Jihohi 18 A Arewa Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Satumba – NiHSA

[ad_1]

Hukumar kula da madatsun ruwa ta Nijeriya (NiHSA), ta gargaɗi cewa wasu jihohi a Arewa cewar za su iya fuskantar ambaliya a makonni biyu na farkon watan Satumba.

A sanarwar da ta fitar a shafinta na X, hukumar ta ce gaba ɗaya jihohi 29 da Babban Birnin Tarayya Abuja ne ke cikin barazanar ambaliya daga 1 zuwa 15 ga watan Satumba.

Hukumar ta ce ambaliyar za ta iya shafar ƙananan hukumomi 107, garuruwa 631, da kuma tituna 50 a sassa daban-daban.

Jihohin da suka fi shiga hatsari sun haɗa da: Borno, Zamfara, Jigawa, Kebbi, Yobe, Filato, Gombe, Taraba da Sakkwato, yayin da a Jihar Kaduna barazanar ba ta da yawa.




Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp



[ad_2]

Source link

Similar Posts

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *