Atiku Abubakar Ya Zargi Bola Tinubu Da Raunana Dimokuraɗiyya

[ad_1]

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da gurgunta tsarin dimokuraɗiyya a Nijeriya.
Atiku, wanda ke jagorantar ɓangaren adawa a jam’iyyar ADC, ya bayyana damuwarsa kan ƙarancin fitowar masu kaɗa ƙuri’a da aka samu a zaɓen ƙananan hukumomin Abuja da aka gudanar a ranar Asabar. Ya ce yawan masu zaɓen bai kai kashi 20 cikin 100 ba, alamar da ke nuna, a cewarsa, yadda dimokuraɗiyyar ƙasar ke fuskantar barazana.
  • Sojoji Sun Daƙile Hare-haren Boko Haram, Sun Kashe Mutane 29 A Borno, Yobe
  • Tinubu Ya Taya APC Murnar Nasara A Zaɓukan Birnin Tarayya, Kano Da Ribas
A cikin wata sanarwa da mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Paul Ibe, ya wallafa a shafinsa na X, Atiku ya ce: “Ƙarancin masu kaɗa ƙuri’a a babban birnin ƙasa ba abin mamaki ba ne, illa sakamakon yanayin siyasa da ya cika da rashin gaskiya, tsoratarwa, da kuma rage ƙarfin muryoyin adawa.”
Ya ƙara da cewa idan ’yan ƙasa suka daina amincewa cewa ƙuri’unsu na da tasiri, to dimokuraɗiyya ta fara raunana.
Atiku ya jaddada cewa, abin da ake gani ba kawai rashin sha’awar zaɓe ba ne, sai dai sakamakon shugabanci da ke takura tsarin dimokuraɗiyya. A cewarsa, dimokuraɗiyya ba za ta cika ba matuƙar babu ƙarfi a ɓangaren adawa, babu gasa ta gaskiya a siyasa, kuma babu cikakkiyar amincewar jama’a da tsarin zaɓe.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *