[ad_1]
Kwamishinan Ci Gaban Matasa da Wasanni a Jihar Kano, Mustapha Rabiu Kwankwaso, ya yi murabus a hukumance daga mukaminsa na mamba a Majalisar Zartarwa ta Jihar Kano.
A cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin, Kwankwaso ya nuna godiya ga Gwamna Abba Kabir Yusuf saboda damar da ya ba shi na hidimtawa al’ummar Jihar Kano.
- Tutar APC Ta Fara Kaɗawa A Gidan Gwamnatin Kano Tun Kafin Dawowar Gwamna Abba Jam’iyyar
- An Yi Bikin Murnar Kaddamar Da Shekarar Musayar Al’adu Da Cudanyar Jama’a Ta Sin Da Afirka Ta Mauritius
Kwankwaso ya gode wa gwamnan bisa amincewar da ya ba shi, yana mai cewa ya yaba da gogewa da darussa da ya samu a lokacin da yake kan mukamin.
A cewarsa, “Ina so in nuna matukar godiyata ga Gwamna Abba Kabir Yusuf saboda damar da na samu na yi wa mutanen Jihar Kano hidima. Na yaba da gogewa da darussa da na samu yayin da nake aiki, kuma ina godiya da amincewar da aka ba ni.
“Yayin da nake yin murabus, ina fatan matasan Jihar Kano za su ci gaba da samun kulawa da goyon bayan da suka cancanta,” in ji shi.
[ad_2]
Source link