Category: Latest News

  • Ana zargin miji da kashe matarsa da duka saboda zuwa gona a makare

    Ana zargin miji da kashe matarsa da duka saboda zuwa gona a makare

    [ad_1]



    Rundunar ’Yan Sandan Jihar Ekiti ta tabbatar da mutuwar wata mata mai suna Ofone Modupe Alasin, a karamar hukumar Efon-Alaaye da ke jihar.

    Kakakin rundunar a jihar, SP Sunday Abutu ne ya tabbatar da kisan matar, inda ya ce an kama mijinta yayin da ake ci gaba da bincike.

    Binciken farko-farko dai ya nuna mijin ne ya lakada wa matar tasa duka saboda ta ki zuwa gonarsu a kan lokaci.

    Wani makwabcin gonar ya ce ya jiyo marigayiyar tana ihun neman taimako, amma duk da haka mijin nata ya ci gaba da nada mata na jaki.

    Kazalika, wata majiya daga ’yan sanda ta ce bayan duka ne mutumin ya bukaci ta samo masa ruwa daga wani rafi da ke kusa da gona.

    Sai dai a kan hanyarta ta zuywa debo ruwa a rafin, ta yanke jiki ta fadi ta mutu.


    [ad_2]

    Source link

  • An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

    An Kama Matasa 2 Kan Nuna Makamai A Shafukan Sada Zumunta A Kano

    [ad_1]

    Rundunar ’Yansandan Jihar Kano, ta kama wasu matasa biyu, Mohammed Isma’il (Linga) da Sani Abdulsalam (Guchi), bisa zargin nuna makamai da kuma tayar da hankali a cikin wani bidiyo da suka wallafa a shafukan sada zumunta.

    Kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce a ranar Laraba an kama su a yankin Dala bayan wani samame da aka shirya ta hanyar leƙen asiri.

    An gano cewa suna tara matasa sannan suna saka bidiyo a TikTok da Facebook suna nuna makamai.

    Lokacin da aka cafke su, ’yansanda sun samu takobi guda ɗaya da sanduna guda biyu a hannunsu.

    Kwamishinan ’Yansandan Jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya umarci a gudanar da bincike a kansu.

    Ya kuma gargaɗi jama’a cewa duk wanda aka kama yana amfani da kafafen sada zumunta wajen yaɗa tarzoma ko ta’addanci, za a kama shi tare da gurfanar da shi a kotu.

    Rundunar ta yi kira ga iyaye da su ja kunnen ’ya’yansu ka da suke kwaikwayon irin wannan hali ko sauran laifuka.

    Ta jaddada cewa ba za ta yadda da duk wani abu da zai kawo tashin hankali a jihar ba.

    Rundunar ta kuma gode wa jama’a bisa irin bayanan da suka bayar da ya taimaka wajen kama matasan.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • ’Yan sanda sun ceto yara 3 da aka sace a Kaduna

    ’Yan sanda sun ceto yara 3 da aka sace a Kaduna

    [ad_1]



    Rundunar ’Yan sandan Jihar Kaduna, ta ceto wasu yara guda uku da aka sace tare da kama mutum uku da ake zargi da sace su.

    A ranar Talata, 26 ga watan Agusta, 2025, wani mutum ya kai rahoton cewa an sace ’ya’yansa uku.

    Yaran sun haɗa da Aslam Umar Lukman mai shekaru 14, Suleiman Umar Tanko mai shekaru 12 da Aliyu Umar Tanko mai shekaru 10.

    Waɗanda suka sace yaran sun nemi a ba su Naira miliyan 50 a matsayin kuɗin fansa.

    ’Yan sanda sun yi amfani da dabaru inda suka cafke shugaban ƙungiyar, Richard Philip.

    Yayin bincike, ya amsa laifin tare da bayyana sunayen waɗanda suka taimaka masa; Ibrahim Ma’aruf mai shekaru 18 da Abubakar Sadiq mai shekaru 15.

    Daga baya ’yan sanda sun kai samame maɓoyarsu, tare da kama sauran sannan suka ceto yaran ba tare da wata matsala ba.

    Kwamishinan ’Yan Sandan jihar, CP Rabiu Muhammad, ya damƙa yaran ga iyayensu.


    [ad_2]

    Source link

  • ’Yansanda Sun Ceto Mutane 16 Da Aka Sace A Edo

    [ad_1]

    Rundunar ’Yansandan Jihar Edo, ta ceto mutane 16 da aka sace a wasu hare-hare daban-daban da aka kai a kan titunan Benin zuwa Legas da Benin zuwa Akure.

    Kakakin rundunar, Joel Yamu, ya ce nasarar ta samu ne sakamakon haɗin gwiwar ’yansanda da jami’an sa-kai da mafarauta.

    Ya bayyana cewa mutane shida aka ceto a kan titin Beninzuwa Akure, ɗaya daga cikinsu ya samu raunin harbin bindiga amma an taimaka masa kuma yanzu ana kula da shi a asibiti.

    Haka kuma, mutane uku aka ceto a kan titin Benin zuwa Legas, sai kuma wasu mutane bakwai da aka sace a kan titin Benin zuwa Akure da aka sake su ranar 25 ga watan Agusta.

    ’Yansanda sun ce masu garkuwa da mutane sun tare titin a ranar 23 ga watan Agusta tsakanin ƙarfe 5:30 zuwa 6:00 na yamma, inda suka yi awon gaba da matafiya.

    Bayan samum rahotom faruwar lamarin, jami’an tsaro suka bazu cikin dazuka domin ceto waɗanda suka sace.

    Kwamishinan ’yansandan jihar, Monday Agbonika, ya jagoranci aikin a kan titin Benin zuwa Akure.

    Ya ce sun yi amfani da sabbin fasahohi ciki har da jirage marasa matuƙa, wanda ya taimaka wajen samun nasara.

    Agbonika ya yaba wa jami’an ’yansanda, sa-kai, da mafarauta bisa haɗin kai, yana mai cewa wannan haɗin gwiwa shi ne mabuɗin magance manyan laifuka.

    Ya tabbatar wa jama’a cewa za su ci gaba da aiki har sai an ceto sauran mutanen da aka sace kuma an kama maharan.

    “Mun ƙuduri aniyar kawar da miyagun laifuka daga titunanmu da al’ummominmu, kuma za mu yi amfani da dukkanin kayan aiki na fasaha domin kare rayukan jama’a da matafiya,” in ji kwamishinan.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Uwa Da ’Ya’yanta 3 Sun Rasu Bayan Gini Ya Rufta Musu A Zariya

    [ad_1]

    Wata mata da ’ya’yanta uku sun rasu a ranar Laraba bayan bangon gidansu ya rufta musu sakamakon ruwan sama mai ƙarfi a unguwar Karauka, Zariya.

    Waɗanda abin ya shafa sun haɗa da Habiba Nuhu, ’ya’yanta mata Hauwa’u da Aina’u, da kuma jikarta Za’uma.

    Ɗan uwansu, Malam Ahmed Ibrahim, ya ce lamarin ya faru ne tsakanin ƙarfe 3:30 na dare da 4:00 na safe, inda bangon ya faɗa a kansu.

    “Sun rasu nan take bayan sun maƙale ƙarƙashin ƙasa,” in ji shi.

    Mai gidan, Malam Nuhu Dogara, ya kuɓuta daga hatsarin.

    An kai shi asibiti, inda aka kula da shi sannan aka sallame shi domin halartar jana’izar iyalan nasa.

    Jami’in hukumar bayar da agajin gaggawa ta Jihar Kaduna (SEMA), Bello Garba, ya ce ba su samu rahoton faruwar lamarin a hukumance ba, amma sun shirya gudanar da bincike kan lamarin.

    An binne mamatan bisa tanadin addinin Musulunci.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • An kashe mutum 3 a faɗan ƙungiyoyin asiri a Legas

    [ad_1]



    Aƙalla mutum uku ne sun rasu, yayin da wani ɗan sanda ya ji rauni a wani rikicin ƙungiyoyin asiri da ya auku a kasuwar Owode Onirin da ke Jihar Legas.

    Rundunar ’yan sandan jihar, ta bayyana cewa tana neman Abiodun Ariori, Shugaban Kamfanin Golden Venture Limited, bisa zarginsa da hannu a rikicin.

    Shaidu sun ce ƙungiyoyin asirin biyu sun yi artabu da bindigogi, adduna da kwalabe.

    Ɗan sandan da ya ji rauni an garzaya da shi asibiti, inda yake cikin mawuyacin hali.

    Kakakin rundunar, CSP Benjamin Hundeyin, ya tabbatar da faruwar lamarin.

    Amma ta ce komai ya daidaita tare da wanzar da zaman lafiya bayan da jami’an tsaro suka isa yankin.

    Kwamishinan ’yan sandan jihar, CP Olohundare Jimoh, ya jagoranci tawagar ‘yan sanda zuwa kasuwar, inda suka buɗe hanyoyin da aka toshe yayin rikicin.

    “A lokacin rikicin, mutane uku sun mutu a asibiti sakamakon raunukan da suka samu, yayin da wani ɗan sanda ɗaya ke cikin mawuyacin hali a asibiti,” in ji Hundeyin.

    Rundunar ta kuma ƙaryata jita-jitar cewa rikicin ƙabilanci ne ya tashi a kasuwar Balogun.

    Ta tabbatar da cewar faɗa ne tsakanin wasu ’yan daba, wanda ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya, kuma ba shi da alaƙa da ƙabilanci.


    [ad_2]

    Source link

  • ADC Tana Da Damar Kayar Da Tinubu A Zaɓen 2027

    [ad_1]

    Tsohon gwamnan Jihar Ribas kuma tsohon ministan sufuri, Rotimi Amaechi, ya ce jam’iyyarsu ta ADC tana da kyakkyawar damar kayar da Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.

    Amaechi ya bayyana haka ne a wani taro da ya halarta a Jihar Kano tare da ‘yan kasuwa, inda ya jaddada cewa babu batun yin sulhu a jam’iyyar idan aka zo fitar da ɗan takarar shugaban ƙasa.

    Ya ce kowa yana da damar tsayawa takara a ADC, kuma shi ma zai tsaya takarar shugaban ƙasa a 2027.

    A cewarsa: “Ni takarar shugaban ƙasa zan yi, ba zan janye wa kowa ba. A bar jama’a su zaɓi wanda suka fi so.”

    Amaechi ya kuma caccaki Shugaba Tinubu, yana mai cewa salon siyasar sa ya gaza kawo sauƙi ga rayuwar ‘yan Nijeriya, har ma da mutanen Kudu yankin da ya fito.

    Ya ƙara da cewa jam’iyyarsu ta ADC za ta iya fito da ‘yan takara daga kowace shiyya, duk da cewa APC da PDP sun nuna cewa daga Kudu za su fito da ɗan takara a 2027.

    Duk da cewa wasu na ganin tasirinsa ya ragu a Jihar Ribas saboda rikicin siyasa tsakaninsa da Nyesom Wike, Amaechi ya ce har yanzu yana da goyon baya sosai.

    Ya bayar da misalin yadda aka tarbe shi a Jihar a baya-bayan nan ba tare da ya biya kowa kuɗi ba.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • HOTUNA: Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki a Japan da Brazil

    [ad_1]



    Shugaba Bola Tinubu ya dawo Abuja, bayan ya kammala ziyarar aiki a ƙasashen Japan da Brazil.

    Mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ya ce jirgin shugaban ƙasa ya tashi daga filin jirgin sama na Brasília a ƙasar Brazil da ƙarfe 12:57 na rana a ranar Laraba.

    A cewarsa ya iso Abuja da safiyar ranar Alhamis.

    Ga hotunan yadda wasu manyan jami’an gwamnati suka tarbi shugaban:


    [ad_2]

    Source link

  • Tinubu Ya Dawo Nijeriya Bayan Ziyarar Aiki A Brazil

    [ad_1]

    Shugaban ƙasa Bola Tinubu ya dawo Abuja bayan ziyarar aiki da ya kai ƙasar Brazil domin ƙarfafa dangantaka tsakanin ƙasashen biyu.

    Jirgin shugaban ƙasar ya tashi daga filin jirgin saman Brasília International da ƙarfe 12:57 na rana agogon ƙasar.

    Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya bayyana cewa jami’an Brazil, Jakada Carlos Sérgio Sobral Duarte da Jakada Carlos José Areias Moreno Garcete tare da Ƙaramin Ministan Harkokin Wajen Nijeriya, Bianca Odumegwu-Ojukwu, da wasu jami’an gwamnati, sun raka shi zuws filin jirgin.

    An gudanar da ƙaramin bikin bankwana tare da girmamawar dakarun soja ƙarƙashin jagorancin Col. Cel Nicolas.

    Tinubu ya isa birnin Brasília ne a ranar Litinin, 25 ga watan Agusta, inda aka tarbe shi a Fadar Shugaban Kasa, Palácio do Planalto.

    A lokacin ziyarar, ya gana da Shugaban Brazil, Luiz Inácio Lula da Silva, da sauran manyan jami’an ƙasar.

    Ƙasashen biyu sun rattaba hannu kan yarjejeniya guda biyar da suka shafi sufurin jiragen sama, harkokin waje, kimiyya da fasaha, da kuma noma, da wasu muhimman fannoni a ci gaban Nijeriya.




    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

    Shiga zaurenmu na WhatsApp



    [ad_2]

    Source link

  • Kotu ta daure dan Shugaban Equatorial Guinea kan sayar da jirgin saman kasar

    [ad_1]



    Wata kotu a kasar Equatorial Guinea ta daure dan Shugaban Kasar a kurkuku kan sayar da jirgin sama mallakin kasar ba bisa ka’ida ba, sannan ya zuba kudaden a aljihunsa.

    Alkalin kotun dai a ranar Laraba ya yanke hukuncin cewa dan Shugaban Kasar Teodoro Obiang Nguema Mbasogo, mai suna Ruslan Obiang Nsue, zai shafe shekaru shida a gidan yari.

    Sai dai kotun ta ce idan zai biya kudin jirgin da ya bace ba za a daure shi ba, kamar yadda Daraktan yada labarai na Kotun Kolin Kasar, Hilario Mitogo ya shaida wa ’yan jarida.

    Kotun dai ta yanke wa Ruslan mai shekaru 50 a duniya, wanda tsohon shugaban kamfanin jiragen samar kasar mai suna Ceiba Intercontinental hukuncin ne bisa laifin sayar da jirgin kasar mai suna ATR 72-500 ga wani kamfanin kasar Spain, sannan ya zuba kudin a aljihunsa.

    A shekara ta 2023 an yi masa daurin talala bisa umarnin Mataimakin Shugaban Kasar, wanda shi ma dan uwansa ne na jini kuma dan shugaban kasar.

    Kotun dai ta ce wanda aka yanke wa hukuncin zai iya kauce wa daurin idan ya biya tarar Dalar Amurka 255,000, kwatankwacin sama da Naira miliyan 382 ga kamfanin jiragen sannan ya biya tara ga gwamnati.

    Sai dai kotun ta wanke shi daga wasu zarge-zargen na almundahana da halatta kudaden haram.


    [ad_2]

    Source link