe wani mutum mai suna Aminu Shehu har lahira, sannan suka yi awon gaba da wani ɗan kasuwa mai suna Alhaji Shehu Dakin.

    Majiyoyi, sun bayyana cewa maharan sun yi amfani da wayar Alhaji Shehu wajen kiran iyalansa, inda suka nemi kuɗin fansa Naira Miliyan 100.

    Wasu mazauna yankin sun ce wannan hari ya tayar musu da hankali tare da sanya su cikin fargaba.

    Sun roƙi gwamnati da hukumomin tsaro su kai musu ɗauki cikin gaggawa.

    Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Kaduna, ASP Mansir Hassan, ya ci tura, domin ba ya ɗaukar waya har zuwa lokacin hada wannan rahoto.


    [ad_2]

    Source link

  • ’Yan bindiga sun wani kashe mutum, sun sace ɗan kasuwa a Kaduna

    [ad_1]



    ’Yan bindiga sun kai hari garin Hunƙuyi da ke Ƙaramar Hukumar Kudan, a jihar Kaduna, inda suka kashe mutum ɗaya tare da sace wani ɗan kasuwa.

    Mutanen yankin sun ce maharan sun kai hari  ne da misalin ƙarfe 12:30 na dare.

    Maharan sun shiga yankin ne ta ɓangaren Katsina ɗauke da bindigogi, inda suka dinga harbi a sama.

    Sun harbe wani mutum mai suna Aminu Shehu har lahira, sannan suka yi awon gaba da wani ɗan kasuwa mai suna Alhaji Shehu Dakin.

    Majiyoyi, sun bayyana cewa maharan sun yi amfani da wayar Alhaji Shehu wajen kiran iyalansa, inda suka nemi kuɗin fansa Naira Miliyan 100.

    Wasu mazauna yankin sun ce wannan hari ya tayar musu da hankali tare da sanya su cikin fargaba.

    Sun roƙi gwamnati da hukumomin tsaro su kai musu ɗauki cikin gaggawa.

    Ƙoƙarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Kaduna, ASP Mansir Hassan, ya ci tura, domin ba ya ɗaukar waya har zuwa lokacin hada wannan rahoto.


    [ad_2]

    Source link

  • ACReSAL ya tallafa wa manoma da buhunan iri 6,220 a Gombe

    [ad_1]



    Shirin Agro-Climatic Resilience in Semi-Arid Landscapes (ACReSAL) ya raba wa ƙungiyoyin manoma 47 a Jihar Gombe, buhunan iri na zamani 6,220 don bunƙasa harkar noma.

    An gudanar da rabon ne yayin taron kwanaki biyar na masu ruwa da tsaki kan kula da manyan koguna na Gongola, Gali-Lamurde da Hawal-Kilunga, wanda yake ɗaya daga cikin muhimman ayyukan ACReSAL a Najeriya.

    Shugaban shirin a Jihar Gombe, Dokta Sani Adamu Jauro, ya ce Gwamna Inuwa Yahaya ya nuna jajircewa wajen tallafa wa manoma ta hanyar shirin.

    Ya ƙara da cewa an samu nasarori kamar shuka bishiyoyi a dukkanin ƙananan hukumomi 11, rage zaizayar ƙasa da kuma kare muhalli.

    Kwamishinan Noma da Kiwo na jihar, Barnabas Malle, wanda Ibrahim Sajo ya wakilta, ya yaba wa shirin tare da shawartar manoma da su yi amfani da irin wajen noma.

    Ya ce gwamnati ta riga ta fara sayar da taki mai rangwame don sauƙaƙa wa manoma.

    Shugaban Kungiyar Manoma (AFAN) a Jihar, Alhaji Ahmed Modibbo Nafada, ya bayyana tallafin a matsayin babban taimako musamman ga shirin noman rani.

    Ya kuma yaba da ƙoƙarin gwamnati wajen rage rikicin manoma da makiyaya a jihar.

    A nata ɓangaren, Sakatariyar Ƙungiyar Mata Manoma (SWOFON) reshen Gombe, Hannatu Iliya Yila, ta ce mambobinsu sama da 5,000 za su amfana da shirin.

    Ta kuma roƙi gwamnati da sauran masu ruwa da tsaki da su ƙara tallafa wa mata manoma da taki da magungunan kashe ƙwari.


    [ad_2]

    Source link

  • Babu ɗaya daga cikin buƙatunmu da gwamnati ta aiwatar — Shugaban ASUU

    [ad_1]



    Shugaban Ƙungiyar Malaman Jami’o’i ta Najeriya (ASUU), Farfesa Chris Piwuna, ya ce Gwamnatin Tarayya ba ta aiwatar da ɗaya daga cikin yarjejeniyar da ta ƙulla da ƙungiyar ba.

    Ya bayyana haka ne a ranar Laraba yayin hira da gidan talabijin na Trust TV.

    Farfesa Piwuna, ya ce ASUU a koyaushe na zaɓar tattaunawa da jami’an gwamnati a matsayin mafita.

    Amma duk da cewa sun cimma matsaya kan batutuwa masu muhimmanci kamar kuɗaɗen gudanarwa, albashi, ’yancin malamai, ‘yancin jami’o’i, da sake duba wasu dokoki, ba a ɗauki mataki kan kowanne ba.

    “Babu saɓani a tsakaninmu da tawagar gwamnati,” in ji shi.

    “Mun amince kan abubuwa da dama, sai dai shugabanninsu, Ma’aikatar Ilimi da Gwamnatin Tarayya ba su ɗauki mataki kan kowanne ba.”

    Ya danganta yawan ficewa daga Najeriya da malamai da likitoci ke yi saboda ƙarancin albashi da mummunan yanayi da suke ciki.

    A asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos inda yake aiki, ya ce aƙalla likitoci 20 sun bar aiki cikin shekara biyu.

    “Yanayin daidai yake da na malaman jami’a. Idan ƙarancin albashi ne ke sa mutane barin aiki, me ya sa ba za a ƙara albashi a riƙe su ba?” ya tambaya.

    Ya ƙara da cewa ƙasashe da dama a Afirka suna ɗaukar malaman Najeriya aiki.

    “A Uganda, a cikin jami’a guda ɗaya za ka iya samun malamai ’yan Najeriya sun kai 20,” in ji shi.

    Shugaban ASUU ya kuma nuna damuwa kan mummunan yanayin kayan aiki a jami’o’in Najeriya, inda ya ce hakan na daga cikin dalilan da ya sa ba sa samun matsayi mai kyau a duniya.

    Ya ce daga cikin jami’o’i 333 da faɗin Najeriya, guda biyar ne kaɗai ke cikin jirin manyan jami’o’i 1,000 a nahiyar Afirka.

    Ya ce malamai ba sa jin daɗin tafiya yajin aiki, amma gwamnati na tilasta musu hakan saboda rashin ɗaukar mataki.

    “Yajin aiki yana shafarmu, iyalanmu, da ɗalibanmu. Amma idan gwamnati ba ta yi komai ba, harkar ilimi za ta ci gaba da taɓarɓarewa.”

    Ya yi kira ga kafafen yada labarai, iyaye, ƙungiyoyi, sarakuna da shugabannin addinai da su haɗa kai wajen nema wa ɓangaren ilimi sauyi a Najeriya.

    “Wannan ba batun ASUU ne kaɗai ba. Muna fafutukar samun ingantaccen tsari ne, da kyakkyawar makoma, da kuma alheri ga ƙasarmu,” a cewarsa.


    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata

    [ad_1]

    Gwamnan Jihar Imo, Sanata Hope Uzodimma, ya amince da Naira 104,000 a matsayin sabon mafi ƙarancin albashin ma’aikatan gwamnati, wanda ya zamo shi ne mafi yawan albashi a Jihohin Nijeriya.

    Gwamnan ya sanar da hakan ne a daren Talata a lokacin da yake ganawa da shugabannin ƙungiyoyin ƙwadago a gidan gwamnatin jihar da ke Owerri.

    Rahoton Hukumar Dillancin Labarai ta Nijeriya (NAN) ya ce, Uzodimma ya bayyana cewa ƙarin albashin na nuna yadda gwamnatinsa ke kula da jin daɗin ma’aikata da bunƙasar tattalin arziƙi.

    Albashin ya tashi daga Naira 76,000 zuwa Naira 104,000.

    Haka kuma, albashin likitoci ya ƙaru daga Naira 215,000 zuwa Naira 503,000, sannan malaman jami’a da manyan makarantu za su riƙa samun Naira 222,000 maimakon Naira 119,000.

    Uzodimma ya ce ƙarin albashi zai inganta rayuwar ma’aikata, sannan ya bunƙasa tattalin arziƙin jihar.

    Ya kuma bayyana cewa kuɗaɗen shiga na cikin gida sun ƙaru daga Naira miliyan zuwa sama da Naira biliyan uku a kowane wata, yayin da bashin jihar ya ragu daga sama da Naira biliyan 280 a shekarar 2020 zuwa Naira biliyan 100.

    Ya yaba wa Shugaba Bola Tinubu bisa cire tallafin mai, yana cewa duk da ya jawo tsadar rayuwa, amma ya ƙara yawan kuɗin da ake raba wa jihohi kuma ya bai wa gwamnati damar yin sauye-sauye.

    Gwamnan ya ƙara da cewa daga ranar 27 ga watan Agusta, gwamnati za ta fara biyan kashin ƙarshe na kuɗaɗen fansho da ake bai wa tsoffin ma’aikata, wanda jimillarsa ya kai Naira biliyan 16.

    A nasa martanin, shugaban Ƙungiyar Ƙwadago (NLC) a Jihar Imo, Uchechigemezu Nwigwe, ya ce sabon albashin babban nasara ne ga dukkanin ma’aikata a jihar.

    Ya bayyana cewa gwamnan ya ceci ma’aikata daga matsin tattalin arziƙi, kuma ya sanya Imo cikin jihohin da ke da albashi mafi tsoka a Nijeriya.

    Nwigwe ya yi alƙawarin cewa ma’aikata za su saka wannan alheri ta hanyar yin aiki da ƙwazo da inganci.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • ‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

    [ad_1]

    Aƙalla mutum takwas ne suka rasu, yayin da wasu da dama suka jikkata a harin ‘yan bindiga guda biyu da suka kai ƙananan hukumomin Kauru da Kudan a Jihar Kaduna.

    A Kauru, ‘yan bindigar sun kutsa cikin Ungwan Rimi da safiyar ranar Litinin, inda suka fara harbin jama’a tare da kashe mutane.

    Shugabannin al’umma sun ce rikicin ya samo asali ne daga wani rikici a Jihar Filato wanda ya bazu zuwa Kauru.

    A wani hari daban, ‘yan bindiga sun kashe mutum ɗaya sannan suka sace wani attajiri mai suna Shehu Hussein a Ungwan Fulani, a ƙaramar hukumar Kudan.

    Gwamnatin Jihar Kaduna ta yi tir da harin, inda ta ce hare-haren na daga cikin waɗanda da ake samu a yankunan a baya-bayan nan.

    Gwamna Uba Sani ya umarci jami’an tsaro da su kamo waɗanda suka aikata laifin tare da wanzar da zaman lafiya.

    Jami’ai sun ce jihar ta samu zaman lafiya sosai cikin shekaru biyu da suka gabata sakamakon Kaduna Peace Model, wanda ya rage rikice-rikice tare da sake ba da damar zuwa gonaki da kasuwanni a wuraren da aka daɗe ana fama da rikici.

    Sai dai sun yi gargaɗin cewa rashin tsaro daga jihohin maƙwabta na yawan zuwa cikin Kaduna, don haka ana buƙatar gwamnatoci na jihohi su haɗa kai domin kawo ƙarshen irin waɗannan hare-hare a nan gaba.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • ’Yan bindiga sun sace ma’aurata da ’yarsu mai shekara ɗaya a Katsina

    [ad_1]



    Maharan da ake kyautata zaton ’yan bindiga ne a ranar Talata sun sace mata da miji tare da ’yarsu mai shekara ɗaya a cikin birnin Katsina.

    An dai kai harin ne a gidan ma’uratan, Anas Ahmadu, da matarsa Halimatu, da kuma ’yarsu Jiddah a Unguwar Kanada a yankin Ƙofar Ƙaura a Katsina.

    Rahotanni sun ce an kai harin ne wajen misalin ƙarfe 3:00 na daren Litinin inda maharan suka sace magidancin mai suna Malam Anas tare da matarsa mai suna Halimatu ​​da ’yarsa.

    Bayanai sun kuma nuna wani dan bangar da yayi ƙoƙarin kai musu ɗauki ya rasa ransa.

    Sai dai wasu mazauna unguwar sun ce tun da farko sun yi zargin wasu mutane biyu da aka ga suna zirga-zirga a yankin har suka sanar da ’yan bangar da ke unguwar.

    Sai dai ko da aka neme su ba a gan su ba, sun buya tun da suka lura jama suna zargin su.

    Rundunar ’Yan Sandan Jihar ta tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da Kakakinta, DSP Abubakar Sadiq ya fitar.

    Ya ce wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun ƙaddamar da harin a ranar Talata a gidan wani Anas Ahmadu, mai shekaru 33, a unguwar Filin Kanada a cikin garin Katsina, inda suka yi garkuwa da shi.

    Kakakin ya kuma ce maharan sun yi awon gaba da matar mutumin mai suna Halimatu da ’yarsa Jidda Anas.

    Ya tabbatar da cewa, ’yan bindigar sun kuma harbe wani mai suna Abdullahi Muhammad, mai shekaru 25, wanda ke aikin banga, kuma sun tsere daga wurin kafin isowar jami’an ’yan sanda.

    DSP Abubakar ya kuma ce rundunar ta shiga yin bincike don gano maharan da kuma kubutar da wadanda aka yi garkuwar da su.

    Mazauna birnin Katsina dai sun fara nuna damuwarsu kan yadda ’yan bindiga ke karuwa a Jihar wanda ta kai har suna shiga cikin manyan biranen jihar suna kai hare-hare.


    [ad_2]

    Source link

  • DAGA LARABA: Abin Da Ya Sa Wasu Maza Ba Sa Son Haihuwa

    [ad_1]

    Karin fannoni

    • Najeriya a Yau

    • Daga Laraba



    A duk lokacin da aka ɗaura aure, wata addu’a da ’yan uwa da abokan arziki kan yi ita ce “Allah Ya kawo ƙazantar ɗaki”.

    A al’adance, ɗaya daga cikin manyan dalilan yin aure shi ne samun haihuwa.
    Sai dai a wasu lokuta, wasu mazan kan nuna a fili ba su da muradin hakan.

    NAJERIYA A YAU: Ci Gaban Da Harshe Da Al’adun Hausa Suka Samu A Shekaru 10

    DAGA LARABA: Yadda wasu tsare-tsaren ba da tazarar haihuwa ke yin illa ga mata
    Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi duba ne kan waɗannan mazan da ba sa son haihuwa da kuma dalilan su.

    Domin sauke shirin, latsa nan


    [ad_2]

    Source link

  • ‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

    [ad_1]

    Rundunar ‘Yansandan Nijeriya ta ce ta ceto wasu mutane biyar da aka sace tare da tarwatsa gungun masu garkuwa da mutane a Jihar Kebbi.

    Kakakin rundunar, Olumuyiwa Adejobi, ya bayyana cewa a ranar 27 ga watan Yuli, 2025, wasu masu garkuwa da mutane sun kai hari garin Sangara a karamar hukumar Shanga, inda suka sace mutum uku.

    Waɗanda suka sace sun haɗa da Muhammad Namata, Gide Namata da Hamidu Namani.

    Sai dai jami’an tsaro tare da ‘yan sa-kai sun bi sahunsu zuwa tsaunukan Shanga, inda suka yi musayar wuta da su.

    Masu laifin sun tsere cikin daji da harbin bindiga, sannan an ceto mutanen uku.

    Haka kuma, a wani samame daban da rundunar ta kai a ranar 15 ga watan Agusta, 2025, ‘yansanda a ƙaramar hukumar Danko/Wasagu sun yi artabu da ‘yan bindiga a kusa da garin Dankade.

    Sun ceto mutum biyu da aka sace; Tukur Bello da Isyaka Abubakar, waɗanda aka sace a dajin Gairi na Jihar Zamfara a ranar 9 ga watan Agusta yayin da suke kiwon shanu.

    ‘Yansanda sun ce sun ƙwato makamai da harsasai daga hannun ‘yan bindigar, tare da alƙawarin ci gaba da yaƙi da masu garkuwa da mutane a faɗin ƙasar nan.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link