Tinubu ya bukaci sabon shugaban INEC ya gudanar da zaben gaskiya a 2027

[ad_1]



Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, a ranar Alhamis, ya rantsar da Farfesa Joash Ojo Amupitan (SAN), a matsayin sabon shugaban Hukumar Zabe ta Ƙasa (INEC) na shida da aka tabbatar da shi.

An gudanar da wannan gajeren bikin rantsarwa ne a ɗakin taro na fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Bayan rantsarwar, Shugaba Tinubu ya bukaci sabon shugaban INEC da ya yi aiki da gaskiya da amana, ba tare da wata matsala ba.

“Naɗa ka da kuma tabbatar da kai da Majalisar Dattawa ta yi, alama ce ta ƙwarewarka da amincewar da bangarorin zartaswa da na dokoki suka nuna gare ka.

“Wannan babbar nasara alama ce ta fara tafiya mai ƙalubale amma mai albarka, kuma ina da tabbacin za ka ɗauki wannan nauyi da cikakkiyar gaskiya, sadaukarwa da ƙaunar ƙasa,” in ji Shugaba Tinubu.

Shugaban ƙasa ya bayyana cewa Najeriya ta fara tafarkin dimokuraɗiyya tun daga 1999, tare da ci gaba mai ma’ana wajen ƙarfafa hukumomi da tsare-tsare, inda ya ce: “Dimokuraɗiyyar mu ta yi nisa cikin shekaru 25. Mun ƙarfafa hukumomin dimokuraɗiyya, musamman tsarin zabe, ta hanyar kirkire-kirkire da gyare-gyare.

“Muna ci gaba da koyon darussa, kuma mun inganta sosai fiye da yadda muke shekaru da suka wuce. Yanzu dole ne mu ci gaba da bin ƙa’idojin dimokuraɗiyya a cikin al’umma mai rikitarwa da sassa da dama.

“Tsarin zabe muhimmin ɓangare ne na dimokuraɗiyya wanda ke ba jama’a damar zaɓar shugabanninsu da tsara makomarsu. Don tabbatar da ci gaban dimokuraɗiyya, dole ne a tabbatar da ingancin tsarin zabe,” in ji shugaban.

Tinubu ya ce zaben gwamna da za a gudanar a Jihar Anambra a ranar 8 ga Nuwamba, 2025, zai zama zakaran gwajin dafin jagorancin sabuwar hukumar zabe.

“Yana da matuƙar muhimmanci a tabbatar da cewa zabukanmu suna da kyau, adalci da inganci. Dole ne mu ci gaba da inganta tsarin zabe, mu magance matsalolin da suka gabata, mu kuma kawo sabbin hanyoyi don yau da gobe.

“Babu tsarin zaben da ba shi da matsala, amma tun da zabe muhimmin ginshiƙi ne ga makomar ƙasa, dole ne a ci gaba da ƙarfafa hukumomin zabe, a tabbatar da cewa suna da ƙarfi, juriya, kuma an kare su daga matsalolin da za a iya kauce wa.

“Saboda haka, ina ba ka umarni, Farfesa Amupitan, yayin da ka ɗauki wannan nauyi mai muhimmanci, da ka kare ingancin tsarin zabukanmu, da kuma ƙarfafa ƙarfin hukumar INEC.”

Bikin rantsarwa ya biyo bayan tabbatar da naɗa Amupitan da majalisar dattawa ta yi a ranar 16 ga Oktoba.

Amupitan ya gaji Farfesa Mahmood Yakubu, wanda ya jagoranci INEC daga 2015 zuwa 2025.

Da yake jawabi ga ’yan jarida bayan bikin, sabon shugaban na INEC ya yi alkawarin kare kundin tsarin mulki da dokokin Najeriya dangane da tsarin zabe.

Ya kuma yi alkawarin yin aiki tare da masu ruwa da tsaki don nasarar zabe a ƙasa.

Ya ce, “Zan kare kundin tsarin mulki da dokokin Najeriya dangane da tsarin zabe, kuma kamar yadda Shugaban Ƙasa ya ce, an ba ni umarni kai tsaye da na tabbatar da zabe mai inganci, adalci da nagarta.”


[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *