Ambaliya ta raba ƙauyukan Sakkwato 6 da sauran sassan jihar

[ad_1]



Ambaliyar ruwar da ta biyo bayan mamakon ruwan saman da aka tafka ta raba kauyuka shida da ke karamar hukumar Sabon Birni ta jihar Sakkwato da saurann yankunan jihar.

Kauyukkan da ambaliyar ta shafa su ne Makuwana da Dangawo da Faru da Gumbula da ’Yan Faruna da kuma Magajin Dawaki, sannan ta lalata hanyar da ta hada kananan hukumomin Goronyo da Sabon Birni.

Tuni dai Majalisar Dokokin Jihar ta yi kira ga gwamnatin jiha da ta tarayya da ke kula da harkokin ruwa da su dauki matakin da ya dace kan wadanda lamarin ya shafa.

Hakan dai ya biyo bayan bukatar da dan Majalisar Dokokin Jihar mai wakiltar mazabar Sabon birni ta Kudu, Aminu Mustafa Boza, ya gabatar gaban majalisar kan bukatar tallafa wa yankunan da iftila’in ya shafa.

Boza a yayin zaman majalisar wanda mataimakin shugabanta, Alhaji Kabiru Ibrahim ya jagoranta ranar Alhamis, ya nemi ta jawo hankalin hukumomin da lamarin ya shafa kan halin da kauyukan suka ciki

Wani mazaunin daya daga cikin kauyukan, Sani Gumbula ya ce ruwan ya yi musu barna sosai don haka akwai bukatar gwamnati ta kawo musu agajin gaggawa.

“Yanzu abin da nake fada maka gidajenmu da yawa sun rushe, gonaki sun nutse a ruwa sanadin wannan iftila’i, mun yi asara matuka, muna kira ga gwamnati ta yi abin da ya dace a kankanen lokaci, gaskiya muna cikin damuwa,” in ji Sani.


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *