Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

[ad_1]

’Yansanda a Akure, Jigar Ondo, sun kama wata mata da ake zargi da kashe ’yar uwarta kan bashin Naira 800.

Matar da ake zargi mai suna Bosede Iluyemi, ’yar kasuwa ce.

Ta nemi ’yar uwarta, Omowumi Tewogboye, ta biya kuɗin tumatir da barkono da ta karɓa bashi a wajenta.

Rigima ta tashi a tsakaninsu, inda Bosede ta ta kama Omowumi da rigima.

Omowumi ta faɗi ƙasa, inda ta ji mummunan rauni.

An garzaya da ita asibiti, amma daga baya likitoci suka tabbatar da mutuwarta.

’Yansanda sun kama Bosede kuma suna bincike a kan lamarin.

Kakakin rundunar, DSP Olusola Ayanlade, ya ce za su tabbatar da adalci.




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *