Hukumar Jiragen Ƙasa ta Nijeriya (NRC) ta dakatar da zirga-zirgar jirgin ƙasa a hanyar Abuja zuwa Kaduna bayan wani jirgi ya yi hatsari a ranar Talata.
Shugaban NRC, Kayode Opeifa, ya shaida wa ’yan jarida a Abuja cewa babu jirgin da zai sake tashi har sai an kammala bincike kuma an tabbatar da tsaro.
Ya ƙara da cewa an riga an mayar wa fasinjojin da abin ya shafa kuɗin tikitinsu.
Opeifa ya bayyana cewa injiniyoyin NRC, jami’an hukumar binciken tsaro ta NSIB, da sauran hukumomi suna wajen da hatsarin ya faru domin gano musabbabin lamarin da kuma ɗaukar matakan kariya a nan gaba.
Ya kuma ƙaryata raɗe-raɗin cewa ana sakaci wajen kula da jiragen ƙasa, yana mai cewa hukumar koyaushe tana bin ƙa’idojin tsaro.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Jagoran marasa rinjaye a Majalisar Dattawa, Abba Moro, ya bayyana cewa ana tattaunawa da Peter Obi da tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan domin su koma jam’iyyar PDP tare da yi mata takarar shugaban ƙasa a 2027.
Moro ya ce wasu daga cikin ‘yan jam’iyyar suna kiran Obi da ya dawo PDP tare da yiwuwar zama ɗan takara.
Haka kuma ya tabbatar cewa ana tattaunawa da Jonathan kan yiwuwar sake tsayawa takara.
Jonathan, wanda ya shugabanci Nijeriya daga 2010 zuwa 2015, ya daina shiga harkokin siyasa tun bayan da Muhammadu Buhari ya kayar da shi.
Obi kuwa ya fice daga PDP a 2022, inda ya tsaya takara a ƙarƙashin jam’iyyar Labour Party a 2023, amma ya zo na uku a zaɓen.
Masu sharhi kan harkokin siyasa na ganin cewa dawowar Jonathan ko Obi na iya sauya tsarin PDP wajen fafatawa da jam’iyyar mai mulki ta APC.
Jonathan na da magoya baya masu tsayi da suka daɗe a PDP, yayin da Obi kuma ya fi jan hankalin matasa.
Sai dai har yanzu akwai tambayoyi kan ko za su amince da wannan kira, da kuma yadda PDP za ta shawo kan matsalolin cikin gida kafin zaɓen fidda gwani.
Zuwa yanzu, babu wanda ya fito fili daga cikinsu ya tabbatar da komawarsa PDP.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Cutar kwalara ta ɓarke a ƙananan hukumomin Gumi da Bukkuyum a Jihar Zamfara, inda ta kashe aƙalla mutum bakwai tare da kwantar da kusan mutum 200 a asibiti.
Ɗan majalisar tarayya mai wakiltar yankin, Hon. Sulaiman Abubakar Gumi, ya ce cutar ta fara tun 10 ga watan Agusta, kuma tana ƙara yaɗuwa.
Ya bayyana cewa rashin tsaftar muhalli da ruwan sama sun taimaka wajen yaɗuwar cutar, musamman a inda ‘yan gudun hijira suke zaune.
Ya yi gargaɗin cewa idan ba a ɗauki matakan gaggawa ba, cutar na iya zama annoba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da aikin gyaran na’urar tiransimita mai gajeren zango (shortwave) ta gidan rediyon Muryar Nijeriya (VON) mai ƙarfin kilowat 250 TX2 a tashar da ke unguwar Lugbe a Abuja.
Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, wanda Babban Sakatare a ma’aikatar, Mista Ogbodo Chinasa Nnam ya wakilta, shi ne ya bayyana hakan a bikin ƙaddamar wanda aka yi a ranar Talata a Abuja.
Idris ya bayyana wannan mataki a matsayin wani “muhimmin lokaci a tarihin Muryar Nijeriya, domin mun fara aikin farfaɗo da tasha mafi girma kuma mafi ƙarfi a nahiyar Afrika wadda yanzu ake sanya mata ingantattun na’urori na zamani da suka dace da fasahar zamani.”
Idris ya gode wa Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu bisa hangen nesan sa da jajircewar sa wajen zamanantar da kayan aikin yaɗa labarai a Nijeriya.
A cewar sa: “Yayin da muke ɗaukar wannan babban mataki na ƙaddamar kwangilar gyara tiransimitar ‘shortwave’ ta Muryar Nijeriya mai ƙarfin kilowat 250, ya dace mu nuna ɗimbin godiyar mu ga Mai Girma Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, GCFR, bisa hangen nesa da jajircewar sa wajen farfaɗo da kuma zamanantar da kayan aikin yaɗa labarai na Muryar Nijeriya.”
Ya kuma tabbatar wa da ‘yan Nijeriya cewa wannan aikin zai sauya yanayin yadda ake yaɗa labarai a ƙasar nan.
Ya ce: “Da zarar an kammala wannan aiki, na’urorin tiransimita na VON da aka farfaɗo da su gaba ɗaya za su sauya yanayin yaɗa shirye-shiryen rediyo na ƙasa, tare da sanya VON a matsayin gagarumar alama mai martaba a duniyar yaɗa labarai ta rediyo baki ɗaya.”
Ministan ya buƙaci kamfanin Confax Nigeria Limited da ke gudanar da kwangilar da ya tabbatar da inganci da kuma kammalawa a kan lokaci, inda ya ce: “Saboda haka ina kira ga ɗan kwangilar da ya tabbatar da ba wai kawai an kammala aikin a cikin lokacin da aka tsara ba, har ma a tabbatar da cewa an kiyaye mafi girman matakan inganci kuma hakan ya fito fili.”
Haka kuma ya umurci ma’aikatan da ke kula da na’urori a VON da su yi aiki da jajircewa da natsuwa wajen kula da wannan aikin.
Ya jaddada cewa ana sa ran gidan rediyon VON zai ci gaba da kiyaye manufar sa ta kasancewa gidan rediyo mai goyon bayan Nijeriya da Afrika baki ɗaya, tare da bayar da sahihan labarai na nasarorin da ke fitowa daga Nijeriya da nahiyar baki ɗaya.
A ƙarshe, Ministan ya ce: “Yanzu ina farin cikin ƙaddamar da kwangilar gyaran na’urar tiransimitar ‘shortwave’ ta Muryar Nijeriya mai ƙarfin kilowat 250.”
Shi dai VON, shi ne gidan rediyon da Gwamnatin Tarayya ta kafa domin bada labarai daga Nijeriya zuwa ƙasashen ƙetare, kwatankwacin gidan rediyon BBC da na Muryar Amurka.
An kafa shi a cikin 1961 a matsayin sashen labaran ƙetare na gidan rediyon NBC, wato wanda ya zama FRCN daga bisani. Firayim Minista na lokacin, Alhaji Sa Abubakar Tafawa Balewa, shi ne ya ƙaddamar da shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Wani nazari da kafar CGTN ta kasar Sin ta gudanar, wanda ya shafi mutane 11,913 daga kasashe sama da 40 ya nuna cewa, kaso 62.1 na mutane a fadin duniya sun yi imanin cewa, kare sakamakon yakin duniya na II abu ne mai matukar muhimmanci wajen tabbatar da odar duniya, inda kimanin kaso 58 daga cikinsu, suka ce odar duniya na tabarbarewa kuma kai tsaye sun bayyana Amurka a matsayin babbar mai haifar da tsaiko a duniya.
Yakin duniya na II wani mummunan lamari ne da dan adam bai taba ganin irinsa ba a tarihi. Kuma shekarun da aka shafe ana gwabzawa da mace-mace da asarar da yakin ya haifar da sadaukarwar da aka yi, dukkansu darasi ne da duniya za ta iya dauka don kaucewa maimaituwar yakin.
Idan zan ba da misali da kasar Sin, la’akari da yadda ta shafe tsawon shekaru 14 tana yaki da Japanawa masu kutse da asarar rayuka miliyan 35, kwatankwacin kaso 1 bisa 3 na jimilar asarar rayukan da aka yi a lokacin, za mu iya cewa ta fi kowa jin jiki yayin yakin, amma kuma ta yi nasara wajen yaki da mulkin danniya da kokarin wanzar da zaman lafiya a duniya. Ta kuma shiga an dama da ita wajen tsara yanayin tafiyar da harkokin duniya cikin lumana kuma bisa doka da adalci, tare da kai wa ga kafa MDD.
Sai dai duk da irin wannan sadaukarwa da aka yi, a halin da ake ciki yanzu, wasu ’yan tsiraru suna kokarin lalata ginshinkin zaman lafiyar duniya da haifar da rarrabuwar kawuna da ingiza rikici tsakanin kasa da kasa ta hanyar yada jita-jita da karairayi da fatali da dokokin kasa da kasa, domin cimma wasu burikansu.
Shin halin ni ’ya su da duniya ta shiga a wancan lokaci bai isa ya zama izina a gare su?
Yakin duniya na II abu ne da ya keta kasashe da iyakoki da launin fata, wanda a karshe ya kawo hadin kai tsakanin kasa da kasa domin wanzar da zaman lafiya da ci gaban duniya. Shekaru 80 bayan samun nasarar yaki da masu danniya, ya kamata a yi waiwaye, a nazarci nasarar da aka samu da kyar, da tsamo hikimomi da dabaru da ma hanyoyin karfafa gina duniya cikin kawanciyar hankali da lumana. Yayin da al’ummomin kasashen duniya ke ganin wasu kasashe na kokarin lalata wannan nasara, ya zama wajibi a tsaya tsayin daka wajen bijire musu, don ganin ba a bar su sun mayar da hannun agogo baya ba. (Fa’iza Mustapha)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni ya kaddamar da shirin dashen bishiyoyi na shekarar 2025 a Damaturu babban birnin jihar.
Gwamna Buni ya kuma yi gargadi game da sare itatuwa ba gaira ba dalili, yana mai jaddada cewa gwamnatin jihar ba za ta amince da ayyukan da za su sanadin kwararowar hamada da lalata muhalli ba.
Da yake jawabi a wurin bikin mai taken: “Shirin Buni na dakile kwararowar hamada” Gwamnan ya jaddada aniyar gwamnatinsa na yaki da kwararowar hamada, da raya gurbatacciyar kasa, da dakile illolin sauyin yanayi.
Ya yi nuni da cewa, tun daga shekarar 2020, gwamnatin jihar Yobe ta dasa miliyoyin itatuwa iri-iri a fadin jihar domin dakile kwararowar hamada daga kudancin Jihar.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
A yau Talata 26 ga wata ne, firaministan kasar Sin, Li Qiang, ya isar da sako zuwa ga Nestor Ntahontuye, don taya shi murnar zama sabon firaministan kasar Burundi.
A sakon nasa, firaminista Li ya bayyana cewa, a ’yan shekarun nan, karkashin jagorancin shugabannin kasashen biyu, wato Xi Jinping da Evariste Ndayishimiye, an cimma manyan nasarori wajen inganta hadin-gwiwar kasashensu a fannoni daban-daban. A yayin taron kolin dandalin tattaunawa kan hadin-gwiwar Sin da Afirka wato FOCAC, wanda aka yi a watan Satumban bara a Beijing, shugabannin biyu sun cimma matsaya daya kan daga matsayin huldar kasashensu, zuwa huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare kuma daga dukkan fannoni, al’amarin da ya kafa alkibla ga ci gaban dangantakarsu.
Firaminista Li ya ce yana fatan kara kokari tare da Nestor Ntahontuye, don aiwatar da muhimman ra’ayoyi iri daya da aka cimma tsakanin shugabannin kasashen biyu, gami da nasarorin da aka samu a wajen taron kolin FOCAC na Beijing, ta yadda nasarorin dangantakar Sin da Burundi za su kara amfana wa al’ummominsu. (Murtala Zhang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen kasa ta Nijeriya (NRC) ta sanar da dakatar da zirga-zirgar jiragen kasa a kan layin dogo na Abuja zuwa Kaduna biyo bayan hatsarin da jirgin ya yi a ranar Talata.
