Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i

[ad_1]

Gwamnatin jihar Kano ta gana da shugabannin ‘yan bangar siyasa da suka tuba a jihar tare da yi musu alkawarin tallafa musu ta hanyar sauya tunaninsu da horar da su sana’o’i da kuma kayan aikin fara sana’ar.

Taron wanda ya gudana a ranar Talata a Kano ya samu halartar tubabbun ‘yan barandan siyasa da masu satar waya kusan 718.

Kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Ibrahim Waiya ya yi kira ga mahalarta taron da su rungumi tuba da gaskiya tare da bayar da hadin kai ga shirin gwamnati na sauya rayuwarsu.

“An shirya tsaf, kawai jira ake ‘yansanda da hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa ta dauki bayananku.

“Waɗannan matakai ne masu mahimmanci waɗanda ta hanyarsu za ku zaɓi irin sana’ar da kuke son koya kuma za a horar da ku duk irin sana’ar da kuka zaba, daga karshe a gwangwajeku da kayan aikin fara sana’ar,” in ji shi.




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *