An Kama Wadanda Ake Zargi Masu Garkuwa Ne 12 Da Wasu 83 A Jihar Ondo

[ad_1]

Hukumar Tsaron Jihar Ondo, wadda aka fi sani da Amotekun Corps, ta kama akalla mutane 95 da ake zargin aikata laifuka a dukkan kananan hukumomi 18 na jihar.

A cewar rundunar, kama wadannan mutane ya samu ne ta hanyar hadin gwiwa da jami’an ofishin rundunar ‘yan sanda na jihar, Nigeria Security and Civil Defence Corps, Department of State Services, da kuma sojojin Nijeriya.

  • Darussa Daga Ramadan Na (2)
  • Jam’iyyar NNPP Tayi Ɓatan Dabo A Tarkadar Zaɓen Cike Gurbi Na Kano

Kwamandan Amotekun na jihar, Akogun Adeleye, ne ya bayyana hakan ranar Lahadi yayin da yake tattaunawa da manema labarai a Akure, babban birnin jihar.

Kwamandan ya ce wadanda aka kama ana zargin su da aikata laifuka kamar satar mutane (kidnapping), sata, fashi da makami, da kuma hako ma’adanai ba bisa ka’ida ba.

Ya bayyana wasu daga cikin wadanda ake zargin kamar haka: Bictor, mai shekara 31; Jonathan, mai shekara 34; Akpan, mai shekara 35; Aliu, mai shekara 27; Sanni, mai shekara 20; Adeoye, mai shekara 44; Ayodeji, mai shekara 50; Abdullahi, mai shekara 24; Doman, mai shekara 25; Isaac, mai shekara 20; Peter, mai shekara 25; da Dada, mai shekara 42.

Adeleye ya ce, “A cikin ‘yan makonnin da suka gabata, dukkan hukumomin tsaro na jihar, musamman Amotekun, ’yansanda, hukumar farin kaya, da DSS, sun yi kokari matuka wajen bibiyar wadanda ake zargi, kuma hakan ya haifar da sakamako mai kyau sosai.”

“Mutum 61 da aka samu a cikin motar tirela, ana zargin su ne, kuma muna ci gaba da tantance su domin sanin matakin da za a dauka bayan an gama tantance su.

“Muna da mutum 19 da suka karya dokar jihar. Muna da uku da suka shafi rikicin harbin shanu tsakanin manoma da makiyaya, sannan muna da 12 da suka shafi satar mutane.

“Labarin mai dadi shi ne cewa wasu daga cikin wadanda ake zargin satar mutane an kama su ne a Karamar Hukumar Akure ta Arewa mai rikici, kuma muna da yakinin cewa wannan zai kawo zaman lafiya a yankin, musamman da ake gudanar da hadin gwiwar ayyukan tsaro a halin yanzu.”

Ya bayyana cewa an kama wadanda ake zargin satar mutane a wurare kamar Ilu-Abo, Akure; Idogun-Ugbe; yankin Alagbaka; Ayede, Akure; Iloro Camp; da Ogbese a Karamar Hukumar ta Akure Arewa.

“Dangane da rikicin harbin shanu, muna da Umai Jibril da Hassan. Wannan ya kawo jimillar wadanda ake gabatarwa a nan kan wadannan laifuka zuwa 34, yayin da wadanda ba a gabatar da su ba, wadanda ake bincike a kansu a halin yanzu, suna 61.

“Ina so in rubuta a tarihi cewa mun sami nasarar cimma wannan sakamakon ne ta hanyar hadin gwiwar dukkan hukumomin tsaro na jihar, musamman ’yan sanda, NSCDC, DSS, da Rundunar Sojin Nijeriya,” in ji shi.

Adeleye ya gargadi masu laifi da su daina aikata laifuffukansu ko kuma su fuskanci mataki mai tsanani daga hukumomin tsaro.

“Jihar Ondo ba wurin tsira bane ga masu laifi. Za mu ci gaba da hadin gwiwa da hukumomi masu alaka domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi,” in ji Kwamandan Amotekun.

[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *