Kwankwaso Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP A Hukumance

[ad_1]

Tsohon gwamnan Jihar Kano kuma ɗan takarar shugaban ƙasa na shekarar 2023 na jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso, ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar nan take.

Kwankwaso ya bayyana hakan ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da kwanan wata 29 ga Maris, 2026, inda ya bayyana cewa yanke irin wannan shawarar abu ne mai matuƙar wuya a wurinsa, amma hakan ya zama dole sakamakon sauye-sauyen da yadda alkiblar siyasar ƙasar ke karkata.

“Ina bayyana ficewata daga jam’iyyar NNPP nan take a hukumance,” in ji shi.

Tsohon gwamnan, wanda ya kuma riƙe muƙamin jagoran jam’iyyar na ƙasa, ya nuna godiya bisa damar da aka ba shi ya wakilci NNPP a matsayin ɗan takarar shugaban ƙasa a zaɓen da ya gabata na 2023.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *