Category: Latest News

  • A ɗora min laifin hatsarin jirgin ƙasan Kaduna zuwa Abuja — Shugaban NRC

    [ad_1]



    Shugaban hukumar kula da jiragen ƙasa ta Nijeriya (NRC), Kayode Opeifa, ya ce ya ɗauki alhakin hatsarin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna da ya auku a ranar Talata.

    Aminiya ta ruwaito cewa hatsarin ya auku ne da misalin ƙarfe 11 na safe bayan jirgin ya taso daga Abuja zuwa Kaduna.

    Da yake zantawa da gidan talabijin na Channels a yau Laraba, Opeifa ya ce ba za su yi ƙasa a gwiwa ba wajen binciken abin da ya haddasa lamarin.

    “Bayan neman gafarar ’yan Najeriya, a matsayina na shugaban hukumar, na ɗauki alhakin duk abin da ya faru,” in ji shi.

    “Ba za mu ɗebe tsammanin faruwar irin wannan lamari ba, amma duk lokacin da hakan ta kasance, tana ƙara mana fahimtar wuraren da suke buƙatar mu inganta.”

    Hukumar agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) ta tabbatar da cewa mutum bakwai suka ji rauni bayan aukuwar hatsarin waɗanda tuni sun samu kulawar gaggawa daga likitoci.

    A jiyan ne dai NRC ta sanar da dakatar da sufurin jirgin ƙasan da ke jigila tsakanin Kaduna da Abuja har zuwa lokacin da za ta kammala bincike kan musabbabin faruwar lamarin.


    [ad_2]

    Source link

  • Gwamnan Katsina Ya Dawo Gida Domin Ziyara Ga Al’ummar Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Wa Hari A Malumfashi

    [ad_1]

    Gwamnan jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Radda ya rage hutun da ya tafi domin ziyartar al’ummar Martau da ke karamar hukumar Malumfashi, wanda a baya-bayan nan ya sake fuskantar hare-haren ‘yan bindiga.

    Gwamnan ya isa yankin ne da yammacin Larabar nan, inda nan take ya fara duba barnar da maharan suka yi, inda suka kashe mazauna yankin, da kona gidaje da matsugunansu.

    Radda, wanda a fili ya nuna kaduwarsa kan irin barnar da aka yi, ya ce, ya zo ziyarar ne don jajanta wa wadanda abin ya shafa da kuma tabbatar musu da cewa gwamnati ba za ta yi watsi da su ba a lokacin da suke bukatarta.

    Ya yi alkawarin cewa, gwamnatinsa za ta kara hada kai da hukumomin tsaro domin dawo da zaman lafiya, tare da samar da kayayyakin agaji da tallafi ga wadanda abin ya shafa.

    Majiyoyin yankin sun ce al’ummar yankin sun sha fama da hare-hare akai-akai a ‘yan makonnin da suka gabata, lamarin da ya tilastawa mazauna yankin kauracewa gidajensu.

    Ku tuna cewa, Gwamna Radda a ranar 18 ga Agusta, 2025 ya bar kasar don hutun makonni uku domin duba lafiyarsa a kasar waje.

    Gwamnan ya samu rakiyar manyan jami’an gwamnati da shugabannin hukumomin tsaro na jihar da kuma kungiyoyin bayar da agajin gaggawa ga al’umma.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Kasar Sin Ta Yi Watsi Da Kiran Shiga Tattaunar Kwance Damarar Nukiliya Tare Da Amurka Da Rasha

    [ad_1]

    Ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ta ce bai dace ba, kuma bai kamata a nemi kasar Sin ta shiga tattaunawar kwance damarar makaman nukiliya tare da Amurka da Rasha ba.

    Kakakin ma’aikatar Guo Jiakun ne ya bayyana haka, yayin taron manema labarai na yau Laraba, lokacin da yake mayar da martani game da rahotannin dake cewa, a baya-bayan nan shugaban Amurka Donald Trump ya ce kasarsa da Rasha suna tattauna batun rage makamansu na nukiliya, kuma yana fatan kasar Sin ma za ta shiga tattaunawar.

    A cewar Guo Jiakun, ko kadan, karfin nukliyar Sin bai kama kafar na Amurka ba. Kuma manufarsu kan nukiliya da ma yanayinsu na tsaro ta fuskar yanki da barazanar da za su iya fuskanta, sun sha bamban da juna.

    Da yake bayyana Sin a matsayin mai bin manufar kaucewa fara amfani da makaman nukiliya da yadda manufarta ta nukiliyar ke mayar da hankali kan kare kai, kakakin ya ce kasar Sin za ta ci gaba da tabbatar da karfinta na nukiliya ya tsaya a matsakaicin mataki da ake bukata na tsaron kasa, kuma ba za ta taba shiga takarar makamai da wata kasa ba. (Fa’iza Mustapha)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Sin Ta Sanar Da Cimma Nasarar Dashen Huhun Alade A Jikin Bil’Adama

    [ad_1]

    A karon farko kwararrun likitocin kasar Sin sun yi nasarar dasa huhun alade da aka sauya kwayoyin halittarsa a jikin wani mutum. Wata makala mai kunshe da binciken kimiyya da aka wallafa a mujallar “Nature” ce ta tabbatar da hakan, inda bayanan suka nuna cewa, duk da kasancewar huhu bangaren jiki mai sarkakiya, amma likitocin da suka yi aikin sun cimma nasarar da ake ganin mataki ne na kaiwa ga gwajin aikin nan gaba ga marasa lafiya dake da bukata.

    An ce wanda aka yiwa dashen huhun matashi ne mai shekaru 39 a duniya, wanda kwakwalwarsa ta riga ta mutu, kuma an yiwa huhun na alade sauye-sauyen yanayin halitta shida, domin ya dace da yanayin jikin dan’adam kafin dasawa mara lafiyan. Daga bisani likitocin da suka yi aikin sun ce mara lafiyan ya shafe kwanaki tara jikinsa na aiki da huhun, ba tare da jikinsa ya bijirewa huhun ko ya kamu da wata cuta ba.

    Daya daga mawallafa binciken He Jianxing, ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Xinhua cewa, sakamakon karuwar bukatar dashen sassan jiki a duniya, dabarar dashen wasu sassan jikin wasu halittu a jikin bil’adama na iya zama hanyar magance matsalar karancin sassan jiki da wasu ke bayarwa domin dasawa marasa lafiya. Ya ce nasarar da aka cimma a wannan karo ta zamo muhimmin mafari a fannin dashen sassan jikin wasu halittu ga marasa lafiya. (Mai Fassara: Saminu Alhassan)




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • ASUU: Malaman Jami’ar FUK sun yi zanga-Zanga kan rashin cika musu alƙawura

    [ad_1]



    Ƙungiyar Malaman Jami’a (ASUU) reshen Jami’ar Tarayya Kashere (FUK), ta yi zanga-zangar lumana, inda ta buƙaci Gwamnatin Tarayya ta aiwatar da yarjejeniyar da suka yi da sauran buƙatunsu da ba a cika ba.

    Zanga-zangar ta fara ne daga ofishin ƙungiyar, ta bi ta ginin shugaban jami’ar, sannan ta ƙare a bakin ƙofar shiga makarantar.

    Shugaban ASUU na jami’ar, Dakta Shehu El-Rasheed, ya ce gwamnati ta kasa cika alƙawuran da suka jawo yajin aikin watanni takwas a shekarar 2022.

    Ya ce har yanzu ba a biya malamai albashin baya ba, haka kuma babu ƙarin albashi na tsawon shekaru.

    Ya ja hankalin gwamnati cewa hakan na iya haifar da damuwa a harkar ilimi a jami’ar.

    Wani malami, Dakta Muhammad Sheriff Ramadan, ya ce ƙarancin albashi na tilasta wa malamai yin wasu ayyuka don samun ƙarin kuɗin shiga.

    Ya buƙaci gwamnati ta ƙara albashi domin inganta rayuwarsu da harkar ilimi.

    Wasu ɗaliban jami’ar, Dung Hannatu Yakubu da Precious Moses Ayomide, sun bayyana fargabarsu cewa rashin jituwar ASUU da gwamnati na iya jawo tsaikon karatu da kuma ƙara musu shekaru kafin kammala karatunsu.


    [ad_2]

    Source link

  • ASUU: Malaman Jami’ar Kashere sun yi zanga-Zanga kan rashin cika musu alƙawura

    [ad_1]



    Ƙungiyar Malaman Jami’a (ASUU) reshen Jami’ar Tarayya Kashere (FUK), ta yi zanga-zangar lumana, inda ta buƙaci Gwamnatin Tarayya ta aiwatar da yarjejeniyar da suka yi da sauran buƙatunsu da ba a cika ba.

    Zanga-zangar ta fara ne daga ofishin ƙungiyar, ta bi ta ginin shugaban jami’ar, sannan ta ƙare a bakin ƙofar shiga makarantar.

    Shugaban ASUU na jami’ar, Dakta Shehu El-Rasheed, ya ce gwamnati ta kasa cika alƙawuran da suka jawo yajin aikin watanni takwas a shekarar 2022.

    Ya ce har yanzu ba a biya malamai albashin baya ba, haka kuma babu ƙarin albashi na tsawon shekaru.

    Ya ja hankalin gwamnati cewa hakan na iya haifar da damuwa a harkar ilimi a jami’ar.

    Wani malami, Dakta Muhammad Sheriff Ramadan, ya ce ƙarancin albashi na tilasta wa malamai yin wasu ayyuka don samun ƙarin kuɗin shiga.

    Ya buƙaci gwamnati ta ƙara albashi domin inganta rayuwarsu da harkar ilimi.

    Wasu ɗaliban jami’ar, Dung Hannatu Yakubu da Precious Moses Ayomide, sun bayyana fargabarsu cewa rashin jituwar ASUU da gwamnati na iya jawo tsaikon karatu da kuma ƙara musu shekaru kafin kammala karatunsu.


    [ad_2]

    Source link

  • Nijeriya Za Ta Ɗaukaka Da Fasahar Ƙere-ƙere Da Tattalin Abinci

    [ad_1]

    Shugaba Bola Tinubu ya yi alƙawarin hanzarta aiwatar da ci gaban Nijeriya ta hanyar amfani da fasahar kere-kere da tattalin abinci don samun nasarori irin na sauran ƙasashe masu tasowa kamar Brazil.

    A yayin da yake jawabi a ranar Talata a lokacin da ya gana da wasu ‘yan Nijeriya mazauna kasar Brazil, shugaba Tinubu ya jaddada kudirin gwamnatinsa na kawo sauyi ta hanyar kere-kere, gyare-gyare, da kuma samar da ci gaba mai dorewa.

    “Dole ne mu sanya Nijeriya a gaba wajen ci gaban Afirka, ta hanyar amfani da fasahar kere-kere, tattalin abinci, da jajircewa wajen sauya irin kaddararmu,” in ji Tinubu a wata sanarwa da kakakinsa, Bayo Onanuga ya fitar.

    A cewar Tinubu, Nijeriya da Brazil a wani lokaci sun taba zama a matsayi daya. “Amma duba Brazil a yau, fasaharta da tsarin tattlin abincinta. Dole ne mu tambayi kanmu: menene suke da shi wanda ba mu da shi? Muna da ilimi, makamashi, da matasa. Muna da duk abin da muke bukata. Yanzu, dole ne mu tashi tsaye mu yi aiki.”

    Da yake yabawa al’ummar Nijeriya mazauna kasashen waje, Tinubu ya bukace su da su dauki kansu a matsayin masu ruwa da tsaki wajen gina sabuwar Nijeriya mai tushe a fannin fasahar kirkire-kirkire, al’adu, da kuma aiki tare.

    Ya amince da matsalolin da ‘yan kasar ke fuskanta sakamakon sauye-sauyen tattalin arziki da ake ci gaba da yi, yana mai jaddada cewa wadannan muhimman matakai ne na tabbatar da ci gaban kasa da za a gani nan gaba.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Dilan ƙwaya ya shiga hannu a Borno

    [ad_1]



    Rundunar ’Yan Sandan Jihar Borno, ta kama wani mutum da ake zargi da dillancin miyagun ƙwayoyi a Ƙaramar Hukumar Bayo.

    An cafke shi ne ranar 23 ga watan Agusta, 2025, yayin wani samame da ’yan sanda suka kai tare da haɗin gwiwar sashen leƙen asiri.

    Kakakin rundunar, ASP Nahum Kenneth Daso, ya ce an kama wanda ake zargin mai suna Nasiru Ibrahim da fakiti 25 na tabar wiwi.

    Ragowar ƙwayoyin da aka samu a wajensa sun haɗa da fakiti 34 na ƙwayar Exzol, da kuma ƙwayar D5 guda 600.

    An miƙa shi tare da kayan da aka ƙwato zuwa sashen binciken manyan laifuka na jihar domin ci gaba da bincike kafin gurfanar da shi a gaban kotu.

    Rundunar ta jaddada aniyarta na yaƙi da miyagun laifuka, musamman ta’ammali da ƙwayoyi, waɗanda ke jawo matsalolin tsaro a cikin al’umma.


    [ad_2]

    Source link

  • Ambaliya: Gwamnatin Yobe ta samar wa magidanta 250 matsugunin wucin gadi

    [ad_1]



    Gwamnatin Jihar Yobe ta kwashe magidanta sama da 250 daga Garin Kolo da ke Ƙaramar Hukumar Nangere, zuwa sabon matsuguni bayan ambaliyar ruwa ta lalata musu gidaje.

    An ƙaddamar da sabon matsugunin ne ƙarƙashin jagorancin Gwamna Mai Mala Buni domin kare rayukan waɗanda abin ya shafa.

    Babban sakataren Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar (YOSEMA), Alhaji Idi Jidawa, ya bayyana cewa an gina gidajen wucin gadi guda 22 domin amfanin mutanen.

    Haka kuma, an samar da rijiya, banɗakunan wucin gadi guda biyar, da motar ɗaukar marasa lafiya.

    Jami’an tsaro da suka haɗa da ’yan sanda da jami’an Sibil Difens na tabbatar da tsaron jama’a a wajen.

    Waɗanda suka samu rauni kuma an tura su zuwa Babban Asibitin Nangere don samun kulawa.

    Magidantan da ambaliyar ta shafa sun samu kayan abinci, inda gwamnatin ke shirin ƙara ba su wani tallafi.

    Jidawa, ya ƙara da cewa gwamna Buni na da niyyar ganin duk wanda aka raba da gidansa ya koma cikin kwanciyar hankali.

    Ya kuma gode wa Sarkin Tikau, ƙaramar hukumar Nangere, ma’aikatar lafiya, RUWASA, jami’an tsaro, da saurasu wajen ganin an cimma wannan nasara.

    Hukumar YOSEMA ta roƙi masu hannu da shuni da ƙungiyoyin agaji da su ci gaba da tallafa wa wannan shiri na taimakon gaggawa.


    [ad_2]

    Source link

  • Amurka ta ɗaure basaraken Osun kan zamba a tallafin COVID-19

    [ad_1]



    Wata kotu a Ƙasar Amurka, ta yanke wa Sarkin Ipetumodu, Oba Joseph Oloyede, daga Jihar Osun, hukuncin ɗaurin shekara huɗu da rabi a gidan yari saboda samun sa da laifin zamba a tallafin COVID-19.

    Alƙalin kotun, Christopher Boyko ne, ya yanke wa Sarkin mai shekara 62 a duniya hukunci a ranar 26 ga watan Agusta, 2025.

    Sarkin ɗan ƙasar Amurka ne, da ke zaune a Ohio.

    Bayan ya fito daga gidan yari, zai yi shekara uku ƙarƙashin kulawa, sannan dole ne ya biya sama da dala miliyan 4.4.

    Kotun ta kuma ƙwace gidansa da ke Ohio da kusan dala 100,000 da aka samu daga cikin kuɗaɗen da aka yi bincike a kansu.

    Waɗanda suka shigar da ƙara sun ce Oloyede tare da abokinsa, Edward Oluwasanmi, sun karkatar da kuɗaɗe wanda gwamnatin Amurka ta samar na rance don taimaka wa kamfanoni a lokacin annobar COVID-19.

    Daga watan Afrilun 2020 zuwa Fabrairun 2022, sun gabatar da takardun bogi don samun rance ta hanyar U.S. Small Business Administration (SBA).

    Oloyede, ya mallaki kamfanoni da ƙungiya mai zaman kanta, yayin da Oluwasanmi ya mallaki kamfanoni guda uku.

    Oloyede, ya shirya takardun bogi 38 da suka ba shi damar samun dala miliyan 4.2.

    Haka kuma, ya taimaka wa wasu abokansa wajen samun rancen, tare da karɓar kashi 15 zuwa 20 daga cikin kuɗin da suka samu a ɓoye, ba tare da ya biya haraji ba.

    An gano cewa sun yi amfani da kuɗin wajen sayan filaye, gina gidaje, da kuma motoci masu tsada.

    Oluwasanmi, wanda shi ma yake da shekara 62, an yanke masa hukuncin ɗaurin shekara biyu da watanni uku gidan yari a watan Yuli.

    Sannan kotun ta umarci ya dawo da sama da dala miliyan 1.2.

    FBI da wasu hukumomi ne suka gudanar da bincike tare da gano yadda aka tafka zamba a tallafin na COVID-19.


    [ad_2]

    Source link