Manajan Darakta na NRC, Kayode Opeifa ne ya sanar da hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a Abuja bayan faruwar lamarin.
Opeifa ya jaddada cewa, an dakatar da zirga-zirgar jiragen har sai an kammala bincike da kuma tabbatar da tsaro, tare da bayyana cewa an shirya mayar da kudade ga duk fasinjojin da wannan lamari ya shafa.
Opeifa ya kara da cewa, tuni tawagar kwararru daga Hukumar, jami’an Hukumar Binciken Tsaro ta Nijeriya (NSIB) da sauran hukumomin da abin ya shafa suka isa wurin domin gano musabbabin wannan matsala da kuma tabbatar da daukar matakan kariya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Da safiyar yau Talata 26 ga watan nan ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da shugaban majalisar dokokin kasar Rasha Vyacheslav Volodin a nan birnin Beijing.
Yayin tattaunawar, shugaba Xi ya bayyana cewa, a mako mai zuwa, Sin za ta gudanar da bikin tunawa da cika shekaru 80 da cin nasarar yakin kin maharan Japan, da kuma yaki da tafarkin murdiya. Sin da Tarayyar Soviet, a matsayin manyan fagagen yaki na Asiya da Turai bi da bi, sun yi babbar sadaukarwa don yakar mamayar dakarun Japan, da kuma mamayar sojojin Facist na Jamus, kuma sun ba da gudunmawar da ta kai ga cimma nasarar yakin duniya na biyu.
Shugaba Xi ya kara da cewa, ya kamata bangarorin biyu su ci gaba da kara karfafa abota, da zurfafa amincin manyan tsare-tsare, da kara hadin gwiwa a fannoni daban-daban, tare da kare bukatunsu na tsaro da ci gabansu, dadin dadawa da hadin kai da kasashe masu tasowa, ta yadda za su rika bin ainihin manufar hadin gwiwa ta duniya, da kuma taimakawa wajen inganta tsarin duniya mafi adalci da inganci.
A nasa bangaren Volodin ya ce, a karkashin jagorancin shugabannin kasashen biyu, dangantakar Rasha da Sin ta ci gaba da zurfafa cikin nasara. Majalisar dokokin Rasha ta himmatu wajen aiwatar da muhimman yarjejeniyoyin da shugabannin kasashen biyu suka cimma, da kara karfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomin dokokin kasashen biyu, da kuma himmatuwa wajen samun karin sakamako mai kyau a dangantakar kasashen biyu. (Amina Xu)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen ƙasa ta Nijeriya (NRC) ta dakatar da sufurin jirgin ƙasan da ke jigila a tsakanin Abuja zuwa Kaduna.
NRC ta sanar da ɗaukar wannan matakin ne har sai an kammala bincike kan hatsarin jirgin da ya auku a wannan Talatar.
Shugaban hukumar, Kayode Opeifa, ne ya sanar da haka jim kaɗan bayan faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa tuni tawagar masu bincike da suka haɗa da ma’aikatan NRC, hukumar binciken sufuri ta ƙasa (NSIB) da sauran hukumomin tsaro, sun isa wurin domin gudanar da bincike.
Opeifa ya yi watsi da maganganun da ake yi cewa jiragen ba su da inganci, yana mai cewa an fara mayar da kuɗin tikiti ga dukkan fasinjojin da abin ya shafa.
Ya ƙara da cewa hukumar ta karɓi fasinjojin da aka sauke a tashar Asham da kuma tashar Idu a Abuja, tare da tabbatar da cewa za a sanar da jama’a duk wani sabon mataki na gaba.
Aminiya ta ruwaito cewa a safiyar wannan Talatar ce jirgin ƙasan ɗauke da fasinjoji da ya taso daga babban birnin Najeriya zuwa Kaduna ya tuntsure yana tafe.
Rahotanni na cewa lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 11 na safe a ƙauyen Asham da ke hanyar Abuja zuwa Kaduna bayan tasowar jirgin ƙasan da misalin ƙarfe 9:45 daga Abuja.